Noor AlbiNOVELS

NOOR ALBI 41

Mamuhgee 41_*
Girgiza Kai tayi cikin neman dawowa daidai Dan Bata Gama fahimtar takardar ba Dan Haka ta dunqule takardar tareda qarasawa kujerar Dake dakin ta zauna ta aje handbag dinta gefe kafin tasake ware takardar da kyau tafara karantowa tun daga sunan asibitin kalma bayan kalma harta Kai qarshe ta jinjina Kai tareda sauke numfashi a bayyane tana cewa”

Yaqi ga Mai yinka…

Kokarin daukan wayarta takeyi ta dauka hoton takardar Kiran Ms Na’ima yashigo wayar saidata sake sake numfashi Mai zafi Dan kuwa yanda takeji Kamar tayi Ido biyu da bomb ta latsa makunninsa asibitin gabaki daya ta buga
Bare Na’ima da zata fadawa zancen yanzu Dan Haka kallon Mai aikinta tayi tareda daukan Jakarta ta Ciro kudi masu yawa tace’

Kira securities din Dake waje maza.

Aje jakar Sa’adah nafisar tayi tareda nufar kofa ta fita da sauri.

Shigowa sukai ba jimawa
Dayan idonsa na Kan kudin Dake hannun Haj Zinat wadda a matse take da kowa ya watse abarta a dakin
Dan Haka ba Bata lokaci ta damqa musu kudin tace su tafiyarsu zata kula da sauran aikin kulawan Sa’adah din.

Dayake idonsu da zuciyarsu na Kan kudin Basu tsaya batawa kansu lokaciba Suma Suka karba Suka tafiyarsu.

Bayan tafiyarsu kallon nafisa tayi tace”

Fita waje kiban guri nayi mgn.

Ficewa tayi tareda Jan kofar.

Wayarta daketa faman vibrating na Kiran Ms Na’ima ta kalla tareda dagawa Kai tsaye tana gyara zama.

Cikin qaguwa da takaici Ms Na’ima tace”

Wai Zinat bazaki fadamun yanayinda yarinyar takebane?,
Idan batada alamar mutuwa ki biya ko nawane likitocin asibitin su Mata allurar qin tashi ta tabbata akwance na huta Dan jikina naban itace aka gani tareda Turaki L.A,
Zuciyata zafi take zancen Nan ya dagargaza hakurina wlh…

Na’ima ki nutsu ki saurara abinda yafi Wanda kikaji abakin khairat Chiroma,

Wannan yarinya dai ta tabbata itace atareda Turaki a L.A,
Gatanan a cikin Jakarta wlh nasamu sakamakon tana daukeda ciki harna wata hudu….

Dan shiru Ms Na’ima tayi na seconds kafin ta Dan gyara murya tace”

Ban fahimtaba,
Meye Kuma sakamon ciki ajikinta harda wasu wata hudu akai..
Kutumar ubanta zakicimun agurin na tafiyar datai da mijina tin kafin wannan maganar da kike ta tabbata Dan kuwa kasheta zanyi duk ta dauka cikin mijina…..

Na’ima maganar zahirin da gaske nake Miki akan abinda idona Suka ganemin Wanda tabbas takardar Babu qarya acikinta,
Wannan yarinyar cikine a jikinta
Na watanni hudu koma fiye…

Yawun da Ms Na’ima zata hadiye tayi numfashi ta nema ta Rasa abakinta
Gigice tafara taba wuyanta zuwa maqoshinta tana neman yawu Amma ya dauke qaf ta Rasa na hadiyewa….

Laylah data shigo dakinta idonta Suka sauka Kan yanayin momyn da sauri ta qaraso cikin firgici tana Kiran sunanta da Dan qarfi
Amma Ms Na’ima kokarin shaqurewa take sbd rashin yawun dazaibi maqoshinta yabi ta kirjinta kafin ya Isa cikinta ko zatai rage zafin wutar data taso cikin kirjinta…

Hankali tashe Laylah ta kamota duk da tafi karfinta sbd yanayin jikinta datake ba Mai qiba sosaiba Amma tanada nata jikin ba laifi musamman tunda tabaro Nigeria tana gaining weight ba laifi sbd ta daina dieting datake tuni.

Palo tayo da ita tana kwalawa siddika Kira tana cewa”

Yi sauri kawo ruwan sanyi ba sosaiba abawa mum, inaga tasamu attack ne
Yi sauri…..

Ruwan siddika taje da gudu takawo
Cindy ma da sauri tabiyota da wasu ruwan a qaramin bowl da towel qarami
Cikin sauri Laylah ke Bata ruwa abaki suna wucewa a wahale
Cindy ma cikin sauri take gogewa mum din qafafu da towel Mai sanyi hankalinsu duk a tashe.

Ruwan na bin kirjinta suka shiga cikinta ta dago idanuwanta cikin masifa ta tayi wurgi da robar ruwan gabanta tana miqewa Laylah tayi saurin riqota tana Kiran sunanta cikin tsoro tace”

Mum, mum lafiya kuwa?
Wani abun yafaru ne?
Please mum kina bamu tsoro…..

