RAUDHA 1-END

RAUDHA Page 41 to 50

Murmushi Ramcy tayi tace, “again?”

Dafe goshi RAUDHA tayi, sai kuma ta kwaɓe fuska tace, “sorry Besty na rigada na saba, sai kin yi haƙuri dani”.

Ramcy zata yi magana, sai wayan RAUDHA ta soma ringing na waƙar larabci me daɗi

Hannu ta saka ta ɗauki wayan tana murmushi tun kafin ta kai ga duba wa, domin ta san mutum ɗaya ne ta saka mishi wannan ring ɗin. Peacking tayi ta kara a kunne, sai ta narke fuska tace, “nayi fushi Ni dai”.

Murmushi kaɗai Ramcy take saki idanun ta akan RAUDHA ɗin, sosai take tsananin burge ta da yanda ta sauya gaba ɗaya, sauraron ta take yi duk da ba ta jin abinda wancan yake faɗa, har ta gama bata ɗauke ido akan ta ba

Hakan yasa RAUDHA da ta cire wayan daga kunnen ta ta ɗage mata gira tace, “lafiya! Kallon fa?”

Still Murmushi Ramcy ta saki tace, “kina tsananin burge Ni ne, ta yanda kika iya tafiyar da soyayyar ki da Ƙalbin ki (dayake haka take ce mishi, kuma har su Daddy babu wanda be san hakan take kiran sa da shi ba, sai dai babu wanda ya san shi har yanzu), ko a mafarki idan wani yace min zaki riƙe soyayya irin haka, zan ƙaryata shi, domin kuwa na fi kowa sanin wacece ke akan yanda kika riƙe so”.

Murmusawa RAUDHA tayi tace, “ai ada ne ba yanzu ba, yanzu ke ma ba ga shi ba har an kusa a shafa fatiha? Bigaddin nazri anil waƙti, (komi da lokacin sa)”

“To yaushe ne zaki nuna mana shi, har yanzu kina min rowan shi na rasa meyasa?”

Lumshe ido tayi tana buɗe wa akan Ramcy, kafin tace, “ƙariban jiddan”. Sai kuma tayi murmushi tace, “sorry Besty, a mean very soon”.

“Ok Allah ya Kai mu”.

“Kin san naji daɗin yanda za’a yi bikin nan naki dani? Tabbas da ina school ne dole sai na ajiye na dawo”.

Ramcy tace, “wa ya isa yayi min aure babu Besty kusa? Ai wlh da bazan taɓa aure ba in dai har sai nayi aure ne kafin ki dawo, dole na saka aka ɗaga”.

“Hal haƙƙan? A mean really?” Tayi saurin sauya zancen tana ɗaura hannun ta a goshi

Ramcy na dariya tace, “yeap I’m sure, but Nima dai dole zan koya larabcin nan ko dan mu riƙa yi, tunda muna baki wahala”.

Dariya itama RAUDHA tayi tace, “ai na dawo da sannu zan rage kar ki damu”.

Daga nan hira suka ci gaba da yi, har time ɗin da Farida ta zo, sai lokacin RAUDHA ta miƙe ta shiga wanka tayi tafito, ta shirya cikin farar jallabiya me hula, ta saki hulan a bayan ta, sai ta ɗaura wani hulan daban

Parlour’n ƙasa suka sauka, inda acan suka haɗu gaba ɗaya ana ta hira, sosai RAUDHA ta maƙalƙale su Haneep tana ta musu wasa, musamman Abdul da ya fi surutu. Sosai take tausayin Haneep sabida rashin lafiyan sa, ko magana be cika yi ba, idan ya zauna ya dinga zilalar da miyau kenan, gaba ɗaya gaban rigan sa sai ya jiƙe, a rana sai a sauya masa kaya babu adadi sabida ɓata wa da yake yi, ga shi ko maganar sa ba ya wani fita sosai, hannun sa ɗaya kuma ashanye duk da yana iya sarrafa shi, wai Nan ma don an ta magani ne.

    Anan Ramcy ta wuni sai dare ta tafi gida, sai gobe zata dawo tunda za’a shirya wa RAUDHA partyn murnan kammala karatun ta.

[3/21, 12:10 PM] نفيسة أم طاهرة: ????????????????????????????????????????

????????????????????

????????????????????

   *RAUDHA*

????????????????????

????????????????????

????????????????????????????????????????

*MALLAKAR:* ✍️

              _Nafisat Isma’il Lawal Goma._

*بسم الله الرحمن الرحيم*

 

*FEENAH WRITER’S ASSO*????

“`®Ɗaya tamkar da Dubu????✓“`

*JIKAR LAWALI CE*✍️

*Wattapad: UmmuDahirah*????

