SARAN BOYE COMPLETE

Tun daga bakin ƙofar sashesa take ƙarema gidan kallo, babu ƙarya gidan ya haɗu, musamman idan kana sama kake kallon tsarin falon ƙasa. Hakama idan kana a ƙasa kake kallon upstairs ɗin. Ga koma tsaf babu wani datti alamar dai ana kula da tsaftar gidan yanda ya kamata. A yanzu haka ma'aikatan gidan daketa shara da goge-gogen yamma sai risinawa suke suna gaishesu. Shi kaɗai yake amsawa. Ita kam binsu kawai take da kallo da takaicin ganinsu ƙattan maza.
Ta saman upstairs ɗin suka nufi sashen Momy dake jikin na papa. Corridor ne mai ɗan faɗi da ƙofofi uku a cikinsa. saɓanin Nasu da zaka iske falo. Knocking ɗin ƙofar tsakkiya yayi. Daga ciki wata murya ta amsa. Juyowa yay ya ɗan kalleta sannan ya tura ƙofar. Ita dai biye take da shi. Yanda taji yace, “Excuse me” itama Excuse me ɗin tace a hankali.
Murmushi madam Chioma dake waya da ƙawarta tana bata wasu dabaru ta saki saboda ganin rabin ranta. A yau ɗin nan duk da zafin zazzaɓin nan da takeji sai taji a ranta garama da take yinsa. Dan koba komai a dalilin zazzaɓin ta samu kusanci da lokacin yaronta mai tsaho tare da ita. A gaba ɗaya yinin yau sai zirga-zirga ya keyi a kanta da son ganin jikinta ya dai-daita. Ɗazuma da taita langare masa yafi awa biyu zaune tare da ita.
A hankali kuma sai fara'ar fuskar tata ta fara gushewa saboda ganin abinda ke a bayansa.......
“Masha ALLAH Mom sauƙi yazo sosai” ya faɗa yana zama a gefen gadon nesa da ita kaɗan batare da ya lura da canjawar fuskar tata ba. Nu'aymah kam dake mata kallon ƙasan ido taga komai da madam Chioma tayi, murmushin farko da canja fuskarta da tai saboda ganinta. Dai-dai Aymah na zama bisa sofa ɗin ɗakinne Momy ke bama Yoohan amsar maganarsa. “Ƙarfin haline kawai my boy, dan dana tashi ma kamar zan kiraka kazo ka sake dubani sai nayi tunanin ko baka a gidan ne?”.
Ɗan murmushi kawai yayi batare da yace komai ba, saboda gaisheta da Nu'aymah keyi. Shiru tayi kamar bazata amsaba, ita kuma Aymah daga gaisuwar nan guda ɗaya bata sake wata ba.
“Mom tana gaisheki fa”. Ya faɗa yana kallonta. Daburcewa ta nema yi, dan batai zaton zai saka baki ba. Cikin kame-kame tace, “Oh Daughter Am sorry, hankalina nakan Son, kina lafiya?”. Cike da mamakinta Aymah tace, “Alhmdllh” daga haka taja bakinta tai tsit fuska babu walwala. Itama Madam Chioma bata sake bi takan Nu'aymah ba. Gaba ɗaya hankalinta naga Yoohan. Sai takalarsa da zance take yaƙi magana ƙwaƙwƙwara, daga guntun murmushi sai um sai a'a. Ita Aymah ma abin dariya yaso bata. A ranta sai gulmar ɗan da uwar takeyi tana kwasar dariya. A fili kuwa fuskarta babu ko ɗigon walwala a cikinta. Ta tsume abinta kamar tama manta da su a ɗakin.
Sosai Yoohan yake lure da ita, amma idan ba shiba bazaka taɓa fahimtar hankalinsa na gareta ba. Agogon hannunsa ya kalla yana faɗin, “Momy bara muje ta gaida Papa nasan ya shigo yanzun”.
“A to muje sai na rakaku ai” ta faɗa tana miƙewa. Da sauri Yoohan yace, “Haba Momy, keda ke fama da kanki”. “Karka damu ai da sauƙi” ta faɗa tana bin bayan Aymah da tunda ya ambaci tafiyar har ta kai ƙofa. Bayansu kawai yabi yana mamakin halin Momynsa.
Koda suka fito Aymah tsayawa tai baya suka wuce gaba tunda sune ƴan gida. Sun shiga sashen papa dake da falo babba, dan har yafi nasu girma ma. bata cuci kanta ba, koda suka zauna sai da ta ƙarema kowace kusurwa ta falon kallo lokacin Momy ta shige bedroom ɗin papa dan basu sami kowa a falon ba. Yoohan kuma yanata latsa waya.
Lokacin da suka shigo shima papan ta ƙasan ido ta gama ƙare masa kallo tsaf. Shima ƙyaƙyƙyawa ne kuma fari, dan suna kama da Yoohan, sai dai Yoohan ya fisa ƙyau da ƙwarjini da ƙuruciya. Da alama dai Yoohan ɗin ya kwaso kamannin wanu bayan shi. Papa na zama Aymah ta zamo ƙasa ta zauna. Ba Yoohan ba har Madam Chioma hakan da Nu'aymah tayi ya bata mamaki. A ranta kuwa ayyanawa take, ‘Wato ni wannan ƴar shilar yarinyar ta raina kenan?, ina zaune sama tana zaune itama a ɗakina’.
