SARAN BOYE COMPLETE

★★★
Tunda suka ajiye wayar baba malam ya shiga dogon nazari, harga ALLAH yana jin son Yoohan cikin ransa. hakan har mamaki yake bashi wani lokacin. Duk da yasan UBANGIJI kan jefa soyayyar wani a zuciyar wani batare da wata alaƙa ba a tsakaninsu
Har yanzu baisan abubuwa da yawa ba dangane da Yaron ba, amma sai ya keji zuciyarsa na tsananin ƙyautata masa zato akan abubuwa da dama na rayuwar yau da gobe. Haɗuwarsu ta uku kenan kacal. Amma ya fahimci wasu ƙyawawan halayya da ko a cikin musulman ma ba kowane ke da su ba. Ga ƙyauttawa da yarda da yaron ke bashi ɗari bisa ɗari.
Numfashi ya ɗan sauke wani gefen zuciyarsa na sake ƙarfafa masa gwiwa akan alkarin da yake shirin aikatawa. Yayinda can kuma wata ke gargaɗarsa musamman akan ahalin da Yoohan ɗin ya fito.........
“Malam lafiya kuwa ka zurfafa a tunani haka?”. Umm data shigo tun ɗazun tanata sallama bai jiba ta faɗa tana mai katsesa.
Ajiyar zuciya ya sauke da sauri tare da kallonta. Gefensa ya nuna mata da hannu alamar ta zauna. Batare da tayi musu ba ta zauna kuwa idanunta a kansa. Hannunsa ya saƙala cikinnata yana ɗan sake furzar da huci. “Jannat wani al'amarine yanzun nan UBANGIJI ya saƙaminshi a cikin tunanina akan yaron nan dana sanar miki jiya ya musulunta. Sai dai kuma wani sashi na zuciyar tawa yana gargaɗina dason jefani a kokwanto game da al'amarin”.
“Tom nidai a nawa tunanin sai naga kamar shaiɗanne Malam. mizai hana ka bama al'amarin wani ɗan lokaci haka, sai ka duƙufa neman zaɓin ALLAH akan yuwuwarsa ko barinsa”.
“Eh tabbas kinzo da shawarar hankali Jannat. Insha ALLAHU kuma zanyi amfani da ita. Amma kema inason ki tayani dan ALLAH”.
“Insha ALLAHU zan tayaka Abban Nu'aymah, ALLAH ya tabbatar mana da alkairinsa”.
“Amin ya rabbil-alamin”. Ya faɗa cike da jin nutsuwa da gamsuwa akan shawararta”.
__★★★
Kwanakin Nu'aymah uku a asibiti aka sallamota. Alhmdllh jikinta yayi ƙyau sosai, sai dai haɗarin da Doctor ya tabbatarma iyayenta tana a ciki akan iya fuskantar loosing mamory shine ya jefasu a cikin matuƙar damuwa.
Yayinda ita kuma da batasan mike faruwa ba sai tata matsalar ta zama Naser. Dan a kwanaki biyun nan daya ɗauka da zuwa gaba ɗaya ya takurama kowanne irin motsinta. Duk da daga gaisuwa babu abinda ke sake haɗasu sai magana kamar kowa. Amma kallon da yake jifanta da shi da tarewa a asibiti da yayi ya tabbatar mata cewar zuwan nasa akwai manufa.
Tun bayan dawowarsu gida Umm ta taimaka mata tai wanka taci abinci da magungunanta ta kwanta danta huta. Shine ta samu damar yin tunani akan Naser ɗin. Kamar daga sama ta dinga jiyo hayaniya na tashi a gidan, sosai mamaki ya kamata, duk da ta tabbatar hayaniyar bata faɗa bace tasan wannan ba ɗabi'ar mutanen gidansu baceba hakan. ‘To minene ya faru?’ ta faɗa a fili cikin sake zurfafa mamakinta.
Kusan mintuna ashirin sai kuma taji hayaniyar ta lafa. bata ko motsa ba balle ai tunanin zata fita ta ganoma idanunta, haka ta cigaba da kwanciyarta tun tana tunani har barci mai nauyi ya ɗauketa saboda a maganin nata akwai na barci daman.
Kiran sallar magriba ne ya saka Umm shigowa ɗakin Nu'aymah ta tadata. Da ƙyar ta samu ta tashi dan barcin nata yayi nisa sosai. Taimaka mata tayi tai alwala kafin tai yunƙurin fita zata barta.....
“Umm wai hayaniyar mi naji anayi ɗazun?”. Ta faɗa cikin katse hanzarin Umm dake ƙoƙarin fita.
Batare da Umm ta juyo ta kalleta ba tace, “Su Abdallah ne, sunma shigo dubaki kina barci”.
Sosai gaban Nu'aymah ya faɗi, sai dai kafin ta sake cewa wani abu Umm ta fice abinta. Shiru tai tsaye hannunta riƙe da hijjab, dan zuciyarta cike take da tambayoyin miya kawo su Yah Ab ɗin gida a yanzun bayan kuma shine da kansa yacema Hajjo sai bikin su aunty Hajarah daya rage saura kwanaki ashirin cif yau ayi. Ganin bata da mai bata amsarta sai ta saka hijjab ɗinta ta kabbara salla kawai.
Koda ta idar bata fitaba tai zamanta a ɗaki, sai da tai sallar isha'i da shafa'i da wutiri sanna ta fito falonsu danta ɗansha iska. Umm kawai ta tarar zaune. Ta zauna kusa da ita tare da ɗora kanta a gefen kafaɗarta.
