NAFEESAT 1-END

NAFEESAT Page 41 to 50 (The End)

      Daure wa sosai Ayush tayi, ta ara wa kanta jarumta ta soma magana da faɗin, “dama I have come to tall you that..” sai tayi shiru ta kasa ƙarisawa

Tun soma maganar nata ya buɗe idanun sa da suka soma sauya kala, sai dai be motsa daga yanda yake ba, har yanzu fuskar sa na kallon sama ne, yana jiran yaji abinda ya kawo ta, domin dai zai iya cewa be ma taɓa sanin ta ba a nan Hospital ɗin, shiyasa zuwan nata wajen sa yake ba shi mamaki, duk da kuwa ba yau ya saba ganin hakan ba, amma kuma ita ɗin ya dangana hakan da zuwan ta a kan aiki ne..

Sauya maganar nata tayi da faɗin, “my name is Ayush Abdulkarim, wacce take tura maka saƙo a facebook, kuma kwanaki biyu kenan da soma maka magana ta WhatsApp”. Sai ta sake yin shiru

Sai a time ɗin ya ɗago kansa sosai yana sauke rikitattun idanun sa a kanta, sosai ya haɗe rai a wannan karon fiye da tunanin me tunani, wanda har sai da ya sa Ayush ta sunkuyar da kanta da sauri sabida ba ƙaramin tsorata tayi da kallon nan da yake mata ba, tabbas tuni ya gane ta da bayanin da tayi masa, sabida yanda take damun sa a facebook; kullum sai ya ga saƙon ta, that’s why tana faɗar sunan nata ya gane.

      Be ce komi ba, kamar yanda itama ta kasa yin magana, tsawon lokaci kafin taji muryan sa ya daki dodon kunnen ta

“Get out”. Ya bata umarni cikin natsatstsiyar muryan sa

Nan da nan sai ga hawaye sharr sun soma kwaranya a fuskar ta, tana kallon sa tace, “don Allah ka taimake Ni kamar yanda Allah ya taimake ka, wlh wlh zan iya rasa raina idan har ban same ka ba, Ina son ka, ina matuƙar ƙaunar ka, don Allah..”

Tsawan da ya daka mata ne, yasa tayi shiru babu shiri

“Out”. Ya faɗa tamkar ana masa dole cikin murya me amo, domin maganar nan da ta saka shi har kanshi ya soma sara wa, dama ga shi yana buƙatar hutu da barci

Miƙe wa tayi idanun ta na tsiyayar da hawaye ta bar Office ɗin.

     Lumshe idanun sa yayi yana sake jingina bayan sa da kujeran, ya rasa meyasa yanzu mata suka ɓaci, shin ina suka bar kunyan su ta ɗiya mace har suke iya zuwa su sami namiji su faɗa mishi suna son sa? Sosai yake mamakin yanda duniya ta sauya, ko zai mutu ne ai bazai iya auren mace irin wannan local ɗin ba, in ba raini ba kamar yarinyan nan ta zo har gaban sa tana faɗa masa tana son sa, tsaban takaici ma tsaki yaja ya miƙe ya ɗauki keeys ɗin motan sa ya bar Office ɗin.

⚫⚫⚫⚫⚫⚫⚫⚫⚫⚫

         *WEDNESDAY*

      Cikin sauri take tafiya kasancewar tayi late, har ga shi 10:03am. Ta yi, wajen motan ta ta ƙarisa ta saka keey tana shirin buɗe wa, sai ta hangi Baffa shima ya fito daga bayan gidan

Tafiya yake yi yana waya kansa a ƙasa yana tsola ƙafafuwan sa tamkar yana ƙwallo

Mayar da ƙofan tayi ta rufe ta taka ta nufi inda yake, be ganta ba har sai da taƙariso wajen, inda daddaɗan turaren ta ya doki hancin sa, da sauri ya juyo suka haɗa ido

Murmushi ta sakar masa, don ganin sa ba ƙaramin faranta ranta ya yi ba, tun zaman da suka yi last two weeks wajen meeting bata sake ganin sa ba. bata yi magana ba ganin yana waya

Sai dai shi gaba ɗaya tunda suka haɗa ido ya rasa sukunin sa, wayan kawai yake yi amma hankalin sa ba ya tare da shi, duk da kuwa ya kawar da idanun sa daga kanta. Ɓata lokaci yayi yana wayan yaƙi ya yanke, sai kamo wani zancen yake yi kasancewar da abokin sa yake wayan.

     Ita kuma tana tsaye ta harɗe hannayen ta a ƙirjin ta tana kallon sa, shiru tayi kawai idanun ta a kansa, sosai take ganin sauyi a tattare da Baffa, gaba ɗaya yanzu ta ga kamar ya sauya mata, kwata-kwata ba ya son ganin ta, idan ba haka ba tasan babu yanda za’a yi a kwana a hantse be nemi ganin ta ba, koda kuwa ta waya ne, amma yanzu tsawon satikai kusan uku kenan ana shirin wata ba ya neman ta, tana ganin kamar akwai wani abinda ke damun sa, yanda gaba ɗaya ya sauya har wani rama yayi…

“Keee!”

