NAFEESAT 1-END

NAFEESAT Page 31 to 40

“`( WE AIN’T PERFECT BUT WE’RE ALWAYS, TRYING OUR BEST TO MOTIVATE AND ENTERTAIN OUR READERS ????)“`

/https://www.facebook.com/Perfect-writers-association-100452275039839/

               *P.W.A✍️*

*JIKAR LAWALI CE*✍️

*Wattpad: UmmuDahirah*????

         

*SADAUKARWA*

_Na sadaukar ga Family na gaba ɗaya. *GOMA’S FAMILY*_

        *EPISODE Nineteen*

       Horn tayi a bakin tanƙamemen Gate ɗin gidan su

Babu ɓata lokaci me gadi ya buɗe mata

Ta kutsa hancin motan cikin gidan, yayinda ta nufi parcking space Direct ta faka motar, jakar ta; ta ɗauka da wayan ta tafito ta rufe ƙofan motan tare da saka mata keey, mayafin ta tagyara kana ta nufi cikin gidan cikin tafiyan ta na tsantsan yanga wanda ya zame mata jiki

Usman dake cikin motan sa yana amsa Call yabi ta da kallo time ɗin da tazo ta gifta shi, kallon ta kawai yake yi har ta ɓace wa ganin sa kafin ya ɗauke kansa, a ransa kuwa yana jan tsaki cike da jin haushin kallon ta da yayi, shi mamaki ma take bashi ta yanda take irin wannan tafiyan tamkar baza ta taka ƙasa ba, kai da gani kasan tana ji da tashen ƙuruciya da tsantsan yanga, wanda shi a ganin sa iya Shege ne, be san cewa Nature ɗin ta bane hakan, ya riga ya zama jinin jikin ta, har a maganar ta da komi nata cikin yanga take yin sa tare da sanyin jiki sosai, shiyasa komi nata daban ne, she has a very classy class.

Wayan sa ya janye daga kunnen sa ya fito cikin motan ya rufe, jin ana kiran sallah sai ya nufi bakin famfo na can wajen masu gadi yayi alwala ya fice a gidan zuwa masallaci.

           ⚫⚫⚫

         Ɗahira na shiga cikin parlour’n su da sallama a bakin ta, babu kowa cikin parlour’n don haka Direct cikin ɗakin su ta nufa

Tana shiga bata zauna ba ta shige Toilet bayan ta ajiye jakar ta da wayan ta, alwala ta ɗauro ta fito

Time ɗin ne itama Fadila ta shigo cikin ɗakin don itama dawowar ta kenan, itama jakar ta ta’ajiye ta nufi Toilet ta ɗauro alwala, tazo ta shimfiɗa sallaya kusa da na Ɗahira ta tada sallah.

       Ɗahira ta soma idar wa, don haka ta miƙe ta fice cikin ɗakin, ɗakin Maman ta tanufa

Tana zaune a kan sallaya tana azkar, sallaman da Ɗahiran tayi ta amsa mata tana bin ta da kallo

A kan sofa ta zauna tana kallon Maman nata har ta ida azkar ɗin

Sannu da gida Ɗahira tayi mata

Ta amsa mata tana tambayan ta “har kun dawo?”

“Eh Mama”.

“So Masha Allah, what is your job? Is there no problem?”

She smiled Ɗahira and said, “It’s all right, Mama.”

Gyaɗa kanta ta ɗan yi kafin tace, “Then go to the kitchen and get some food, and if you leave it later, then.”

Gyara kwanciyar ta Ɗahira tayi saman dogon kujeran tana ɗaura hannun ta saman kanta tace, “I’ll eat later.”

Aunty Amarya bata sake cewa komi ba taci gaba da addu’o’in ta, har sanda ta gama ta tashi ta fice cikin ɗakin.

        Ita kuwa Ɗahira tana nan kwance tana tunane-tunane cikin ranta, kuma duk tunanin nata akan Masoyin ta ya ƙare, zuciyar ta na ƙwaɗaita mata son ganin shi matuƙa, tana son sanin ko wane ne but ya ƙi amince wa su haɗu, Allah ya gani tana ƙaunar sa itama, zata so su haɗu ko dan ya nuna mata soyayyar da yake mata a zahiri ba a cikin waya ba, har yanzu ba su taɓa yin waya ba, ko ta kira ba ya shiga, amma kuma idan ta tura text babu daɗe wa yake turo mata reply.

        Numfashi taja tana juya kwanciyar nata fuskarta ƙunshe da murmushi.

       Aunty Amarya da ta shigo tana kallon ta, kaɗa kai kawai tayi bata ce mata komi ba, sai da ta daidaita kanta a sallaya sannan ta sake duban ta tace, “To idan kin gama murmushin da saƙar zucin; ki tashi ki je kiyi sallah, Abbun ku ya dawo ma yana neman ki”.