Ɗan kallonta tayi, kamar zatai magana sai kuma ta fasa ta ɗaura hannunta a wuyanta. Jin jikinta babu wani zafi ya saka Umm sauke ajiyar zuciya da janye hannunta.
“Umm nafa warke”. Nu'aymah ta faɗa tana murmushi dajin ƙaruwar ƙaunar mahaifiyar tata a cikin rai. Itama Umm Murmushin tayi, ta shafa kumatun ɗiyar tata da faɗin, “Ai haka muke fata Nu'aymah, ALLAH ya ƙara miki lafiya dai damu baki ɗaya”.
“Amin Umm”. Ta amsa mata zuciyarta cike da damuwa. tasan iyayenta suna cike da damuwar halin data tsinci kanta, basu da damuwa sama da lafiyarta, basu kuma da burin da ya wuce su wayi gari suga ta warke.........
Sallamar Adawiya ta katse tunanin Nu'aymah. Ta ɗan ɗago daga kafaɗar Umm tana amsawa. Sai dai ganin harda Yah Abdallah ya sata maida kan ta sake kwantarwa zuciyarta najin zafin kishi a kansa.
Rungumeta Adawiya tayi cike da munafincin data saba nunawa idan suna a gaban mutane. Itama sai Nu'aymah ta tarbeta fuskarta fes. Umm dai cike da jin daɗi take dubansu. Yayinda Abdallah kam kallonsu kawai yakeyi.
Bayan sun gaisa da Umm, Nu'aymah ta gaida Abdallah batare data yarda sun haɗa ido ba duk da kuwa shi hakan yake buƙata tun ɗazun. A tunaninta zasu tafi ne, amma sai taga sunyi zamansu sunata hira da Umm. Kusan mintuna talatin basu da ko niyyar tafiyar, takaici ya cika Nu'aymah, dan haka kawai yau itama sai takejin zafin Adawiya akan Abdallah. Shiyyasa hirarma bata saka baki, tana lafe jikin Umm tamkar wata mage.
Basu bar sashen ba har sai da Baba malam ya shigo gidan, dama shi suke jira. Zama kuwa yay suka gaisa a ransa yana mai jin daɗin ganin yanda Adawiya ta kwantar da hankalinta. Yanda tai ƙiba ta ƙara ƙyau kawai ya isa fahimtar da mai kallonta hankalinta a kwance yake sosai. Barci ne ya sake kwashe Nu'aymah har suka bar sashen bata saniba. Koda Umm datai tunanin anan Adawiya zata kwana amma taga saɓanin hakan sai da ta tashe Nu'aymahr ma ta rakata ɗakinta saboda barcin da tayi.
Washe gari Nu'aymah ta tashi ne duk a takure. Ba komai ya jawo hakanba sai zuwan su Yah Ab da zaman Naser a gidan. Maƙalewa tayi a sashensu taƙi fita har rana. Sai da Umm ma ta takura mata ɗaukar abincin Hajjo ta kai mata sannan ta fita badan taso ba.
Tunda taga takalma birjik a ƙofar Hajjo taji kamar ta juya. Amma gudun kar Umm tai mata faɗa sai ta daure tayi sallama. Sai da aka bata izinin shiga sannan ta shiga da wata sallamar a bakinta. Duk samarin gidanne a she. Sai Rufaida da Hajjo. Nu'aymah ba wani shiri sukeyi da Rufaidah ba itama, dan ta girmesu, gata kuma da shegen son girman tsiya, shiyyasa take ganin sai dai su bita. Ita kuma Nu'aymah tsiwa.
A tare kawai tace dasu “Ina yinin ku”. batabi takan dawa-dawa ya amsa ba ta nufi Hajjo daketa binta da kallon jin daɗin ganin jikinta ya sake warwarewa.
“Hajjo barka da gida. Ga abinci inji Umm na”.
“To takwara sannu kinji, yaya jikin naki?”.
“Naji sauƙi Hajjo”.
“Alhmdllh ai haka akeso dama. Tun ɗazun nake tsumayen ganinki amma shiru. Tashi ki duba a firiji na ajiye miki fura”.
Sosai daɗi ya kanata. Cike da ɗoki ta nufi fridge ɗin hajjo ta ɗakko kofin furar tana sakema hajjo godiya. Har zata fice Naser ya kirata. Badan tasoba ta amsa tare da juyowa tana kallonsa. Ya sakar mata sassanyan murmushi tare da miƙewa ya nufo inda take tsaye. Bayare da yay magana ba yay gaba da mata alamar ta biyoshi.
Bataso hakanba, amma sai ta bisa kawai gudun kar yaga kamar ta masa wulaƙanci. Ɗaya daga rumfar bunun da aka jera guda uku a harabar gidan ya nufa. Nu’aymah ma dai na biye da shi. Kujera ya ja mata baya yace ta zauna. Nanma bata musaba tayi yanda yake buƙata. Sai da ta zauna sannan shima yaja wata ya zauna.
Yana zama Abdallah na isowa wajen kamar daga sama. Daga ita har Naser kallonsa sukai. Yayi kicin-kicin da fuska tamkar zai fasa ihu. Batare da yace dasu uffanba yaja kujerar ɗanyan gefen Nu’aymahn ya zauna suka sakata a tsakkiya.
‘Ikon ALLAH ’. Nu’aymah ta faɗa a cikin ranta tana kallonsu da mamaki.
“Alhaji lafiya kuwa?”. Naser ya faɗa a lalace yana kallon Abdallah. Murtani Yah Ab ya maida masa cike da dizgi. “Itace ta kawo haka”.
“Humm!” Naser ya faɗa yana ɗauke kansa daga garesa ya maida ga Nu'aymah da mamaki ke cigaba da nuƙurƙusarta a zuciya.
