RAUDHA Page 41 to 50

Can ya hange ta a sama tana yawo tana wannan dariyan me ban tsoro. Da sauri ya bar ɗakin don kiran sauran ƴan uwan sa
A time ɗin ne Daddy da Suhaib suka zo duba ta
Nan likitan yayi kiciɓis da su, sai ya miƙa musu hannu suka gaisa sannan ya kai su office ɗin sa ya ajiye su, sai ya fita ya bar su suka koma tare da wasu Doctors ɗakin da RAUDHA take ciki
Har a time ɗin tana saman tana shawagi tana wannan mahaukacin dariyan da yake karkasuwa da yawa, suna shigowa ta kallo su da idanuwan ta masu tsananin haske tamkar an ƙara musu haske, har wani walwali suke yi kamar an kunna tocila
Sosai likitocin suka tsorata da wannan al’ajabin, har za su koma sai ɗayan ya dakatar da su
Kamar ƙiftawar ido sai ganin ta suka yi ta koma ƙasa a yashe, gashin kanta ya rufe mata fuska duk ya barbaje
Shi babban likitan shi ya ƙarisa gaban ta ya yaye mata gashin kanta, sai dai da alamun ba ta numfashi, duk inda yakamata ya taɓa don jin tana numfashi amma alamu sun nuna ta sume ne, dama ta saba haka, sai tayi wajen kwana biyar tana barci, ko kuma ta dena numfashi gaba ɗaya, hakan na basu mamaki, amma basu alaƙanta hakan da komi ba, tunda gashi result ɗin su na nuna musu ƙwaƙwalwan ta ta samu matsala sakamakon ƙwayoyin da take sha, kuma koda yaushe suna mata gwaje-gwaje amma abu ɗaya suke gani, duk maganin da zasu ba ta still dai babu ci gaba.
Sake ɗaure ta suka yi da sarƙan, kafin suka soma aiki akanta, bayan sun gama suka fito daga ɗakin, likitan ya nufi Office ɗin sa da su Daddy ke ciki, yana shiga ya sake ba su haƙuri da zaman jiran sa da suka yi, sai da suka sake gaisawa sannan ya soma musu bayani, kamar dai ko yaushe babu wani ci gaba da ake samu
Gaba ɗaya ransu duk a matuƙar damuwa suke sauraron likitan, kullum abu ɗaya yake faɗa musu, duk kuma hanyan da zai kawo yace a gwada, idan an gwada ɗin abu ɗaya ne babu sauƙi, gashi kuma babu yanda za’a yi a fitar da ita wani ƙasan, nan kuma asibitin yana ɗaya daga cikin asibitin da yafi ko wanne ƙwararrun likitoci na masu hauka, da ba don haka ba da tuni sun sauya mata wani wajen, su yanzu har sun fawwala wa Allah komi, sabida kullum babu ci gaba
Ajiyan zuciya likitan ya sauke yana kallon su, sai da ya ɗan ja fasali kafin yace, “sai dai Ni akwai shawaran da nake so in baku idan babu damuwa”.
“Menene likita? Ka faɗa ko wani shawara ne idan har hakan zai kawo samun lafiyan ɗiya ta, muna maraba dashi”. Cewar Daddy da tsantsan damuwa a maganar sa
“Eh to Ni dai a haƙiƙanin hange na da nayi, ciwon ɗiyar ka ba na asibiti bane gaskiya, duba da yanda kuke ta wahala da ita, mu ma kuma muna yi wajen treating ɗin ta, amma kuma har yanzu babu ci gaba, sai kuma abinda ke ɗaure min kai a tattare da ita, musamman idan na je inda take, hakan yasa nayi tunanin tabbas ciwon ta akwai yiwuwar shafan aljanu a tattare da ita, ba wai zan ƙaryata cewa ƙwaƙwalwan ta be taɓu bane a sabili da shaye-shayen da take yi, tabbas hakane, sai dai kuma idan har akwai aljanu a jikinta, to, tabbas babu ta yanda za’a yi maganin da muke mata ya warkar da ita, duba da yanda aljanu suna irin hakan a jikin Mutum, zasu lafe su hana tasirin duk wani magani a jikin ta, haka za’a yi ta wahala da ita a kasa gane meke damun ta, ya kamata a gwada na Islamic tunda an kasa dacewa anan ɗin”.
Daga Suhaib har Daddy zuba ma doctor idanu suka yi suna sauraren sa, har sanda ya dire bayanin sa babu wanda yayi yunƙurin magana, gaba ɗayan su sun tafi ga tunanin abinda ya sa tun farko ba su yi wannan tunanin ba.
[3/19, 10:08 AM] نفيسة أم طاهرة: ????????????????????????????????????????
????????????????????