Maganar papa ce ta katse madam Chioma. Cikin fara'a sosai yake amsa gaisuwar da Aymah ke masa, harda haɗawa da ƴar tsokanarta. Itako tanata zuba murmushi kanta a ƙasa. Tambayoyi ya rinƙa mata dake nuna kulawarsa a gareta. Hakan ne ya sakata ɗan sakin jiki da shi tana bashi amsar da duk ya buƙata.
Shi dai Yoohan ma abin sai ya bashi mamaki, dan koshi bata sakin jiki da shi kamar hakan. Papa daketa murmushin jin daɗin yanda Aymah ta saki jikinta da shi ya dubi Momy yana faɗin, “Darling a tattaro min duk members na gidan nan da masu aiki, zan gabatar musu da daughter in-low ɗina. Itama na gabatar mata da su.
Cikin ɗan yatsine fuska madam Chioma ta miƙa hannu ga wayar landline dake a table ɗin jikin kujerar da suke zaune ita da papan ta hau danne-danne. Kira tayi, bayan an ɗauka daga can tace, “Joy, ki sanarma kowa na gidan nan yazo Master parlor yanzun nan”.
“Okay maa!”
Joy ta amsa daga can tana ajiye wayar.
Cikin mintuna ƙalilan kowa ya shigo falon, hatta da maigadi bai zaunaba, kulle gate ɗin yayi ya taho. Shi dai Yoohan kamarma baya cikin falon. Babu wanda ya damu da shariyar tasa tunda sunsan halinsa kenan. Victoria ce ma uwar surutu taje jikinsa zata zauna ya harareta. Da sauri ta canja mazauni tana tura baki gaba na shagwaɓa.
Sai da kowa ya nutsu sannan papa ya fara magana. “Na taraku anan ne domin na sake tabbatar muku da ƙaruwar member da family ɗinmu ya samu duk da nasan kun sani. Karku ganta ƴar ƙarama kuce zaku ɗauketa ƙasa da ku, har wani raini ko abu mara ƙyau ya faru a tsakaninku. Duk wanda ya aikata hakan zan saɓa masa da saɓawa mafi ciwo. Dolene kowa na gidannan idan ka cire su mama da Darling dake matsayin kakanni a gareta da Uwa kowa ya bata girmanta. Saboda mata ce ita a wajen John, kowa kuma yasan a gidan nan bayan ni John shine uba, dan shine babban ɗana abin alfaharina. Sunanta Zainab, amma ana kiranta Ayimah. My daughter ko ba haka bane?” ya ƙare maganar yana kallonta. Murmushi Aymah tayi, batare data ɗagoba ta gyara masa da cewar, “Nu'aymah”.
Sake maimaitawa yayi duk da dai yanzunma bai faɗa dai-dai ba. “Nasan dai baku manta da sharaɗin John ba. Zainab ɗago kanki zan nuna miki kowa da sunansa anan kema”.
Babu musu kuwa ta ɗago, dan ganinsu cike da falon baisa taji ko ɗarba a ranta saboda tun fil azal ita ALLAH yayita mutum mara tsoro. “Wannan itace mamana sunanta Mama debora. Itace ta haifeni tare da ƙannena. Maza mu uku, mata su biyu. Gasu nan” ya nuna ƙannensa biyu mata dake zaune a wajen. Maman Favour, da maman Destiny. “Akwai maza biyu suma zan nuna miki su idan sunzo. Sai wannan itace Maman Darling. Momyn John kenan gata nan” ya nuna madam Chioma da mamanta. Daga haka ya dawo kansu Joy, Gebrail, Abraham, Victoria ƙannen Yoohan kenan. Sai Miracle ɗiyan ɗan uwansa Uncle Mike. Sai Aunty Blessing kuku, daga haka ya koma kansu Solomon daki-daki da ayyukansu a gidan duk ya sanar mata har zuwa kan maigadi.
Cikin murmushi tace, “Nayi murnar haɗuwa da ku duka”.
A tare suma duk suka amsa mata da hakan, duk da dai da yawansu ba har cikin zuciya bane ba. Sun faɗane kawai saboda tsoron Yoohan da duk abinda sukeyi yayi kamar baya falon.
Sallamar ma'aikatan gidan ya farayi, kafin ya sake duban family nasa ya shiga musu nasihar zaman lafiya (Su papa kenan????lol). Daga haka ya sallami su Miracle ma daketa antayama Aymah harara ta ƙasan ido ita da joy. ya rage daga shi sai su mama debora da su maman Destiny. A gabansu ya fiddo keys ɗin mota guda biyu ya miƙama Nu'aymah ɗaya.