“Kayi haƙuri ka bamu waje magana nakeson yi da ita Abdallah”.
“Wannan isar ce kuma baka yiba. Duk abinda zaka faɗa mata inhar kasan ba mara ƙyau bane ka faɗa a gabana mana”.
“Mtsoww! Ai kasan baka isa sakani yin abinda banyi niyya ba. Nu'aymah tashi muje can...”
Batayi niyyar binsaba a yanzu. Tayi niyyar kawai tabar musu wajen. Sai dai tana yunƙurawa zata miƙe Abdallah ya daka mata tsawa. “Koma ki zauna kona mareki!!”. Ya faɗa yana ɗaga hannun tamkar zai maketa.
Ɓata fuska sosai tayi tamkar zata fasa kuka. Dan ita kam sun sakata a tsaka mai wuya.
A fusace Naser yace, “Abdallah karka bari nakai bango da kai, wai shin ina ruwanka dani ne? Naga dai Nu'aymahr nan ba matarka bace balle kace zakama mutane iko. Idan ada kayi ikon saboda akwai alƙawarin aure a tsakaninku yanzu saika tuna babu wannan. Ita ɗin allura ce cikin ruwa mai rabo ka ɗauka........”
“Nine mai rabon kuma insha ALLAHU!!, dan haka ka kama kanka karka bari a jimu da kai Naseer”.
“Hhhhhh! Abin dariya. Sannu Abdallah ubana mai bani umarni. ai ka sani kayi sake tun a farkon dama, a yanzu kuma ta suɓuce maka har avada. A da canma dan ba'a bata dama bane akaso mata auren dole da kai, amma sai UBANGIJI yay dubeta ya hana hakan.....”
“Naser!!!”
Abdallah ya kirashi cikin ƙaraji da fusata tare da dunƙule hannu tamkar zai kai masa naushi. Ƴar zabura baya Naser yayi kamar irin yaji tsoro ɗin nan. Sai kuma ya kwashe da dariya ya kuma ɗaure fuska duk a lokaci ɗaya. “Oh to ko dukan nawa zakayi ne?!”.
Bai gama rufe baki ba kuwa Abdallah ya kai masa naushi. Da sauri Naser ya duƙe naushin yabi iska. Ya sake kai masa wani Baba malam da ke bayansu shi dasu Abbah ya daka musu tsawa.
“Kai!! wane irin shashanci ne haka kukema mutane a cikin gida da hankalinku?. Ko kunya bakujiba kuka zauna faɗa a gaban ƙaramar ƙanwarku, wannan ai rashin hankaline da sakarci”.
Duk ƙasa sukai da kawunansu kowa na huci. Abban su Adawiya yace, “Ku wuce muje ciki. Kema Nu’aymah shige”.
Sum-sum ta wuce tana danne dariyar dake cinta a rai tun fara rigimar yayun nata. Tana shiga falonsu kuwa ta fashe da dariya. Da sauri Umm da Rabi dake a kitchen suna aiki duk suka leƙo.
“K lafiyarki kuwa kike wannan dariyar ta rashin hankali?”.
Hannu Nu’aymah tasa da sauri ta danne bakinta, da ƙyar ta haɗiye dariyar tata sannan ta kalle su. “Wlhy Umm su Yah Ab ne suka bani dariya”.
Batare da Umm ta tsaya jin ba’asi ba tai tsaki ta koma kitchen. Rabi kam sai ta nufota tana tambayarta wai miya faru?. Da sauri Nu’aymah ta haɗe fuska tare da zuba mata harara tabar wajen. Itama Rabin da harara ta raka Nu’aymahn, a ranta kuwa faɗi take, ‘Zaki gane shayi ruwa ne yarinya, shegiya mai kama da ƴaƴan aljanu’.
Oho Nu’aymah batasan tanai ba. Dan tuni ta shige ɗakinta. Sai dai itama a ranta tana matuƙar mamakin munafunci irin na Rabi. amma sam Umm ta kasa fahimtar akwai wani abu a zuciyar Rabi, dan ita ta jima da fahimtar hakan, harma a ranta tana zargi Rabin da ɗaukar sirrin Umm tana fitarwa. Dan akwai ranar data taɓa ganinta bayan ɗakinsu tare da wanda bata fahimci namiji ne ko mace ba suna magana. Sai dai kafin ta zagaya taga wanene ta iske sunbar wajen Rabin ma harta shigo ciki. Tun daga lokacin ta saka mata kahon zuƙa. Taso fahimtar da Umm amma saita hauta da faɗa akan batason wannan halin banzar, dan Rabi a haife ta haifi Nu’aymah harma wanda ya fita. Kuma tun Nu’aymah na ƙarama suke tare ita bata taɓa ganin wani abu mara ƙyau daga gareta ba.
Tsaki tayi kawai da kauda zancen Rabi a ranta ta koma tuno su Abdallah. Haka kawai takejin al’amarin nasu na sakata nishaɗi. Ba sai an faɗa ba kowa yasan tana tsananin son Abdallah, ƙaddara ce kawai ta shiga tsakanin al’amarinsu. Amma a yau sai kawai yanda Naser yay sai shima ya birgeta. Har takeji zata iya aurensa duk da zuciyarta bawai tana sonsa bane ba. Amma tunda ta haƙura da Yah Ab zata iya maye gurbinsa da Naser ɗin. Sai dai fa tasan lallai akwai ƙura a cikin faruwar hakan kuma.