????????????????????
*RAUDHA*
????????????????????
????????????????????
????????????????????????????????????????
*MALLAKAR:* ✍️
_Nafisat Isma’il Lawal Goma._
*بسم الله الرحمن الرحيم*
⚖
*FEENAH WRITER’S ASSO*????
“`®Ɗaya tamkar da Dubu????✓“`
*JIKAR LAWALI CE*✍️
*Wattapad: UmmuDahirah*????
*F.W.A????/*
.
*NOT EDITED* ___________________________????
*SEASON THIRTY SEVEN*
_______???? Sun daɗe a wajen likitan yana musu bayani, har yayi musu hanyar wani babban Malami dake garin Zaria, kuma sun amince zasu gwada ɗin ko Allah zai sa a dace.
Sai da suka duba RAUDHA kafin suka bar asibitin.
A cikin kwana biyu har an gama shirye-shiryen yanda zasu tafi da RAUDHA zuwa Zaria, tunda an rigada an sanar wa malamin kuma ya ce a kawo ta, gaba ɗayan su zasu yi tafiyan har Farida, tunda dama gida ne zasu koma shiyasa zasu tafi gaba ɗaya
Rayyan ya so ya bi su, sai dai yanayin aikin sa bazai bar sa ba, dole ya haƙura ba don ya so ba.
A jirgi suka isa Zaria, gidan Daddy suka sauka inda anan ne Malamin zai zo ya riƙa duba ta, bisa alfarman da Daddy ya nema a wajen sa, (Chemist) cibiya ce babba suke da shi a Zarian, wanda aikin su ne cire ma mutane aljanu
A ranan da suka zo, a ranan ne Malamin da zai duba ta shima ya iso gidan, a time ɗin RAUDHA na barci ne sabida alluran barcin da aka yi mata daga can asibiti, saboda samun sauƙin tahowa da ita
A tare da Daddy da Suhaib suka raka sa ɗakin da aka ajiye RAUDHA, sai da ya nemi abubuwan da yake buƙata wajen su, sannan ya zauna ya saka mata magani a cikin kasko, ta yanda idan har tana da aljanu dole zasu bayyana kansu idan turaren ya shiga hancin ta
Ilai kuwa, ana saka wa sai ta farka a firgice, gaba ɗaya zubo musu idanu tayi tana kallon su tamkar zata cinye su, sabida yanda ta waro idon nata waje, sai yamutsa fuska take yi tana cije baki
Malamin ta kafa ma idanu, wanda shima ita yake kallo, nan da nan idanun ta suka soma sauya kala zuwa ja, sai ta kawar da kai ta koma ta kwanta batare da ta sake ko motsi ba
Su dai su Daddy suna zaune akan sofa suna kallon ta, ko wannen su ya buga tagumi
Ajiyan zuciya Malamin yayi kafin ya kalli su Daddy yace, “tabbas yarinyan ka tana da aljanu a jikin ta, da alamu dai manya ne, saboda duk wanda na saka mishi maganin nan, dole ne su tashi a lokaci ɗaya su bayyana kansu, amma kuma ita ba haka ba, sai dai ta yanda ta farka ɗin nan, da kuma yanda idanuwan ta suka sauya kala, to, tabbas tana tare da su. Insha Allahu zamu fara aikin mu nan ba da jima wa ba idan abokan aikina sun zo, zamu fara mata ruƙiya ne su fara bayyana kansu, sannan mu san abun yi”.
Suhaib da Daddy jinjina kai suka yi alamun gamsuwa.
Suna nan zaune Sai ga wasu Maza su kusan biyar sun shigo ɗakin
Malamin kallon su yayi yace, “su zauna su soma karatun”.
Gaba ɗaya zama suka yi suka zagaye RAUDHA da har yanzu tana kwance idanu a rufe taƙi motsawa
Karatu suka soma yi da ƙarfin muryan su. sun daɗe suna karatun amma RAUDHA bata yi wani motsi ba, su kuma basu fasa karatun ba, sai da suka ɗau kusan mintuna talatin suna karatu kafin ta soma wani irin gurnani har yanzu idanun ta a rufe, hakan yasa suka sake dage wa suna sake ɗaga murya, nan da nan ta soma ihu tamkar wani ƙaton gardi, kukan yana fita ne kashi-kashi wanda baza ka gane na mutane nawa bane, kukan kawai take yi bata motsa ba, kuma idanuwan ta a rufe
Sai malamin ya tashi ya matso kusa da kanta, ya soma yin wasu addu’o’i yana tofa mata akai, yayinda sauran mutanen suka ci gaba da karatun Alqur’ani da iyakan ƙarfin su, idan suka zo wasu ayoyi na jinnu sai suna maimaita wa kafin su wuce