“Dota wannan shine wedding gift ɗinki daga ni. Kai ma John ga naka. ALLAH ya sanya muku albarka a cikin aurenku”. Da hannu biyu Aymah ta amsa bayan taje gabansa ta durƙusa. Tai masa godiya sosai. A ranta kuma tana addu'ar ALLAH ya shiryesa idan yana da rabo, idan baida kuma ALLAH yay maganinsa. Shima oga Yoohan ya amshi nasa. Tare da rungume papansa yana mai nuna masa jin daɗinsa da waɗannan ƙyaututtuka shi da matarsa. Buɗe masa hannaye madam Chioma tayi wai itama ya bata hug.... Kafaɗa ya maƙale mata yana faɗin, “Sai kin bamu naki gift ɗin sannan”.
Kusan a tare duk falon akai dariya. Banda Aymah da sam abin ita bai birgeta ba. Dan haka kawai madam Chioma duk da mahaifiyar mijin nata ce batai mataba ko kaɗan. Su mama debora ma duk sun bama Yoohan ƙyauta, amma basu bama Aymah ba. Ko a jikinta ita kam, dama bata buƙata. Ganinma lokacin salla yayi saita miƙe tana faɗin ita zataje tai salla lokaci yayi.
Papa ne kawai ya amsa mata. Sai Yoohan da ya bita da kallo saboda ganin yanda tai maganar kanta tsaye babu wani inda-inda a ciki. Harga ALLAH ta birgesa, dan da watace sai tai ta nuku-nuƙu musamman data san su ɗin sun rinjayeta a gidan.
Ko kallon inda yake bataiba tai ficewarta, dan tasan zata gane hanya abinta. Acan downstairs ta hango su Miracle sun baje suna kallo, ta girgiza kai da taɓe baki tana faɗin, ‘ALLAH ka rabamu da gafalalliyar rayuwa dai’.
Sai da ta tsaya a falon ta gamai masa kallon tsaf tana jinjina yanda ya haɗu, da jin ƙaunar iyayenta. Ganin zata makara salla ta nufi hanyar bedroom. Tana buɗe ƙofar zata shiga aka buɗe ta falon. Kallon inda ƙofar take tayi, ganin shine ya sakata ƙarasa shigewa batare data nuna alamar tasan da shigowar tasa ba. A fili ta furta, ‘Ai nazata tuban mazuru kayi, bazaka taso kayi sallan ba’.
Oho, shidai baisan tanayi ba. Dan ɗakinsa shima ya shige kai tsaye dan gabatar da sallar, tunda an ja masa makara bai tafi massallaci ba.
★★★★
“Wai nikam murmushin mi kike tayi hakane Jannat? Tun jiya ina lura dake Murmushin nan ya kasa barin ƙyaƙyƙyawar fuskarnan taki”.
Murmushin Umm ta sake yi tana kallon mijin nata da take ɗunbin so da ƙauna. Sai da ta miƙa masa kofin ruwan data zuba masa kafin tace, “Wlhy idan na tuno Nu'aymah tabar gidan nan sai naji wata irin nutsuwa da kwanciyar hankali. Duk da ina fargabar inda ta tsinci kanta kuma a yanzu. Sai dai inaji a raina bazata bari a cuta mataba acan tunda tasan suɗin su wanene. Amma a gidan nan da bakasan wanene mai SARAN ƁOYE ba tayaya zakai taka tsantsan da al'amarinsa. ALLAH ya ƙarama Hajjo tsahon rai da nisan kwana. Dan nasan ita ɗin babbar garkuwa ce a garemu a gidan nan. Kaga yanzu saimu gani, yarinyarmu ce ba'a buƙata a gidan? Komu kanmu ne?”.
“Gaskiyarki Jannat, koni inajin nutsuwa ta musamman a zuciyata tun bayan ɗaura auren mamana. UBANGIJI shine masani akan wannan auren na Yahya da mamana ya ƙumsa. Dan maybe da ɗaya daga cikin su Abdallah ta aura salamar da muke mata fata bazata taɓa samunta ba. Sai ma wasu sabbin fitintunu ne zasu cigaba da bayyana ƙilama har sai mun rasata gaba ɗaya. Amma kinga a yanzu aurenta da yaron nan zan jefa tsuntsu uku ne da dutse ɗaya”.
“Tsuntsu uku kuma Abban Nu'aymah?”.
“Ƙwarai kuwa Jannat. Na farko zan ƙara ƙarfafa gwiwar Yahya akan musulinci, zata taimakesa akan dukkanin ilimin da yake buƙata na sanin musilinci. Na biyu Mamana zatayi ibadar aure, ta kuma samu lafiya da kulawa mai inganci akan lalurarta. Na uku zataimin wani aiki da zuciyata ta kasa daina min kokwanto a kansa. Maimakon inji na ajiye batun, kullum sai sake jin ƙwaɗayin tabbatar da gaskiyarsa nakeyi”.
“Ikon ALLAH, Abban Nu'aymah minene shi kuwa wannan al'amari?”.
“Zan faɗa miki shi Jannat, ki bani lokaci na gama neman zaɓin UBANGIJINA akansa sannan”.
“To UBANGIJI yayi jagora Abban Nu'aymah, ALLAH kuma ya tabbatar da alkairi a cikin al'amarin”.
“Amin ya rabbi Umm-Muhammad. Yanzu yaya batun mai aikin da mamana ta buƙata?”.