★★★
A ɓangaren su Abdallah kuwa faɗa sosai su Baba malam sukai musu akan abinda suka aikata. Dan a gabansu mafi yawan rigimar ta faru shiyyasa basu bi takan jin yanda akai ba. Sai da baba malam ya tabbatar jikinsu yayi sanyi sannan ya ɗora musu da nasiha kuma, ya kuma sakasu bama juna haƙuri sannan suka sallamesu.
Suna fitowa kowanne ya wurgama ɗan uwansa harara da jan tsaki.............✍
Kuyi manage Please, inada baƙi????????????.
ZAFAFA BIYAR 2021
Hafsat miss xoxo????
KIBIYAR AJALI……!
(Sulke baya tareta saita gitta).????????
Mamu gee????
MIN ƘALB!!????????
Hafsat rano????
ABINDA KE CIKIN ZUCIYA…!!????????
Safiyya huguma???? SIRAƊIN RAYUWA????????
Bilyn Abdull????
SARAN ƁOYE????????
Duka akan farashi mai rahusar gaske.
Kamar haka????????????????
Ɗaya___300
Biyu____400
Uku_____450
Huɗu____500
Biyar_____700
Zaku biya kudinku acikin wannan asusun namu na banki????????
ACCOUNT NO 0812652655
ACCOUNT NAME- HAFSAT LAWAN GAMBO
BANK NAME: ACCESS BANK.
saiku turawa wannnan numban shedan biyanku(evidence of payment)????????
0903 234 5899
IDAN KUMA KATIN WAYANE KO VTU/TRANSFER ZAKU TURA TA WANNAN NUMBER TAREDA SHEDARKU????????
09033181070
????????????????????????????????????????
TEAM—-ZAFAFA BIYAR????????????????
ALLAH ka gafartama iyayenmu????????????.
[5/22, 10:26 PM] +234 809 502 2953: LITTAFIN nan na kuɗi ne. Dan girman ALLAH ki daure ki biya kafin ki karanta, idan kuma bazaki iya biya ba ki haƙura domin ALLAH karki karanta. Idan kuma kin saya dan girman ALLAH karki yaɗa mana????????.
No. 34
…………Abu kamar wasa sai ga ƙaramar magana na neman zama babba. Dan kuwa dai rikici sosai ke wakana a tsakanin Abdallah da Naser akan Nu’aymah. Amma sai suka canja taku yanda iyayensu bazasu fahimta ba. A duk sanda Naseer yasa aka kira masa Nu’aymah sai Abdallah yazo ya tsare. Hakama duk lokacin da Abdallah ya buƙaci ganawa da Nu’aymah sai Naser yazo ya hana hakan ta hanyar zama tsakaninsu kamar yanda Abdallahn keyi.
Hajjo da mafi yawan rigimar a sashenta akeyi tana kallonsu amma tai kunnen uwar shegu da su kamar bata ganiba. Wani lokacinma da biyu take sakawa a nemo mata Nu’aymah ta zauna a sashenta dan tasan nanne wajen zaman su Naser ɗin musamman da daddare.
Duk kuma wannan abun dake faruwa Adawiya bata nan, dan kwanansu biyu da zuwa sukai tafiya biki ita dasu Hajarah dangin kakarsu maman su Addah. Da Addah ta ƙarrafa ayi tafiyar da Nu’aymah ma. Sai dai yanayin jikinta yasa Hajjo hanawa. Shiyyasa suka tafi su uku harda Kubrah sai Addahn da sauran ƴaƴanta na ma’auri.
Da farko rikicin nasu Naser nishaɗi yake saka Nu'aymah, amma ganin al'amarin na sake ɗaukar zafi sai hankalinta ya fara tashi. Dan neman birkita mata tunani sukeyi har takan rasa wanene yafi cancanta ta mallakama kan nata?.
Al'amarin bai sake tada hankalin kowaba a gidan sai randa Hajjo take cema Abdallah dama ya haƙura ya barma Naser Nu'aymah. Tunda shi a yanzu gashi yana auren su Yusrah. A fusace yace, “Indai su Yusrah ne zasu masa katanga da mallakar Nu'aymah to lallai zai rusa katangar”.
Babu wanda ya ɗauki furucin nasa da muhimmanci a lokacin da yayisa. Sai dai ga mamakinsu bayan sallar isha'i sai gashi da zungureriyar takarda har guda biyu yazo ya dire gaban hajjo.
Kallonsa tayi fuska a yatsine. “Kai wannan takardun kuma na miye ka ajiyemin kamar wani ɗan saƙon kotu?”. Fuska a turɓune yace, “Hajjo sakamakon katangar da kika tabbatar min zata shiga tsakanina da Nu'aymah ne a ciki. Kinga yanzu sai ki daina min baki ko”.
Sam hajjo bata fahimci zancen nasa ba, amma sai ta saka Omar dake zaune tare da ita ya duba mata. Ɗaukar ɗaya yay yana murmushin diramar kakar tasu da yayansu. Da sauri ya fesar da ruwan da ya ke sha yana faɗin, “What!?” saboda abinda yaci karo da shi a rubuce.
A rikice hajjo tace, “Miya faru Umaru?”. Jikin Omar na ɓari ya ajiye kofin ruwan tare da ɗaukar ɗayarma ya buɗe. Nanma dai abinda ke cikin ta farkon ce a ta biyu, ai baima san lokacin daya furta, “Hajjo wlhy Yah Abdallah ya haukace! ko kuma ya fara shaye-shaye ku bincika!. Hajjo sakin Yusrah da Adawiya fa ya yi.....”
“Saki kuma?!!” Hajjo ta faɗa itama tana miƙewa zumbur.
“Wlhy kuwa Hajjo gashi a rubuce saki ɗai-ɗai”.