Wayarta take ware ido nema Dan Haka Bata iya cewa komaiba sai ture Laylan datai da qarfi tayi baya da qarfi tana sakin salati Mai qarfi Dan kuwa kife ta tafi zata Fadi
Da sauri Cindy ta tarota cikin tsananin firgici da tashin hankali…

Kallon juna sukai itada Cindyn lokacinda ta tsayu daidai suka kalli cikin tare jikinsu duka Yana Yar rawa
Take tsoron halin data tashi fadawa data fadin yasata shiga yanayi na tsoron ta dago idanuwanta da tuni Suka ciko da hawaye tabi bayan mum da kallo harta shige dakinta ta rufo…

Kasa tafiya tayi da kanta sbd ta firgita sosai itama Dan Haka hannun Cindy ta Kama suka Isa har cikin dakinta ta zauna bakin gado tareda cewa Cindy takawo Mata ruwa Mara sanyi.

Ruwa Cindy takawo Mata Tasha kadan ta Haye gadonta ta kwanta sai Alokacin tasake Ajiyar zuciya tana Dora hannunta Kan cikinta daya Dan taso.

Ms Na’ima na shiga daki ta dauki wayarta Dake yashe tsakiyar dakin ko gani Sosai batayi ta Danna Kiran Zinat.

Zinat data kasa barin asibitin sbd yanzu Kam aiki yadawo musu sabo,
Dan kuwa aikine gagarumi ya taso musu bayyanar wannan cikin.

Tana dauka tace”

Na’ima Shiga wannan halin na some some ba naki bane yanzu,
Menene abin Yi Dan Kiran da waccar tsohuwar najadun keyi yasa Dole ansanar da ita yarinyar na asibiti Dan Haka inaga…….

Zinat Ina hanyar zuwa,
Acikin Daren Nan zanyi booking ticket nadawo nayi maganin matsalar Nan kowa ya huta Dan idan bada hannuna nayi sanadin cikin yarinyar Nan ba bazan iya nutsuwaba,
Zinat kafin ki wuce Anne tazo inason kisa ai Mata allurar wata masifar koma wace iri ce Dan wlh zuciyata wuta takeci,

Turakin da akansa nake duk wani Abu danakeyi,
Yaushe Turakin ya samu lafiyar duka duka da har wata zata rigani daukan cikinsa¿
Shin yaushema har Suka sabane har Haka tafaru Banda labari?Tabbas nayi sake Amma wlh sai tayi Dana sanin kallonsama amatsyin Miji bare hada shimfida dashi.

Kashe wayarta tayi tareda .

neman numbern A Abdoul tace tana buqatan ticket na zuwa Nigeria cikin gaggawa.

Bai tsaya tambayar komaiba tunda ba huruminsa bane Dan Haka yace to tareda bincikawa ta waya ba Bata lokaci yayi Mata komai kwana biyu kafin tafiyar.

Kamar zata Ara hauka taji daya kirata ya sanar da ita sai Bayan kwana biyu Dan Haka duk saita qara Shiga bacin Rai Dan kuwa Bata taba Jin Dana sanin baro Nigeria ba sai lokacin.

Acan Nigeria a asibitin kafin Haj Zinat ta san abin Yi akan Sa’adah din Anne ta iso asibitin Dan Haka Dole ta fuske Akan itace takawo Sa’adahn asibitin harma ta biya komai tana jiran isowarsu ne dama.

Anne Bata nuna komaiba saima jinjina Mata tayi da kokarin datai na kulawa da Sa’adah kafin su zo duk da aranta tabbas tasan da wuya idan tsautsayin ne sbd tasan halayensu ita da Aminiyar tata na boye Dana bayyane.

Duk yanda taso samun ganin likita ko nurses din dake kulawa da Sa’adahn Bata samu dama ba Anne ta toshe koina ta hanyar dauke Sa’adah daga asibiti ta aka maida wata Dan Haka damarsu ta lalace saidai ta jira isowar Na’ima su San abin Yi tun kafin cikin yawuce lokacin illatawar.


Laylah kwana biyu gidansu baya cikin kwanciyar hankali sbd gabaki daya sun Rasa gane Kan mum
Ta birkice gabaki daya laifi kadan fadan gaske take rufe mutum dashi har ita Laylan Yar gaban gashinta Bata ragawaba saima tsanarta datake ji ta wani bangaren tunda sun hada jini da Sa’adah duk ba komai yasa batama kawo alaqarsu araiba sanin irin muguwar qiayyar Dake tsakanin Momy da Laylah da uwar Laylah tasan ba lallai akwai qauna a tsakaninsu ba tunda Laylan bamai surutu bace Dan hakanema batasan irin kusanci da qauna Mai qarfi Dake tsakaninsu ba,ita koyaushe kallon ba wata alaqar a tsakaninsu sbd qiyayyar Momy akan Laylan.

1 2Next page

Related Articles

Leave a Reply

Back to top button