RAUDHA 1-END

RAUDHA Page 41 to 50

Ammee tace, “ƙyale shi ai halin sa sai shi in dai Abubakar ne”.

Daga nan hira suka ci gaba da yi. Inda Faruk shima ya dawo ya zauna kusa da su ana yi da shi

Sai da aka kira sallan isha’i kafin su wuce masallaci, su kuma RAUDHA da Ammee suka nufi ɗaki don gabatar da nasu.

           *WASHE GARI*

     Ƙarfe 11:30am RAUDHA ta tashi daga barci, wanka tayi ta shirya cikin riga da skert ƴan kanti, rigan me ruwan madara ne me gajeren hannu, sai kwalliya da akayi da jan zare aka saka Stones, sai kuma skert ɗin ja ne, daga ƙasan an zizara kalan ruwan madara, yana da faɗi skert ɗin sai tsagu ta baya, hula ta saka irin na saƙa me tuntu fari, an yi harafin *R* a gaban da jan zare, flet shoes ta zira a ƙafafun ta ta ɗauki wayan ta tafito Parlour.

      Ammee na zaune ita da wata matashiyar yarinya me kimanin shekaru 22, yarinyan tana da girman jiki da tsaho shiyasa idan ka ganta zaka yi zaton ta haura 25yrs.

       Hango ta da Ammee tayi nan da nan ta washe baki tana nuna mata kusa da ita “ta ƙariso”

Sai da ta gaishe ta kafin ta zauna tana kallon yarinyan da itama take kallon ta

Ammee tace, “ku gaisa mana Suhaima”.

Gaishe ta Suhaiman tayi. RAUDHA ta amsa tana murmushi

Ammee ta sake cewa, “ita ce ɗiyar Baba Iliya, Sauran duk sun zo sun tafi kina barci ban tashe ki ba”.

Murmushi kawai RAUDHA tayi

Sannan Ammee tace, “ta je tayi Breakfast in ya so Suhaima ta raka ta zuwa gidan ta gaishe su”.

Tashi tayi ta nufi wajen dainning, sai da ta gama karya wa kafin ta dawo tana tambayan Ammee su Abubakar

Ammee tace, “Abubakar ya shiga school, Zannurain kuma sun wuce wajen aiki da Uncle ɗin ku, shi ya hana Ni ma in tashe ki, yi maza ɗauko mayafin ki ku je ku dawo”.

Amsa mata tayi da, “to” sannan ta wuce ɗakin, bata jima ba ta dawo riƙe da ƙaramin mayafi a hannun ta baƙi, rataya shi a wuyan ta tayi suka fita da ita da Suhaima

A waje suka iske Faruk na waya, da hannu yayi musu alaman su jira sa. Yana gama wa ya kalle su yana murmushi yace, “sai ina kuma? Sarkin yawo an samu ƙawa ko har an soma jan ta?”

Dariya Suhaima tayi tace, “kai yaya Faruk kai kuma. Ammee ce fa tace in raka ta gidan mu”.

Ita dai RAUDHA murmushi tayi, sannan ta gaishe shi tana cewa, “kai baka je aikin ba?”

Idanun sa akan ta yana murmusawa yace, “ban je ba, sai zuwa anjima zan leƙa, ku mu je in raka ku”.

Tare suka jera suka nufi babban gidan nasu, sashi-sashi suka je da RAUDHA ta gaisa da mutanen gidan, sannan suka yaɗa zango sashin su Suhaima, sun jima suna hira kafin suka fito suka yo gida

RAUDHA anan waje ta bar Suhaima da Faruk suna magana ta shigo gida. Tana shiga ciki Ammee ta tambaye ta Suhaiman? Take sanar mata “tana waje ita da Faruk”.

Hira suka soma yi, can sai ga Suhaima ta shigo ta zauna aka ci gaba da yi da ita.

       Suhaima ita ce yarinyan da suke soyayya da Faruk, da tuni sun yi aure amma yace ba yanzu ba, wai karatu zai koma.

      Sosai RAUDHA take jin daɗin zaman ta a cikin wannan Familyn, kowa na son ta kuma yana nuna mata ƙauna. musamman ma kasancewar ta samu Suhaima, tunda ita mace ce tana jin daɗin zaman su tare, kullum suna yawo a cikin gari, idan basu fita da su Abubakar ba, to Suhaima zata ja ta su fita tare, har gidajen ƙawayen ta suke zuwa tare

Ana gobe zata tafi sai ga Rayyan ya dira gidan, lokacin Ammee ce kaɗai zaune a Parlour ya shigo, tace, “a’a kai kuma daga ina? Saukar yaushe?”

“Yanzu Ammee”. Yayi maganar yana zama

“To aikin kuma fa?”

Murmushi yayi yace, “kai Ammee kya bari mu gama gaisa wa ai ko?”

Taɓe baki tayi tace, “to”.

Dariya yayi yace, “Ammee kenan, wai to”.

Itama dariyan tayi tace, “to in ban ce to ba me kake so in CE?”