“Innalillahi wa'inna ilaihirraji'un. Abdullahi!!. A wlhy gaskiyarka kuwa Umaru Abdullahi ya haukace. Ni Zainabu na shiga uku. Kaga kiramin ɗan malam duk inda yake yazo gida”.
Ɗan jimm Omar yayi alamar tunani, sai kuma ya dubi Hajjo da ranta ke a matuƙar ɓace. Cikin lallashi yace, “Amma Hajjo inaga kamar dai kiyi haƙuri har ya dawo gida. Kinga yanzu bamusan wane uziri yake kan yiba, kiran da za'ai masa zai iya dagula masa tunani, amma idan kince a kirasan dai sai na kirasa ɗin”.
“Hakane Umaru! Kaima kayi maganar hankali, amma lallai sai na saɓama Abdullahi fiye da zato a gidan nan. Wane irin wawancine wannan? Ashe hankalin da ake ganinsa da shi da girma bashi da shi ɗin?”.
“Kiyi haƙuri Hajjo, ALLAH ya huci zuciyarki. Ni kaina ban taɓa zaton hakan daga garesa ba. Kinga wannan ai tushen ɓata zuminci ne, idan iyayen namu basu kai zuciya nesa ba sai kiga al'amarin ya kawo ɓacin rai. Sannan su kansu yaran an saka wani abu a zuciyarsu gurɓataccen. Dan zasu iya tsanar Nu'aymahr da yace dominta yayi, hakan kuma bashi da amfani”.
Ƙwafa kawai hajjo tayi ranta da zuciyarta na ƙara mata suya da ɗaci. Omar dai yayta lallashinta har sai da yaga ta ɗan kwantar da hankalinta sannan ya fice cike da jimami. Sashensu ya nufa, yaje ya faɗama Momy duk abinda ya faru.
Sosai itama ta rikice hankalinta ya tashi. Dan ta tabbata Abbansu dama wasu a mutanen gidan bazata fita da ga zarginsu ba, musamman ma da akasan taso ya auri ɗiyar ƙanwarta. Waya ta ɗauka ta shiga neman Abdallah. Sai dai harta tsinke bai ɗagaba. Bata gajiya ba wajen cigaba da jera masa kira, amma yaƙi ya ɗaga.
Hajjo, Omar, Momy sun yi yinin yau ne cikin tashin hankali da damuwar ɓarnar da Abdallah ya tafka. Duk da sun ƙagara Baba malam ya dawo gidan ransu cike yake da fargabar sakamakon da zai biyo baya kuma.
Sai bayan sallar la'asar baba malam da Abban Abdallah suka dawo gidan. Dan dama tare suka fita. Sunje wani ƙauyene akan maganar wata katafariyar gona da zasu saya. Sunason gyarata su maidata gidan gona a zuba dabbobi kala-kala na kiwo a ciki. Wannan ma ne dalilin da yasa har yanzu shi da Abba Musbahu basu koma ba. Suna son sai komai ya kammala sannan su ɗauka iyalansu su koma inda suka fito sai kuma biki.
Kamar yanda al'adarsu take ta fara shiga sashen mahaifiyarsu yau ma hakan suna fitowa daga mota can suka nufa. Yanda suke tafe suna firarsu kowanne fuska ɗauke da fara'a dolene su matuƙar burgeka. Dan a kallo ɗaya zaka fahimci ɗunbin shaƙuwa da ƙaunar juna dake a tsakaninsu.
Sai da sukai sallama Hajjo da ke zaune cikin ɓacin rai har yanzu ta amsa musu da basu izinin sannan suka shiga. Kallo ɗaya sukai mata suka fahimci tana cikin damuwa. Kusan da sassarfa duk suka ƙarasa gareta kowanne na tambayarta tana lafiya?.
Batai magana ba, sai wajen zama data nuna musu. Sai dai maimakon su zauna a kujerun sai suka zauna ƙasa tamkar yanda suka saba. Gaisheta sukayi, sannan suka sake jero mata tambayoyi akan yanayin nata.
Ƙwallar da suka cika mata idanu tasa bakin ɗan kwalinta ta share. Hakan sai ya sake tada musu hankali.
“Inna dan ALLAH ki faɗa mana minene ke damunki? Mune mukai muki laifi? Ko matan mu? Kokuwa a cikin yaran nan ne wani yay miki wani abu?”.
Sake share hawayen data matso tayi da cewar, “Ni babu abinda kukai min ɗan malam, Abdullahi ne kawai keson watsa mana gida”.
Hankali a tashe baba malam da Abban su Abdallah suka kalli juna. Cikin ƙarfin hali baba malam yace, “Innah mi Abdallahn ya aikata?”.
Takardun da Abdallah ya rubuta ta ɗakko ta miƙa musu. Amsa sukayi kowanne ya buɗe guda ɗaya gabansa na faɗuwa. A tare suka ɗago a razane suka kalli juna da ambaton sunan ALLAH. Baba malam har yana tsallaken kalma wajen faɗin, “Innah shi Abdallah ɗinne ya rubuta wannan takardar?”.
“Shine ɗan malam, shine da kansa ya rubutasu ya kuma kawo mani. Wai dan kawai jiya na bashi shawarar cewar yay haƙuri ya barma Nasiru Zainabu tunda shi yanzu yana da matansa har biyu. Shine fa yau ya kawomin takardar sakinsu Adawiya wai gashinan ya rushe katangar dana ce masa tana tsakaninsa da Zainabu”.
Abba da ya gaza cewa komai tun ɗazun yace, “Innalillahi..., wai inna kina nufin su duka biyun ya saka?”.
“Eh mana Lurwanu, baga takardun nan ba duka biyu na baku”.