Tsawan da aka daka mata ne ya sanya ta dawo hankalin ta cikin matuƙar tsoro

Ba ita kaɗai ba, har ta Baffa da ya juya baya a yanzu ɗin yana ci gaba da wayan sa, sai da ya tsorata da tsawan da aka yi

Sa’adatu ce tsaye ƙiƙam gaban Ɗahira, ta kame ƙugun ta da hannayen ta biyu tana faman huci tamkar zaki, ba komi ya fusata ta haka ba illa fitowar da tayi tana shirin fita, sai ta hangi Ɗahira gaban Baffa ta ƙure sa da idanu ko ƙyafta wa ba ta yi, ga shi kuma har ta iso wajen tana mata magana amma bata ji ta ba, hakan ya sa ta daka mata tsawan nan

Bata bari kowa yayi magana a cikin su ba tace, “uban meye kika tsaya kina kallon sa tamkar zaki cinye sa? Ko dai wani makircin zaki ƙulla iyeee? Ki faɗa idan ba muna-furci da makircin da ke ran ki ba; meye ya kawo ki bayan shi kina kallon sa be ma san kina yi..”

“Kee Sa’ada are you crazy? Kin san da wa kike magana kuwa?” Cewar Baffa a matuƙar fusace da ɗaga murya

Kallon sa Sa’adatu tayi, sai ta zaro masa ido tace, “hankali na ƙalau kuwa Yaya, so nake in San meye alaƙan ka da wannan yarinyan? Ina ce Hajja ta raba ku meye kuma ya sake haɗa ku? Ok har yanzu kana son…”

Mari ya yarfa mata, wanda har sai da yasa ta soma ganin taurari, ba ita kaɗai ba har Ɗahirah dake kusa da ita, bata san sanda hannun sa ya gilma ta gefenta ba, hakan yasa ta tsorata taja baya da sauri tana shirin faɗi

Saurin taro ta Baffa yayi, hakan yasa ta faɗo kansa tamkar ya rungume ta.

      A wannan lokacin shi kuma Usman ya fito gida, babu inda idanun sa ya sauka sai a kansu, tsaya wa yayi kawai yana kallon su cike da mamaki. Janye idanun sa yayi daga kallon su yana jan tsaki a fili, a zuciyar sa kuwa cewa yake, “dama daga gani idan wannan sheɗaniyar yarinyan bata ja hankalin maza sun faɗa tarkon ta ba ai ƙarya ne, waye ya san ma ranan da kuka soma hakan”. Motan sa ya ƙarisa ya shiga ya ja ya bar gidan.

     A can kuwa wajen su, Baffa ya kasa cire Ɗahira a jikin sa, while itama ta kasa motsa wa, domin sosai ta tsora ta, sai da ta gama dai-dai ta nutsuwar ta kafin tayi yunƙurin janye jikin ta.

     Sa’adatu da tayi mutuwar tsaye na daga tsantsan mamakin marin da Baffa yayi mata, ga kuma takaicin ganin su haɗe da juna, shi ne yasa ta kasa koda ƙwaƙƙwaran motsi, illa bin su da kallo da take yi.

        Ɗahira na janye jikin ta ta juya ta wuce ba tare da ta furta komi ba

Baffa be iya dakatar da ita ba, duk da kuwa yana son tsayar da ita ɗin, har ta shige mota yana bin ta da kallo, sahun gudun Sa’adatu da kukan ta kawai ya ji, ya juya yana kallon ta wanda har ta kai ƙofa ta shige cikin gidan. Ajiyan zuciya ya sauke yana bin wayan sa dake ƙasa da kallo, be ma san sanda ya wuntsilar da ita ba garin taro Ɗahira. Lumshe idanun sa yayi a hankali ya furta, “Ina son ki Ɗahira! Ina matuƙar ƙaunar ki! Kuma ba zan taɓa dena ƙaunar ki ba har na koma ga mahalicci na”.

           ⚫⚫⚫

     Ɗahira motan ta kawai take ja tana tunani, ko kaɗan ta kasa gane takamaiman abinda ke damun ta

Tsaki kawai ta ja ganin tana son damun kanta da tunanin banza, ƙara Speed ɗin motan tayi tana kallon agogon hannun ta

Dai-dai ta isa kusa da Hospital ɗin, tana shirin shan kwana ta shiga, bata kula sosai ba, Ashe wata mota babba na ɗan gote ta dumfaro. shi kuma can ɗaya side ɗin me machine ya dumfaro da gudu yana shirin gilma motan, sai motan tayi ciki da shi, Wanda machine ɗin da me machine ɗin tuni sun yi hanyar su daban, inda machine ɗin ta zo kan motan Ɗahira da har ta kusa tura kan hancin motan ta cikin Hospital ɗin, sai ji kake yi motar nata tayi ƙuuuuuuu.. saboda wani wawan burki da taja kasancewar buguwan da machine ɗin tayi a kan motan ta, yayi matuƙar tsorata ta har ta rasa nutsuwar ta gaba ɗaya taja burki a take tana salati

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14Next page

Related Articles

Leave a Reply

Back to top button