“Karka damu za'a nema insha ALLAH, bandama rigima irin tata mizatayi da wata ƴar aiki tunda nasan can gidan bazasu zauna babu ma'aikata ba”.
“Eh duk da haka dai a nema mata. Koba komai zata samu yarenta a cikinsu, ko wani abinne ya dameta ta faɗa mata kafin mu mu sani. Shiyyasama nake ganin ko haƙura zakiyi ki bata Rabi'atu, tunda kinga ta saba da ita sosai, akwai shakuwa tsakaninsu sannan itaɗin ba yarinya bace zata taimakamata da shawarwarin zaman rayuwa”.
“To banƙi ta taka ba Abban Nu'aymah. Sai dai kasanfa ko sanda Nu'aymah na gidan nan ba shan inuwa ɗaya sukeyi da Rabi ba. Inaga ka fara tambayarta idan tanason a bata ita sai taje. Idan bataso sai a aika mata wata ɗin. Dan kasan halin butsutsun yarinyarka ɗin nan ba man kai ne da ita ba sam”.
Dariya baba malam yay tayi da zancen matar tasa. Daga haka suka cigaba da firarsu duk kusan kashi biyu na firar akan Nu'aymah ne. Da kaji kasan cike suke da kewar ɗiyar tasu da begenta. Sai dai dattakonsu ya danne komai suna binta da fatan alkairi a zuci da fatar baki.....
ABUJA
Nu'aymah bata sake ganin Yoohan ba ko wani a jama'ar gidan har washe gari. Dan tunda ta shiga ɗakinta bayan barowa wajen su papa saita kulle harda murza key. Littatafan ta na islamiyya da aka zubo mata cikin kaya ta ɗauka taita dubawa a hankali har lokacin barcinta yayi ta kwanta.
Washe gari tunda tayi sallar asuba bata koma ba. Gyara ɗakinma tayi har toilet, rashin sabo da zaman ya sata sha'awar fitowa falon shima dan ta ɗan gyara ko ta ƙarajin ƙarfin jikinta ta kuma ɗan rage kewa. Tana buɗe ƙofar ɗakin nata shima yana buɗe tasa ƙofar............✍
yanzu haka an kusa kai ƙarhe, gamai buƙata zai iya garzayawa ya biya????????????.
Hafsat miss xoxo????
KIBIYAR AJALI……!
(Sulke baya tareta saita gitta).????????
Mamu gee????
MIN ƘALB!!????????
Hafsat rano????
ABINDA KE CIKIN ZUCIYA…!!????????
Safiyya huguma???? SIRAƊIN RAYUWA????????
Bilyn Abdull????
SARAN ƁOYE????????
Duka akan farashi mai rahusar gaske.
Kamar haka????????????????
Ɗaya___300
Biyu____400
Uku_____450
Huɗu____500
Biyar_____700
Zaku biya kudinku acikin wannan asusun namu na banki????????
ACCOUNT NO 0812652655
ACCOUNT NAME- HAFSAT LAWAN GAMBO
BANK NAME: ACCESS BANK.
saiku turawa wannnan numban shedan biyanku(evidence of payment)????????
0903 234 5899
IDAN KUMA KATIN WAYANE KO VTU/TRANSFER ZAKU TURA TA WANNAN NUMBER TAREDA SHEDARKU????????
09033181070
????????????????????????????????????????
TEAM—-ZAFAFA BIYAR????????????????
LITTAFIN nan na kuɗi ne. Dan girman ALLAH ki daure ki biya kafin ki karanta, idan kuma bazaki iya biya ba ki haƙura domin ALLAH karki karanta. Idan kuma kin saya dan girman ALLAH karki yaɗa mana????????.
NO. 48
I’m on Instagram as yerwaincense_and_more. Install the app to follow my photos and videos. https://www.instagram.com/invites/contact/?i=ayfowzb2ah8k&utm_content=6k8ur6p
YERWA INCENSE AND MORE
(Masarautar K’amshi)
We’ve got you covered with our balsamic scented products.. Yerwa scents last longer and linger.. Ba kauri irin na wa’ensu turaren, Chadian kamshi ne na gaske, Kowane irin samfurin turaren wuta munayi, traditional and modern.
Akwai Khumrah’s kala kala. Kulaccams, Turaren wanka dana wanki dana mopping, Da tsugunno, Jiki da kaya duk muna dasu. Domin mallakar naki tuntub’e ta number shafin dake kasa, Ko kuma Ki duba shafin mu na manhajar Instagram ta: @yerwaincense_and_more.
Kyau, arha, inganci , sai yerwa incense. Muna tura kayanmu ko’ina a fadin nigeria da waje.. Ayi following, Da liking dinmu a Instagram handle dinmu dake sama.
No. 48
…………..Kallo ɗaya tai masa ta kauda kanta. Dan daga shi sai wando gajere fari dako cinyoyinsa bai gama rufewa ba. Sai singlet kalar gwaiduwar ƙwai hannunta mai faɗi fiye dana singlet data sani. Shikam dai kansa tsaye yake ƙare mata kallo cikin kayan barcin wando da riga pink masu taushi. Duk da basu kama mata jiki ba sun mata ƙyau, musamman daya kasance kanta ko hula babu. Gashin dake a ɗaure a tsakkiya duk ya zazzame a gaba ya tashi.