Da sauri baba malam ya amshi ta hannun Abba, shima ya karɓa ta hannunsa. Da gaske kuwa su duka biyun ya saki. A take tsananin ɓacin rai ya sake bayyana a kan fuskokinsu. Abba ya miƙe a fusace zai fice. Kiransa baba malam ya shigayi amma ina zuciyar gadon ta motsa. Dan haƙuri kawai ya bashi batare da ya juyoba ya fice.
Momy na zaune cikin damuwa da fargabar jiran dawowar mijinta Abba ya shiga. Jiki a sanyaye ta dubesa dan ko sallama baiyi ba
Takardun guda biyu ya watsa mata a jiki. “Da saninki ɗanki yay wannan aika-aikar ko?”.
Gaban Momy na faɗuwa ta ɗauki takardun ta karanta, hawayen da taketa faman dannewa tun ɗazun suka zubo mata a saman kumatu. “Wlhy Abban Abdallah ban sani ba. Nima ina zaune Omar yazo yake sanarmin. na kirashi yafi sau hamsin amma ya ƙi ɗagamin waya ma, kai........”
Baki ya buɗe zai daka mata tsawa Omar da ya shigo basu sani ba yace, “Abba wlhy babu ruwan Momy, hasalima batasan komaiba akan al'amarin nan sai da nazo na sanar mata. Abba ko kasan dama tunda Yah Abdallah ya dawo gidannan baiyi zaman minti biyar da Momy ba. Da ya shigo ya gaidata da safe bazata sake ganinsa ba sai washe gari. Fushi yake da ita babu gaira babu dalili. Ta sakani na tambayesa amma yacemin idan na sake zuwa masa da zancen Momy sai ya ɓatamin rai. Ita kanta nace zan sanar maka abinda ke faruwa amma ta hanani, wai mu bashi lokaci kozata fahimci abinda ke damunsa”.
Jikin Abba ne yay sanyi, dan tabbas kuwa ya kula tunda Abdallah ya dawo ƙasar nan bai taɓa ganinsa zaune da Momy ba, da farko yaso tambayarta sai kuma yayi tunanin ƙila sai ya fita suke zaman. Wannan ya sakashi yin shiru duk da kuwa yasan yanda matar tashi take da ƙulafucin ƴaƴa musamman Abdallah.
Nannauyan numfashi ya sauke tare da zama yana cire hular kansa ya ajiya.....
A ɓangaren baba malam kuwa Abba na fita waya ya zaro ya shiga neman layin Abdallah. Sai dai kuma abin mamaki switch off. Ajiye wayar yayi ya maida hankali ga Hajjo da ke sharar hawaye har yanzun. Kwantar mata da hankali ya shigayi da bata haƙuri. Yace, “Inna ki kwantar da hankalinki dan ALLAH, insha ALLAHU mu dai wannan bazai kawo mana rabuwar kawuna ba. Duk inda Abdallah ya shiga kuma na tabbata zuwa dare dole ne ya dawo gida ya kwana ai, insha ALLAHU a daren nan sai ya maidasu su duka biyun”.
“Ɗan malam bazaka gane abinda nake nufi ba, amma duk yanda kake tunanin sauƙi a al'amarin nan da wahala ya kasance hakan. akwai abinda na sani wanda kai da sauran ƴan uwanka baku san da shi ba a gidan nan. Ina barin masu aikatawar ne kawai kafin ranar da zan masu bankaɗa da tonon silili a gaban kowa. Ni dai abinda zan sanar maka yanzu shine da ga Abdullahi har Nasiru ka zaunar da Zainabu ta zaɓi wanda tafi so tunda abin ya zama haka. Kokuma ta auri wani bare can a zauna lafiya. Sannan inason ka nutsu kayi tsai da hankalinka a wannan karon game da kowa a gidannan, koda baka fahimci duka abinda na fahimtaba zaka fahimci wasu daga ciki. Dan kai ne uba a gidan nan, duk da dama nauyi da girman ya rataya a wuyankane tunbayan rasuwar mahaifinku, ina kuma alfahari da yanda ka riƙe hakan, amma sai randa ƙasa ta rufe idanuna zaka sake tabbatar da girman dake bisa kanka da tarin fituntunun da ke kwance a cikin gidannan wanda ALLAH ne kawai hanasu fallasuwa saboda rahamarsa da ikonsa da kuma ƙarfin addu'ar mahaifinku da har yanzu take biye da ku. Kai dai ALLAH ya ƙara maka haƙuri da juriya kawai. Tashi kaje ka huta, ka kumayi ƙoƙarin tausar sauran ƴan uwanka akan duk ma abinda zai iya biyo baya game da wannan gagarumar fitinar da Abdullahi ya ɗaɗɗago mana”.
Kasa cewa komai baba malam yayi. Cike da ruɗanin maganganun Hajjo ya jinjina mata kansa kawai da miƙewa ya fice zuwa nasa sashen. Bai iske kowa a falon ba sai Muhammad dake karatun Al-Qur'ani na haddar da aka basu a islamiyya. Yaron bai dakata daga karatun da yakeyi ba, shima kuma bai masa magana ba ya wuce ɗakinsa.