Murmushi kaɗai yayi sannan ya gaishe ta. ta amsa tana tambayan sa lafiyan sa da aikin nasa

“Alhmadulillah Ammee, ina mutanen gidan?”

“Ai gaba ɗaya ba sa nan, Ni kaɗai ce, yanzu ma Suhaima da RAUDHA suka fice”.

Numfashi yaja kafin ya miƙe yace, “bari in ci abinci Ammee, yunwa nake ji”.

Wuce wa yayi kan dainning, yaci abincin sannan ya wuce ɗakin sa, yayi wanka ya ɗauro alwala ya tafi masjid, kasancewar a time ɗin ana kiran sallan Azahar ne. Daga can sai ya wuce family House ɗin su don gaida su.

        Babu jima wa su RAUDHA suka dawo gidan, a gajiye suka shigo, sabida yawon da suka sha yau ɗin, Suhaima ma bata zauna ba tayi gidan su

     RAUDHA kuma ɗaki ta shige tayi wanka ta saka riga da skert Robber, light green colour, ta fito Parlour ta zauna akan dainning tana zuba abinci.

     Ammee ce ta fito daga kichen tace mata, “ɗiya ta bari na shiga ɗaki na kwanta zuwa anjima, idan Uncle ɗin ku ya dawo ki tashe Ni”.

“To Ammee”. Ta amsa mata tana ƙoƙarin ɗaukar wayan ta dake ring

Abincin da ta saka a baki take tauna wa tana kallon wayan, number ne shiyasa bata yi peacking ba ta ajiye, taci gaba da cin abincin ta, sake kira akayi, sai da akayi mata Three missed calls kafin ta ɗaga tana kara wa a kunne.

      Daga can ɓangaren Zulain ne yayi sallama

   Ta amsa mishi tana tambayar “waye ne?”

Murmushi yayi yace, “Zulain ne Masoyin ki?”

Ɗan jim tayi don ta manta shi ma

Ya sake cewa, “har kin manta Ni Ko? Uhmmm”.

“Sorry i remember.. but aina ka samu Numba na shi ne abinda ya bani mamaki?”.

“Kin san duk wanda yake son abu, to samuwar hanyar da zai bi don mallakar shi ba abu bane me wahala, Sharif Ya samo min wajen yayan ki”.

“Eyya”. Tafaɗa tana kai abincin baki

“Uhmmm me kike ci haka babu tayi?”

Murmushi tayi tace, “ko zaka ci ne? Shinkafa ne. Duk da dai nasan ba iya cin ciman mu zaka yi ba?”

“Wa ya faɗa miki? Ai muna dafa wa acan”.

“Really”.

“Yes sweetie”.

Dariya kawai tayi taci gaba da cin abincin ta tana sauraron sa.

      A lokacin ne Ray ya shigo parlour’n, idanun sa a kanta ya faɗa yana ganin yanda take sakin murmushin ta me ƙara mata kyau, take yaja numfashi yana sake ƙare mata kallo. Ahankali ya soma takowa cikin parlour’n hannayen sa cikin aljihun wandon sa

    Motsin da taji kaɗan shi yasa ta waigo idanuwan ta suka faɗa kansa, tsayar da idanun ta kawai tayi tana kallon sa a ranta tana mamakin ganin shi ɗin

While shima idanun nasa akanta ne, ya nufo inda take, dai-dai ya ƙariso wajen take faɗin, “ok shikenan zan yi missing naka nima, shikenan ko?”

Daga can Zulain yace, “No ban yarda ba, don nace dai ki faɗa ne kika faɗa, amma Ni kaɗai ne nayi missing ɗin ki”.

Ray tuni ya runtse idanun sa saboda wani irin kishi da ya turniƙe shi, tuni zuciyar sa ta raya masa ba da Suhaib ko Daddy take waya ba. Buɗe ido yayi ya sauke a kanta, sai kuma ya ja kujera ya zauna yana ci gaba da tsare ta da ido

Haka kawai taji baza ta iya ci gaba da wayan a gaban sa ba yana kallon ta, don haka tayi wa Zulain sallama ta kashe wayan

Anan Ray ya sake tabbatar da ba su bane tunda ta kira sunan sa

Abincin ta taci gaba da ci batare da ta kula sa ba, sai tsinkayar muryan sa tayi yana cewa

“Meyasaka kika tsane Ni RAUDHA?”

Take ta ɗago manyan idanuwan ta ta sauke a kansa, kallon kallo suke wa juna ko wannen su zuciyar sa na saƙa masa abubuwa a game da ɗan uwan sa. Ganin kallon da yake mata yana saka ta jin wani iri, sai ta ɗauke nata idon tana mayar wa ga Plate ɗin abincin ta, sai dai tambayar da yayi mata yake kai kawo a ranta amma kuma bata da alamar tanka masa

“Why kika tsane Ni nace? Ko gaishe Ni ba kya son Yi a matsayi na na Yayan ki, why?”

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18Next page

Related Articles

Leave a Reply

Back to top button