Cike da ƙosawa da kallon ƙurillar da yake matan tace, “Good morning”. Kamar dama abinda yake jira kenan. Ya janye idanunsa daga kanta yana sakin handle ɗin ƙofar da faɗin, “How are you feeling now?”. “Alhmdllh”. Ta amsa dai-dai lokacin da yake tura glass ɗin dake bangon kudu a falon ƙofa ta bayyana. Ita duk zatonta ma an sakashine kawai domin ado. Amma sai taga ya shige ƙofar ta koma da kanta ta rufe. Shiru tayi tana ta kallon wajen kamar wata sokuwa…….
“Good Morning Maa!”.
Aka faɗa a bayanta. Da sauri ta juyo danjin muryar gardi. Solomon dake ta wani ɓata fuska yay saurin sunkuyar da kansa ƙasa bayan ya gama ƙare mata kallo tun shigowarsa. Wani irin mugun takaicine ya turnuƙe Nu’aymah, taya ƙaton banza da shi zai shigo musu babu wani neman izini. Lallai dolene ta saitama ma’aikatan gidan nan zama, dan bazata ɗauki wannan iskancin ba sam. Da ƙyar ta iya haɗiye bala’in dake a harshenta. Murya a daƙile tace, “Ince dai lafiya?”. “Yes maa! Zanyi sharane. Dan nine mai yima oga gyara”. ‘Zan saita muku layi kai da ogan ai’ ta faɗa da hausa tana zuba masa harara kamar idanunta zasu faɗo. Shi dai Solomon bai ji mita faɗa ba, amma yana kallon harar da take zuba masa. Kuma harga ALLAH sai yaji wani irin shakkarta da ganin ta cika masa idanu da kwarjininta duk da kuwa inda aure yayi sai ya haifi wadda ta fita ma.
“Kaje bana buƙatar sake ganinka ka shigo mani nan, ka ajiye min kayan sharan hannuna zai iya yin komai”.
“Okay maa! I’m sorry”.
Banza tai masa, sai harar da taketa cigaba da antaya masa hannayenta riƙe da ƙugunta kamar mai shirin yin dambe. Kamar walƙiya Solo yabar falon. Ta dafe goshi cike da takaici. ‘Shegu dangin ƴan sama jannati, duk saina muku sabon kaciya tunda idonku bai iya daina kallon mutane. Yanda kasan mayu, suyi maka ƙuri da idanu’.
Haka taita banbamin jaraba ita ɗaya kamar wata zararriya. Ta gyara falon tsaf harma kitchen da ba komai aka taɓa yi aciki ba. Ta kwaso turarenta na ƙamshi haɗin da miss xoxo tai mata ta baje ko’ina da su, (Da gaske masoya, duk mai buƙatar turarurrukan su khumrah da makamantansu ya tuntuɓemu zai samu. Kuma a kowane gari kake muna aika kayanmu insha ALLAH) sannan ta ɗora da Air Fresheners ɗin data gani. Yanda gidan ke tashin ƙamshi tuni zai saka ka barci baka shirya yi ba. Yunwan da takejine ya sakata nufar inda taga an shirya kayan tea cikin wata drawer glass dake a dining ɗin. Sai da ta gama ƙarema kayan shayin kallo da su biscuits dake ciki kala-kala, sai su cornflakes, gyaɗa soyayya a cikin kwalabe, dabino, zuma, kayan ciye-ciye ne dai iri-iri wasuma ko ganinsu bata taɓa yiba. ‘Oh ALLAH, amma guy ɗinnan mugun makwaɗaici ne yasin. Kaga yanda ya haɗa kayan ƙwalama kamar wani sa’an Muhammad. Amma dai anji jiki yasin’. Tana mita tana zagurar waɗanda ta gani a buɗe tana jefawa a baki (makwadaitan sun ƙaru kenan????lol).
★★
Sosai Solomon yaji zafin abinda Aymah tayi masa, ya kuma ɗauki alwashin sai ya saita ta a layi duk da matar ogansa ce. Da wannan takaicin yaje kitchen ya amshi tatattun kayan itatuwan Yoohan ɗin a wajen Blessing data kammala haɗawa. Ta waccan ƙofar yabi ya shiga Gym ɗin. Inda ya tarar Yoohan ko rabin motsa jikinma baiyi ba. “Good Morning sir”. Ya faɗa ransa har yanzu najin zafin Aymah. “Morning?”. Yoohan ya amsa masa yana dubansa da tunanin ko baida lafiya ne. Yanzun ma cike da ɗacin murya yace, “I'm Good sir”. Komai Yoohan bai kuma ce masa ba. Ya cigaba da harkokin gabansa har ya kai lokacin da yake tsayawa. Towel Solo ya miko masa. Amsa yay yana furzar da huci ya ƙarasa kujerar zamansa ya zauna. Solomon ya karaso ya miƙa masa juice ɗin. Sannan ya ɗauka remote ya kunna television.