Murmushi kawai Ɗahira tayi tana kallon Maman nata da har ta soma sallan ta tamkar ba ita ce tayi maganar ba, tashi tayi tana sosa kanta cike da kunya da ya kama ta jin abinda tafaɗa mata, ta fice a ɗakin.

           Bayan kowa ya idar da sallan sa fitowa suka yi suka hallara a kan dainning, cike da nishaɗi suke gudanar da dinnern su, kai da gani kasan suna farin ciki, musamman yanda Abbu ke ta jan su da hira yana tsokanar su don shi dama al’adan sa ne tsokanar ƴaƴan sa, yana da son yara kuma ba ya da ɗaurewar fuska ga iyalan sa.

       A haka har suka gama cin abincin suka dawo Parlour suka yi zaman hira, in ka ɗauke Fadila da tuni ta shige ɗaki abun ta, don ita bata cika zaman hiran ba ne sai ta ga dama, kuma ko ta zauna baza ta ce uffan ba, wayan ta ko t.v su ne kaɗai abokan hiran ta, wani lokacin kuma idan an sako ta takan saka musu baki ko tayi murmushi, babu me damuwa da halin nata tunda ba baƙon abu bane a gidan nasu, ba ita kaɗai ba gaba ɗayan su hakan a jinin su yake, sai dai nata abun ya girmama ne, to zan iya cewa halin su ɗaya da Usman domin miskilancin ya girmama.

⚫⚫⚫⚫⚫⚫⚫⚫⚫⚫

          *Ƙarfe 11:30pm.*

       Lokacin ne Hajja Fatu ta tura ƙofan ɗakin mijin ta tashiga da sallama

Be ɗago kai daga aikin da yake yi cikin Laptop ba ya amsa mata

Taho wa tayi ta samu wuri gefen gadon kamar yanda shima yake zaune, ta zauna tana kallon Laptop ɗin, duk da kuwa ba ta ganin abinda yake yi a ciki amma hakan be sa ta ɗauke kanta ba, illa ma ƙoƙarin leƙa wa da take son yi

Shi kuma jin tayi shiru sai ya ɗan ɗago kansa kaɗan ya kalle ta, ganin tana leƙa masa Laptop sai yace, “lafiya dai Hajjaju, what do you want to see?”

Ɗan ja da baya tayi cikin basarwa duk da kuwa taji kunyan kama ta da yayi, sai lanƙwaye murya da tayi tace, “to Abban Baffa laifi ne don na leƙa naga me kake yi? Don’t forget that I am also a doctor.” 

“Eh ke doctor CE sai aka yi ya ya? Ko an ce miki wannan aikin Hospital ne?” Yayi maganar yana yatsina fuska

“Uhmm Abban Baffa why are you like this to me? Mene ne dalilin ka na son ɓoye min sirrin ku? Kar ka manta fa Ni matar ka ce kuma uwar ƴaƴan ka, sannan a duk matan gidan nan Ni kaɗai ce wacce tayi ilmi me zurfi har kuma take ci da gumin ta, idan baku saka Ni a al’amuran ku na taimaka muku ba; to wa zaku saka? Wlh ba na jin daɗin abinda kake min kwata-kwata, na kula ko kaɗan kana ɗauka ta wata aba ce daban saɓanin yanda ni na ɗauke ka”. Hajja Fatu taƙarishe maganar nata cikin tsantsan damuwa da ya nuna a muryan ta, tabbatan dai abinda mijin nata yake mata ba ya mata daɗi

Murmushi Abba ya saki cike da mamakin matar tasa, shi be ga abinda yake mata ba da koda yaushe idan taga yana aiki sai tayi ƙorafi, musamman idan ya nuna mata aikin be shafe ta ba duk lokacin da ta buƙaci taya sa, to shi me zai saka ya bata bayan wannan sirrin Business ɗin su ne da ƴan uwan sa, don tana aiki a Hospital ɗin ai ba yana nufin tasan sirrin su bane, da me tafi sauran matan gidan ne?…

“Abban Baffa, I am talking and you are listening because you have made Me nothing.” Maganar ta takatse masa tunanin sa

Still murmushin yayi yace, “kin fiye rigima ke kam Hajjaju, kin ga na nemi taimakon ki ne? Meyasaka baza ki ji da naki aikin ba? Ko da ma abinda ya shafi aikin asibiti ne ai ba ɓangaren mu ɗaya ba bare ki taya ni, ki je abun ki na gode”.

A fusace Hajja Fatu take kallon sa, cikin takaici da halin mijin nata da har yanzu ya ƙi ya gane tace, “haka kace ko Alhaji? Well shikenan God help”.

Da gama maganar; ta miƙe ta nufi ƙofa don ficewa, duk da har aranta ta nuna masa fushin ta ne don ta san halin sa zai iya dawowa da ita, daga nan ma ya faɗa mata abinda yake yi, ita kuma ta samu damar shiga jikin sa har tasan sirrin komi nasu

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8Next page

Related Articles

Leave a Reply

Back to top button