Komai tsaf a gyare kamar yanda ya saba zuwa ya iske, ga ƙamshi mai daɗi. A ɗaya daga kujerun ya zube hankalinsa har yanzu baya tare da shi. Dan ransa da zuciyarsa cike suke da tarin ruɗanin kalaman mahaifiyar tasu. Shi kansa yasan akwai abubuwan dake kwance a gidan nan ƙwarai da gaske. Waɗanda da yawansu shi da iyalinsa sun cutu matuƙa a cikinsu. Koma yace suna kan cutuwa. Ya kumayi imani da ALLAH babu wani baƙon ido daga waje da zasuce yana aikata su, dolene mai aikatawar a cikin zuri'arsu yake. Yasha yin tunanin tsananta bincike, amma sai zuciyarsa ta gargaɗe sa da yin haƙuri, sannan yana mai tsananin jin tsoron wanda sakamakon ɓarnar zata tabbata a garesa. A ganinsa gara kawai a cigaba da tafiya a lulluɓen dan UBANGIJI mai ji ne kuma mai ganine akan kowa da komai..........
Taɓa shin da akayi ne ya saka tunaninsa katsewa. Duban Umm da tun ɗazun take masa magana yay. Fuskarta cike da damuwa tace, “Malam lafiya kuwa? Wane irin zurfafa tunanine haka? lna fatan dai lafiya ko?”.
“Humm! Jannat lafiyar nan da dauƙi”.
Saurin zama tayi hannunta riƙe da kofin data zuba masa ruwa tana faɗin, “Miya faru?”.
Ruwan ya fara karɓa ya sha, ta sake ƙara masa ya shanye sannan ya ajiye kofin ya labarta mata duk abinda ya faru, harma da zancen da Hajjo tai masa.
Duk da itama ta jima da ji a ranta duk abinda Hajjo ke zargi a kwaishi a gidan hakan bai hanata jin tashin hankali ba. Ita kanta tanason sanin mai aikata musu SARAN ƁOYE a lokuta da dama. Sai dai tsoron wanda zata gani yana aikatawar ke sakata sama ranta haƙuri da barin komai hannun UBANGIJI.
★★★★
A yau dai har dare Abdallah bai dawo gidanba duk jiran da su baba malam sukai zaman yi masa. Dole suka haƙura suka kwanta al'amarin nacin ransu da zuciya.
Washe gari bayan fitowa sallar asuba baba malam da sauran ƴan uwansa suka hallara gaba ɗaya a sashen mahaifiyarsu. Bayan sun gaisheta suka sake haɗuwa gaba ɗaya wajen bata haƙuri akan abinda Abdallah yayi, suka kuma tabbatar mata insha ALLAH zasu dai-daita komai ba sai yayi tsamari ba.
Batace da su komaiba dai, sai dai ta musu addu'ar nasara da nemawa Abdallah dama sauran yaran shiriya gaba ɗaya.
A wannan yinin maganar sakin ta shiga kunnen kowa dake a gidan ciki harda Addah da yaranta dake can suna shan biki. Aiko ba ƙaramin rikita musu lissafi Adawiya tayi ba. Dole babu shiri suka tattaro suka nufo kano zuciyar kowa babu daɗi.
Tunda saƙon saki ya isa kunnen Yusrah kuwa sai wani tarin farin ciki ya kamata. Bama tasan lokacin data shiga dirga tsalle akan gadon ɗakinsu ba. Kafin ta sakko da sauri ta shiga bayi ta ɗauro alwala. Salla tayi raka'a biyu na godiya ga ALLAH daya kawo ƙarewar wannan aure da ko tarewa batayi ba a cikinsa. Dama tunda su Adawiya suka diro ƙasar bata da wani sukuni. Shiyyasa ta koma yinin makarantar Tahfiz ɗin gidansu dan kawai ta gujema ganinsa. Hakan kuwa akayi, dan tunda suka iso sau biyu ta haɗu da shi. Ɗaya da daddare ya shigo sashensu wajen Abba. Na biyu kuma a sashen hajjo taje kai mata abinci. Duka a haɗuwar tasu gaisuwa ce kawai ta shiga tsakaninsu. Yanda baya sakar mata fuska itama bata shiga sabgarsa sam, dan baya wani nuna alamar akwai ko ɗigon haƙƙinta daya rataya a kansa ma. Hakan kuma bai dameta ba, to gashi cikin amincin ALLAH komai ya zama yanda taketa fata a kullum. Ba ƙaramin azumi da ƙiyamullaili tayi ba akan auren nan a cikin watannin nan. Dan ita kaɗai tasan dalilin rashin son auren.
Duk wannan ruguɗai da akeyi Nu'aymah batasan anai ba ita kam, dan Umm da baba malam babu wanda ya sanar mata. Sashen Hajjo kuma yanzu ba wani shigarsa takeba sosai saboda takurawar Nasir da Abdallah da suka maida sashen hajjo wajen zamansu. Ta gwammaci taita zama a sashensu, idan Muhammad na gidan susha shirmensu, idan kuma ya fita makaranta tayi kallo idan akwai wuta ko su zauna hira da Umm. Wani lokacin kuma tai barcinta dan Doctor ya ce ta dinga yawan barci, shiyyasa ma ya saka mata maganin barci a magungunanta.
Yauma tana a ɗaki tasha barcin rana har su Adawiya suka dawo bata saniba. Ta fito wanka tai sallar la'asar, shiri ta farayi da ƙudirin zuwa islamiyya yau dan tanajinta Alhmdllh. Tana tsaka da saka kaya ta jiyo kururuwar kuka kamar muryar Adawiya kuma. Saurin ƙarasa saka kayan tayi ta fito, a mamakinta duk ma sai ta iske ƴan gidan a tsakar gida kowa ya fito an rufu kan Adawiya. Gabantane ya faɗi da tunanin ko Accident sukayi a hanya. Da sauri ta shiga bin kowa da kallo sai taga kowa ma yana nan, harsu Aunty Aysha ma basu wuce gidajensu ba nan sukayo.
Kallon Jafar dake kusa da ita tayi tace, “Jafar miya faru wai?”.