Sai da Yoohan ya sha kusan rabin juice ɗin, hankalinsa nakan program ɗin yace, “Ka bama su SJ kayan dana ce?”. “Sir wane kaya? Bansan ka ajiye kaya na basu ba ai”. Da mamaki Yoohan ya juyo ya ɗan kallesa, sai kuma ya maida ga television ɗin yana faɗin, “Baka gyara min ɗaki ba kenan?”.
A take abinda Aymah tai masa ya dawo masa a rai. Murya a cinkushe yace, “Sir naje zan gyara Madam ta hanani. ta kuma min gargaɗin ma karna sake shiga sashen gaba ɗaya”.
“Madam? Wace madam?”.
Yoohan yay maganar da tsatstsare sa da idanu. Kan solo a ƙasa yace, “Madam Nu’aymah”. A take ya zayyane masa duk yanda sukayi da Aymah kafin yazo nan wajensa. Ya zata zaiga ɓacin rai tattare da ogan nashi, dan ya saka aiki aƙi masa ko wani ya hana a masa yana ɗaya daga cikin abinda ya tsana, ko madam Chioma ce sai ya nuna ɓacin ransa koda ba zaiyi magana ba. Amma a mamakin Solo sai yaga Yoohan ɗin yayi wani ɗan munafukin murmushi yana ajiye kofin hannunsa. Batare da yace komaiba ya shiga zare takalman ƙafarsa. Yana kammalawa kuma ya miƙe ya fito solo na binsa da kallon tsoro dan ya wuce na mamaki kam.
Har yanzu Aymah na a falon, dan tsabar ƙwarewa a ƙwaɗayin da take cema wani yana yi ita kofi ma ta ɗakko ta haɗa madara da zuma da yawa, tasa ruwa ɗan kaɗan. Ta kwaso biscuits kala-kala kusan shida tazo ta zube a dining tana faman ci da lumshe idanu. Dan babu ƙarya biscuits ɗin duk sunyi uwar haɗuwa.
Cak Yoohan dake ƙoƙarin fitowa ya tsaya kawai yana kallonta da maɗaukakin mamaki da al'ajab. Yayi tsayuwar kusan mintuna uku yana kallonta da ita da falon da ƙamshinsa ke neman saukar masa da kasala kafin ya cigaba da takowa a hankali ya iso inda take. Kamar zaiyi magana sai kuma ya wuce a binsa zuciyarsa fal mamakinta. Ya tabbatar ta gansa amma ta basar.
Tunda ya tura ƙofar ɗakinsa yaga yanda ya barsa haka yake sai ya juyo bai shiga ba. Wajen Aymah dake cigaba da party ɗinta ya dawo. Yanzun kam a bisa tsautsayi ta ɗago kanta, dan batai tunanin shine ya dawoba duk da taji ƙamshinsa sai suka haɗa ido. Saurin kauda nata tayi tana tura biscuit cikin baki.
Shikam yana tsaye hanayensa duka cikin aljihun wandonsa, cikin ƙasa da murya sosai, kamar baya son yin maganar yace, “Hy Smally, tuda kin korarmin maimin aiki sai ki je ki min dan bana iya wanka a toilet ba'a wanke ba”.
Kamar Aymah zata sharesa sai kuma ta kasa, dan yanda yay maganar ƙasa-ƙasa da kiranta sumoli yaja hankalinta wajen son maida masa murtani. Sai dai kuma tana ɗagowa ta sami fuskarsa a tsuke mayun idanunsa kuma ƙyam a kanta kamar zasu haɗiyeta. Kumbura baki tayi da faɗin, “Wlhy niba smally bace, dan ko a yanzu dai shekarata goma sha bakwai da wata tara”.
A ransa yace, ‘Ai fa sai sha bakwai ɗin’.
Ta cigaba da faɗin, “Kuma da kake cewa na korar maka mai aiki, ta yaya zanbar wannan ƙaton gardin yana tsayamin a kai kamar wani mala'ikin dake tsaron ƙofar wuta. Baga ƙannenka nan ba wani yazo ya gyara maka”.
Harga ALLAH maganarta ta bashi dariya, amma sai ya danne. Takawa yay gab da ita. Hakan yasa ta miƙe zumbur tana ajiye ledar biscuit ɗin hannunta, ta tura kujerar baya danta samu hanyar guduwa. Caraf ya riƙo hannunta ta faɗo jikinsa. Duk da yaji ɗan zafin yanda ta faɗo masa bai damuba. Sai ma hannunsa daya ɗora akan ƙugunta ya sake matsota ta manne masa sosai.
“Ouch!! Wannan muguntar fa?”. Ta faɗa tana ƙoƙarin ɗago fuskarta dake saman ƙirjinsa gab da haɓarsa, dan har ɗan gashin gemunsa na gogar gashin kanta. Kallon ido cikin ido sukaima juna. Tana ƙoƙarin son kauda nata amma ya hana, da wani irin yanayi yace, “Miyasa ke bakinki baya iya daina magana? Kowacce amsa kinada ita?”.
“To sai in zauna a ringa cutata, ku mutane ai kunason mutum ya zama banza ku dinga takashi kamar wani tiles kuna wucewa”.
