RAUDHA Page 41 to 50

Da ya nemi ra’ayin ta akan school ɗin da zata shiga
Sai ta ce masa tana son abroad ne
Da sauri Daddy ya kalle ta ya ce, “haba Baby taya zan bar ki ki je wani ƙasa karatu bayan kin san halin da ake ciki yanzu? Ga kuma halin da kika shiga a baya, ki zaɓi dai inda kike so anan don ba na son kiyi nesa dani”.
Shagwaɓe fuska tayi ta hau buga ƙafa a ƙasa tana hawaye
Janyo ta yayi jikin sa ya hau rarrashin ta, sai da ya ga taƙi haƙura, don daga ƙarshe saka mishi kuka tayi, sosai yake ƙaunar ta, domin soyayyar ta bazai iya bari yana gani tana neman abu ya hana ta ba, sai yace mata, “yi shiru to, faɗa min wani ƙasa kike so ki je umm Baby na?”
Cikin shagwaɓa tace, “Daddy Saudia zaka kai Ni, can nake so sabida in koyi addini sosai, tunda ka ga ban iya komi ba, ka ga idan na je can zan shiga school ɗina, sannan zanna riƙa islamiyya sosai a can”.
Washe baki Daddy yayi yana sake rungume ta ya ce, “iyeeeee ashe Baby na ta girma haka? Ashe kina da wayau? Good dear gaskiya naji daɗin zancen ki”.
Dariya ta ƙyalƙyale dashi cike da farin ciki itama
Nan Daddy yayi ta nuna farin cikin shi, kafin yayi mata alƙawarin zai nema mata insha Allahu idan har an dace, tunda a time ɗin ba kasafai ake bari fita Abroad ba, su ma can ɗin ba sa bari a shigo musu ƙasa.
Koda Daddy ya sanar da Suhaib shima yayi murna sosai, sai dai kuma ba su so tayi nisa da su har haka ba, amma kuma sun san can ɗin zai fi nan, tunda zata je ta nemi ilmin addini ne, kuma can shine garin musulunci, ta yiwu idan ta dawo ma ta zama wata Malama Sheikhiya, hakan da suke tuna wa shi ke saka su jindaɗi sosai.
Babu jima wa Daddy ya soma mata cuku-cukun fitar da ita zuwa Saudia, sai dai ba’a saki hanya ba har yanzu, dole Madina zata tafi tunda can anfi barin mutane zuwa, Saudia kuwa ko ƴan zuwa hajji an hana su zuwa.
Da labarin tafiyan ta ya iske Rayyan, ya shiga wani hali sosai, har faɗa sai da yayi wa Suhaib wai “akan me za su tura ta wani ƙasa bayan sun san halin da take ciki? Kuma yanzu sai su ƙara barin ta tayi nesa da su?”
Sosai Suhaib yayi mamakin faɗar Rayyan ɗin, har dai ya ce, “wai Dude ko dai akwai abinda kake ɓoye min ne a game da Baby?”
“Kamar ya fa?” Cewar Rayyan ɗin
“Ina nufin faɗan yayi yawa, ko matar ka ce sai haka ai”.
“Ok kana nufin Ni ban isa inyi mata faɗa a matsayin yayan ta ba ko?”
“A’a ba haka nake nufi ba, ina..”
Cike da ɓacin rai Rayyan ya tari numfashin sa da faɗin, “haka kake nufi mana, Ni ban isa da ita ba, kana son ka nuna min banbanci tsakani na da ku, tunda har ku kun yarda Ni kuma asuwa da zan hana ta”.
“Haba Dude wlh baka fahimce ni bane, meye na zafi haka abinda be kai ya kawo ba?”.
Ƙitt ya kashe wayan
Sosai Suhaib ya sake mamaki da halin da Rayyan ya nuna masa, ya san shi ba mutum bane me yawan ɗaukan zafi akan abu, idan kuwa ka ga fushin sa, to, tabbas ba abu bane ƙanƙani, har yana mamaki da kasancewar sa ya zaɓi soja, domin kuwa ko kusa aikin be kamace sa ba, yana da sauƙin hali sosai, idan har ba ka ƙure sa ba ne, to shine zaka ga ainihin waye shi, a nan ne zai nuna maka haukan sa tuburan.
Sake kiran sa yayi, daƙyar ya amsa call ɗin, sosai Suhaib ya ba shi haƙuri
Shi kuma a lokacin shima ya sauko kaɗan, don ba kaɗan yayi fushi ba, har yanzu baƙin cikin tafiyan RAUDHA wani ƙasa ne ke nuƙurƙusan shi
Anan suka shirya har suna taɓa hira kafin su kashe wayan, aran Suhaib dariya kawai yayi ya ce, “uhmmm idan tayi tsami ma ji”.
????????????????????????????????????????