            *F.W.A????/*

*TARIHIN FARILTA SALLAH*

        “`An farilta sallolin nan biyar ne gabanin ƙaura, watau hijira, da shekara ɗaya da rabi. Sallah ce kaɗai ibadar da aka farilta ta a sama a daren Isra’e, kamar dai yadda aka ruwaito a hadisin nan na Anas. Da farko an umurce shi da Sallah guda hamsin ne; da sannu aka dinga rage su har suka zama biyar a bisa roƙon da shi Manzon ya yi wa Ubangijin sa. Da suka zama biyar, sai Allah ya ce masa su biyar ɗin nan, dai-dai suke da hamsin.

   Malamai da yawa sun yi bayanin yadda sallar ma’aikin Allah, mai tsira da aminci, take gabanin Isra’en.

Wasu malaman sun ce, “Gabanin Isra’e, babu wata sallah wadda aka farilta sai sallar dare (Ƙiyamul lail) wadda aka umurci ma’aiki da yin ta ba da iyakataccen lokaci ko adadi ba, kamar yadda yake a suratul Muzzammil, ayoyi huɗu na farko:

    “Ya wanda ya lulluɓe! Ka tsayu domin yin Sallah a cikin dare (duka) face kaɗan, rabin sa, ko ka rage abu kaɗan daga gare shi, ko ka ƙara kansa…        Ma’aikin Allah ya kasance yana yin sallar a kashi biyu cikin uku na dare ko a rabin sa ko kuma sulusin sa. Musulmi suka dinga yi tare da shi kamar shekara guda har suka gaji; daga nan sai Allah ya shafe ta don jin ƙan su.

       An ruwaito cewa sallar da Musulmi suke yi gabanin tafiyar dare suna yin ta ne kafin faɗuwar rana da kafin ketowarta kamar yadda yake a sallah littafin Almanhalil Azb. Gabanin ƙaurar Annabi zuwa Madina raka’o’in sallah bibbiyu ne, bayan ƙaura ne suka zama hurhuɗu, illa magriba da ta kasance raka’a uku, ita kuma sallar subahi ta tsaya a kan biyu saboda dogon karatun da ake yi cikin ta. Buhari da Ahmad sun ruwaito daga Nana A’ishah cewa, “an farilta sallah raka’a bibbiyu, bayan ƙaura ne aka mai da ita raka’a hurhuɗu, amma an bar sallar tafiya a kan raka’a ne bibbiyu, sai sallar magriba ita ko da ma raka’a uku-uku ce.”

        Allah ya sa mu dace.“`

.

  *NOT EDITED* ___________________________????

        *SEASON FORTY*

_______???? Daga airport kai tsaye Zaria me Taxi ɗin ya wuce da shi, can cikin tudun jugun; gonan ganye. A bakin tanƙamemen wani baƙin gate aka sauke sa, ya fito ya saka hannu cikin aljihun sa ya fiddo kuɗi, kuɗin irin na American ne, sai ya kalli me Taxi ɗin sannan ya kalli kuɗin, guda biyu ya zara ya miƙa masa batare da ya ce komi ba

Me Taxi ya tsaya sakaka da baki yana kallon sa, sai kuma ya ce, “bawan Allah ban san ya zan yi da wannan kuɗin ba, kana gani wannan ai ba na Nigeria bane”.

Sai a time ɗin ya sauke hulan kansa, fuskar sa ta bayyana duk da ba duka bane, kasancewar akwai Glasses. Murmushi yayi cikin harshen sa da be gama iya hausan ba ya ce, “I know, but ka amsa idan ka sauya dana Nigeria 10k ne”.

Zaro ido drever’n yayi, sai kuma ya washe baki cike da murna ya saka hannu ya amsa, nan ya soma mishi godiya

Sai dai shi murmushi kaɗai yayi ya juya ya nufi bakin Gate ɗin, hannu ya saka ya tura small door ɗin dake buɗe

Me gadi dake zaune saman benci kusa da Gate ɗin, ya kara rediyo a kunnen sa idanuwan sa a rufe. jin ƙaran buɗe Gate, firgigit yayi ya miƙe yana nufo sa, be gane sa ba sai da ya iso gaban sa, sai ya washe baki ya ce, “ranka ya daɗe kai ne?”

Murmushi yayi masa, ya gyaɗa masa kai

“To ai an tafi ɗauko ka, baka gansu bane?” Me gadi ya sake faɗa cike da fara’a

Still Nan ma gyaɗa masa kai yayi, yayi hanyar gidan zai bar wajen

Biyo sa me gadi yayi yana mishi barka da zuwa, har bakin ƙofan shiga parlour’n ya rako sa, sannan ya juya

Shi kuma ya buɗe ya shiga, babu kowa a cikin parlour’n sai t.v dake aiki, ƙamshin daɗi ya cika ko ina, tsaya wa yayi a tsakiyar parlour’n yana bin ko ina da kallo, har hotunan dake cikin parlour’n na mutanen gidan, tare da iyayen sa da kakannin sa, murmushi kaɗai yake zuba wa yana ci gaba da taka wa zuwa cikin parlour’n.

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18Next page

Related Articles

Leave a Reply

Back to top button