Shi sam bama ya fahimtar mi take faɗa, hankalinsa gaba ɗaya yana kan bakinta ne da idanunta da suka ciko da ƙwalla. Hakan yasa baice mata komaiba, sai saukar babban ɗan yatsansa taji akan gefen bakinta. Saurin kauda fuskarta tai ƙoƙarin yi tana zaro ido. yayinda shi kuma ya ɗaga mata yatsan yana nuna mata ɓurɓushin biscuit daya goge mata. Haɗiye abinda zata faɗa ɗin tayi da ƙoƙarin san zamewa daga jikin nasa. Babu musu ya saketa kuwa.
Daɓar ta faɗa saman kujerar da take zaune da. “Wayyo Abbana!”. Ta faɗa saboda zafi da taji.
Dafe tebirin yayi da hannu biyu ya ranƙwafo kanta har tanajin saukar numfashinsa. Cikin kunnenta yace, “Silly girl, wannan shine maganin masu bakin magana kamar akku”.
Hawaye na silalo mata akan fuska ta sa hannu kan damtsen hannunsa ta turesa. Fuskarsa ɗauke da murmushin mugunta ya riƙe hannunta, “Tashi muje ki gyaramin ɗaki kona sake ɗagaki sama na dire a kujerarnan har sai........ ” Sai kuma yay shiru bai ƙarasa ba
Zatai magana ya ɗora yatsansa saman bakinta yace, “Shiiii!!!!”. Sai kuma yaja hannunta dake cikin nasa ya miƙar da ita. Tanaji tana gani ya jata har ɗakinsa. Ganin ya nufi hanyar da take ƙyautata zaton toilet ne ta tirje da faɗin, “Nifa bana shiga toilet babu ɗan kwali”.
Baice komaiba, sai sakin hannunta da yay ya nufi Wadrobe ɗinsa, sai gashi riƙe da babban handkerchief. Gani tai kawai ya warwaresa yay masa linkin ɗankwali ya ɗora mata bisa kai. Tsaf ya ɗaura mata shi kuwa duk da bawai ya buɗe bane da ƙyau yanda ya kamata, amma dai ya rufe gashin. Sake kama hannun nata yay zuwa cikin toilet ɗin.
“Ki fara wanke nan, wanka zanyi na fita”. Daga haka ya saketa ya fita.
Dubansa tayi kamar zatai magana sai kuma tai shiru dan harya gama ficewa. Tsaf ta gama bin toilet ɗin da kallo, dan babu ƙarya ya haɗu, gashi an zuba kayan toilet ɗin irin kalar, garai-garai ɗin nan kamar ƙanƙara, sai dai sunfi ƙanƙara duhu dan sunyi ɗan kalar ash da fari-fari. Komai tsaf a tsare inda ake buƙatar ganinsa babu wani dattin da yake faɗa akansa bazai iya wankan ba. Da yake neman aikin yin take saboda jikinta da yay mata nauyi sai gashi ƙara gyarashi tsaf, kamar taje ta ɗakko turaren toilet ɗin da miss xoxo ta haɗa mata mai shegen ƙamshi na wanke toilet sai kuma ta fasa. A cewarta kada ta cika zaƙewa ya ɗauka ya sameta ne a ɓagas.
Fitowa tai riƙe da ƙugu alamar ta gaji, Yoohan dake zaune a kujerar dake tebirin karatunsa ya ɗago yana kallonta jin tana nishi. Dan shi a zatosa ko faɗuwa tayi a toilet ɗin ma. “lafiya?”.
Baki ta kumbura gaba da faɗin, “Na gaji ne, bayana kamar zai ɓalle”.
“Kaɗanma kenan, tunda kika koramin mai mini ai”. Ya faɗa yana ɗauke kansa daga gareta ya maida ga lap-top ɗin gabansa da yake aiki a ciki. Haushin maganar tasa ya hanata tanka masa, ta ƙarasa ga makeken gadonsa ta faɗa a kai tana faɗin, “Wash Umm na gaji, nima bara na rama hawar min gado da kayi”.
Miƙewa yay idonsa a kanta. Batare da yace mata komaiba ya nufi bayi yana wani murmushin daya zo masa babu shiri. Harga ALLAH ta burgesa da tai aikin, dan baiyi zaton zatayin ba saboda sanin tsiwarta. Iyawarma baiyi zaton ta iya ba. Amma daya shiga bayin sai yagama gyaran natama yamafi na Solomon ɗin.
Sai da taja kusan mintuna uku a kwance tana shaƙar ƙamshinsa daya manne bedsheet ɗin, kafin ta miƙe ta fara gyarawa duk da harga ALLAH ta gaji da gaske. Amma batason ya fito ya isketa. Kuma tanama buƙatar zuwa tayi wanka itama dan cikinta dam yake da ciye-ciyen da tayi.
Tana tsaka da mopping kuwa ya fito. Kallo ɗaya tai masa tai azamar maida kanta ƙasa ta duƙar tana ƙunƙunin wai mara kunya ne mutumun nan. Yasan da ita amma ya fito da towel.