Komi na tafiyar RAUDHA ya gama kammaluwa
A washe garin ranan da zata tafi haka Ramcy ta zo ta wuni mata har zuwa dare, sannan ta tafi.
Washe gari Daddy da Suhaib da ya zo don yin sallama da ita, su suka kai ta har airport, sai da tayi ta kuka kafin ta yarda ta shiga jirgin
Ahaka suna ɗaga mata hannu har jirgin ya tashi, sai da dukan su suka share ƙwalla kafin suka juya suka shiga motan su, suka bar wajen ko wannen su cike da kewar RAUDHA.
.
_muna miki fatan alkhairi RAUDHA, sai mu ce sai kin dawo._
_Nima zan tafi hutu har sanda RAUDHA zata dawo._ ????????????????????
????????
????????
[3/19, 8:47 PM] نفيسة أم طاهرة: ????????????????????????????????????????
????????????????????
????????????????????
*RAUDHA*
????????????????????
????????????????????
????????????????????????????????????????
*MALLAKAR:*
_Nafisat Isma’il Lawal Goma._
*بسم الله الرحمن الرحيم*
*FEENAH WRITER’S ASSO*????
“`®Ɗaya tamkar da Dubu????✓“`
*JIKAR LAWALI CE*
*Wattapad: UmmuDahirah*????
*F.W.A????/*
.
*NOT EDITED* ___________________________????
*SEASON THIRTY NINE*
_______???? *AFTER FOUR YEAR’S.*
Gaba ɗaya haraban airport ɗin ya cika maƙil da jama’a, ciki kuwa har da ƴan jaridu waɗanda suka zo domin samun rahoto, sabida zuwan Jikan Sarkin American da zai bayyana a ƙasar ta mu
Sai dai kuma jami’an tsaro sun hana kowa shiga cikin haraban airport ɗin, har ta da ma su zuwa ɗaukan ƴan uwan su, sai dai suka faka motocin su daga can nesa
Suhaib na ɗaya daga cikin mutanen wajen, yana tsaye jikin motan sa yana jiran saukar jirgin, sosai idan ka kalli fuskar sa zaka ga bayyanuwar tsantsan farin cikin da yake ciki a wannan ranan, saboda dawowar ƙanwar ta sa.
Koda jirgin ta gama sauka sai mutane suka fara fito wa, can na hango wata kyakykyawar cikakkiyar kamilalliyar budurwa tana sauko wa, a ƙalla shekarun ta bazai wuce 24years ba, tsananin kyauwun ta da hasken ta sai da duk wanda ke haraban wajen idan har idanuwan sa sun sauka a kanta sai ya kasa ɗauke ido a wajen ta, a zuciyar sa yana sarkake Allah da yayi wannan kyakykyawar halittan
Tana sanye da doguwar rigan abaya baƙa ce, daga saman gaban rigan har ƙasa an saka kalan ruwan ƙasa, sai aka bi wajen da kwalliyan stones masu tsananin ƙyalƙyali me ban sha’awa, ta yane kanta da ɗankwalin abayan, sai ta toshe idanunta da wani faskeken baƙin Glasses da ya sake ƙawata farar fuskar ta, sak idan ka ganta tamkar wata balarabiyya sabida shigan ta da yanayin ta, baza ka taɓa cewa ita ɗin ta haɗa jini da bahaushe ba, Bahaushen ma Bazazzage.
A hankali take taka matattaƙalan benen, wanda hakan yayi matuƙar ƙosar da matashin saurayin dake bayan ta, shi ɗin yana sanye da riga da wando baƙaƙe ne ma su tsananin kyau da tsada, ya saka rigan sanyi ja me hula, wanda hakan yasa ya rufe kansa da hulan, tare da saka faskeken Glasses a fuskar sa, wanda ya ba shi damar ɓoye fuskar sa gaba ɗaya. Sosai ya ƙosa da ya bar wajen tun kafin asirin sa ya tonu, shi ɗin mutum ne da ba ya son mutane bare kallo, shiyasa ya zaɓi ɓoye kansa batare da an yi talla da shi ba.
Ta Geben ta ya raɓa ya wuce, hakan yasa ya ɗan bige ta har wayan hannun ta ya so kubce wa, sai dai tayi saurin tare wa tana ɗago kai tabi bayan sa da kallo, wanda shi tuni har ya ƙarisa sauka kan benen ma
Dogon tsaki taja, ahankali ta furta, “Useless”.
Tsakin nata kaɗai yaji, don haka ya juyo don ganin wacce har ta samu damar iya masa tsaki. Akan kyakykyawar fuskar ta ya sauke, sai kawai ya ware idanun sa sosai yana kallon ta
Ita kuwa a time ɗin ma ta mayar da hankalin ta kan wayan ta tana latsa wa, har tazo ta wuce sa batare da ta sake bi ta kansa ba, ba ma tasan Allah yayi ruwan tsakin sa ba