“Aunty Nu'aymah ban saniba nima. Kawai dai naga Aunty Adawiya na kuka tana cewa wai indai aka rabata da Yah Ab zata mutu”.
Kafesa da kallo Nu'aymah tai tana son fassara kalaman nasa amma sunƙi fassaruwa. Dubanta ta kai ga Umm dake lallaɓa Adawiya taje sashensu amma taƙi, hakan ya sake tabbatar mata da lallai ba lafiya ba kuwa. Baba malam daya shigo gidan yanzunne ya dakama Adawiya tsawa. Jiki na rawa ta miƙe tsaye.
“Wane irin rashin hankaline wannan tun daga wajen gate anajin muryarki, tona mana asiri zakiyi da shirme ko mi?. To wlhy bara kuji bama ita ba duk wanda na sakejin bakinsa a wannan maganar saina ɓata masa rai, naga dai Abdallahn a ƙarƙashin ikonmu yake shima, dolene kuma yabi abinda mukeso inhar yana buƙatar gamawa da rayuwarsa lafiya. Kowa ya shige ciki”.
Jan ƙafa kowa ya shigayi zuwa sashensa. Kubrah ta kama hannun Adawiya suka shige tare. Inda suka bar Addah da bata fitaba nan suka isketa zaune. Babu wanda taima magana a cikinsu har suka zazzauna kowa na ƙannun magana. Batace musu komaiba dai har lokacin, saima jingina da tai da kujera ta lumshe idanu.
Nu'aymah suna shiga sashensu ta shiga tambayar Umm abinda ke faruwa. Dan ita harga ALLAH bata fahimci komaiba dai har yanzun. A taƙaice Umm ta faɗa mata, sai ko ta zabura a matuƙar razane. “Ya salam. Umm Yah Ab kuwa yana da hankali?! Wannan ai gogama mutane sharri ne da zai ce saboda ni ya aikata saki ga matansa”.
“Wannan sakaki a cikin da yayi shine ya sake tada mana hankali muma Nu'aymah. Dan zai iya zama wata fitina daban wadda ba'asan iyakar inda zata tsaya ba a gidan nan. Yanzu dai Abbanku ya gano inda yake, ya kuma bashi daga nan zuwa kwana uku idan bai dawo gida ba zai haɗu da ɓacin rai mai tsanani daga garesu”.
“Ai gara yazo ya kwance wannan ƙullin da yay min nikam, a dalilin mi zai sakani tsakkiya, a barni da abinda ya damenima nikam ya isheni Umm”. Tai maganar tana fashewa da kuka.
Tausayinta ne ya kama Umm sosai, ta ruƙo hannunta ta sakata jikinta tana lallashi............✍
???? Yah Ab ya zaka mana haka ne?????????♀️????????♀️
ZAFAFA BIYAR 2021
Hafsat miss xoxo????
KIBIYAR AJALI……!
(Sulke baya tareta saita gitta).????????
Mamu gee????
MIN ƘALB!!????????
Hafsat rano????
ABINDA KE CIKIN ZUCIYA…!!????????
Safiyya huguma???? SIRAƊIN RAYUWA????????
Bilyn Abdull????
SARAN ƁOYE????????
Duka akan farashi mai rahusar gaske.
Kamar haka????????????????
Ɗaya___300
Biyu____400
Uku_____450
Huɗu____500
Biyar_____700
Zaku biya kudinku acikin wannan asusun namu na banki????????
ACCOUNT NO 0812652655
ACCOUNT NAME- HAFSAT LAWAN GAMBO
BANK NAME: ACCESS BANK.
saiku turawa wannnan numban shedan biyanku(evidence of payment)????????
0903 234 5899
IDAN KUMA KATIN WAYANE KO VTU/TRANSFER ZAKU TURA TA WANNAN NUMBER TAREDA SHEDARKU????????
09033181070
????????????????????????????????????????
TEAM—-ZAFAFA BIYAR????????????????
ALLAH ka gafartama iyayenmu????????????.
[5/24, 12:25 PM] +234 806 269 3623: LITTAFIN nan na kuɗi ne. Dan girman ALLAH ki daure ki biya kafin ki karanta, idan kuma bazaki iya biya ba ki haƙura domin ALLAH karki karanta. Idan kuma kin saya dan girman ALLAH karki yaɗa mana????????.
Ina fatan ansha weekend lafiya? ☺️????????????
No. 35
………….Kamar da wasa sai ga Abdallah ya shanye kwanaki ukun da baba malam ya bashi babu shi babu mai kama da shi. Ran baba malam da sauran ƴan uwansa ya sake ɓaci matuƙa, amma duk sunta ƙoƙarin dannewa. Dan hatta Hajjo ranta a ƙololuwar ɓace yake.
Hankalin Nu’aymah ne ya sake ta shi. Dan koba komai har yanzu tana son Yah Ab, bazata so bari ya cigaba da munana a idon iyayensu ba akan shima son da yake mata. Tunda duk abinda yake aikatawa na laifi a garesu a kanta ne.
Kuka sosai Nu’aymah tasha akan wannan al’amari. Musamman ma da itama tai kiransa da wayar Umm amma yaƙi ya ɗaga tun a ranar.
Yau ma wayar ta sake ɗakkowa ta Umm ta kirasa, sai dai bai ɗaga ɗin ba. Haƙura tayi da kiran, sai dai kuma bayan kamar awa guda kamar an tsikareta ta sake zuwa ta aro wayar again. Test massege ta tura masa, bakinta cike da addu’ar ALLAH yasa ya duba.
Bayan kamar mintuna biyar kuwa sai ga reply ɗinsa. Jikinta har rawa yake wajen ɗauka ta duba.