Oho shi baimasan tanai ba. Dan mirror ya nufa bayan shima ya mata kallo guda ya dauke kansa. kansa tsaye yake komansa duk da kuwa yasan tana cikin ɗakin. Ta gama tana fesa fresheners data gani shi kuma ya ɗakko kaya zai saka. Juyowar da zatayi idonta ya sauka a kansa yana ƙoƙarin ƙwaye towel ɗin. Cikin subutar baki tace, “Babbar bala'i a gabana?”. Kafinma ya fahimci mitake nufi ta jefar da roban freshener ɗin ta kwasa da gudu ta fice.
Da kallo ya bita ransa fal tunanin lafiya kuwa? Sai kuma yay saurin kallon hannayensa biyu dake riƙe da gefe-gefen towel ɗin. Ai baimasan sanda ya fashe da dariya ba. Ya saki towel ɗin yana zama bakin gadon har sannan dariyar yake hannayensa riƙe da kansa. Pant ɗin dake jikinsa fari ƙal ya shafa yana faɗin, ‘Silly girl, an gaya miki zan fito gabanki babu pant’.
Oho Aymah tuni takai ɗakinta ita dai, ta faɗa toilet tana hakki idanunta a rufe kamar ance gashi gabanta. Taja kusan mintuna biyu sannan ta sami nutsuwa, ta ɗan dafe kanta a ranta tanajin da sakamakon abinda zata gani kenan da bata biye masa tai wannan shararba. Dan dama tayine kawai saboda an koya musu biyayya gana gaba dasu, sannan nasihar iyayenta a gareta tana nan daram cikin ranta babu abinda ta manta a ciki. Daga haka itama ta zame kayanta ta hau yin wankan.
Ta kammala shirinta kenan cikin baƙar doguwar rigar jallabiya data ji stones ya shigo. Saurin juya masa baya tayi tana ɓata fuska. Kansa ya girgiza kaɗan ya cigaba da takowa cikin ɗakin. A kan laɓɓanta ta furta, ‘Mayen suit ’ dan tsaf ta gama ƙare masa kallo ta cikin mirror ba tare da ya sani ba. Shima ɗin dai kallonta yake daga sama har ƙasa dan rigar ta mata ƙyau sosai. Idonsa akan dokin wuyanta da kananun gashi ke kwance luf-luf yace, “Ni zan wuce porthercout, sai gobe idan ALLAH ya kaimu zan dawo”.
Da sauri ta juyo tana kallonsa idanu a buɗe, tace, “Ni kuma ka barni a ina?”.
Da mamaki yace, “A ina kike anan?”.
“Gidanku”.
ta bashi amsa kansa tsaye.
“Oh to anan zaki zauna kenan, tunda kinsan ni dai aiki zanje ko”. Yanda yay maganar a dakile ne ya bata haushi. Cike da tsiwar tata data motsa tace, “He’em. Wlhy to nima ka kaini gidan Abbah dan bazan zauna ni ɗaya ba. Sannan kuma nama Abbana maganar ƴar aiki daga can kano yace babu ruwansa saika amince. Please ka kirashi kace ka yarda”.
Necktie ɗinsa dake rike a hannu da rigar saman suit ɗin ya gyarama zama yana tsatstsare ta da idanunsa, “Duk waɗanan masu aikin dake gidan nan su menen amfaninsu da har sai an kawo mai aiki daga kano?”. “Toni bana buƙatar aikinsu, ni dai kawai a akawomin YARENA ADDININA hankalina zaifi kwanciya. Amma ta ina zan yarda waɗan nan garadan na shigomin kai tsaye gasu da shegen kallo kamar ƴaƴan mayu”.
Ƙala baice da itaba, dan shima ya tafi wani kuma tunani daban. A ganinsa zaiyi amfani da wannan damar wajen binciko abinda yay alwashi. Dan dole kam ya yarda sai sun sami kusanci da wani ɗan gidansu Aymah anan sannan zai fahimci abinda yake zargin. Kuma ya tabbata idan aka kawo mai aikin duk wanda yayma Nu’aymah wancan ƙullin zai haɗa alaƙa mai ƙarfi da wanda za’a kawo musun saboda samun bayanai akanta. Shi kuma wannan shine mabuɗin bincikensa………..
“Na shirya” data faɗa ne ya maidosa hankalinsa. Yay saurin dubanta da ƙyau yana bin handbag ɗin hannunta da kallo da ƙaramar leda. ‘Lallai kan yarinyar nan da motsi’ ya ayyana a ransa yana ɗauke idonsa a kanta. Duk da take masa kallon ba bahaushe ba duk yanda al’adunsu da dokokin musulinci sai da Hamza manager ya bashi haske a kansu daki-daki. Shi kuma ya ɗauki ɗammarar bi da ita akansu kodan ta samu nutsuwar zama da shi.
“Karki ma ɓatama kanki rai dan babu inda zakije. Idan abokan hira kike bukata gidan nan cike yake da mutane”. “To ni……..” ta kasa ƙarasawa saboda matsota da yayi. “Ke me?”. Ya faɗa yana tsuke fuskarsa da ƙyau. Bata sake magana ba dan kwarjinin da yay mata da cika idanu. Ga kuma zuciyar ta gado ta yunƙuro tazo gab da maƙoshi ta tsaya. Harya juya ya fita bata sake magana ba sai hawayene da suka cika mata idanu. Yana rufe mata ƙofar kuwa ta matsosu suka zubo.