NOVELSUncategorized

SOORAJ 6

*????SOORAJ FANS GROUP????* 

Follow this link to join my WhatsApp group:     

*Idan kinsan Bazakina Comment ba kada kishiga, ONLY NOVELS kawai mukeso, bayan haka bamason kowani irin post…. Bamason Talla kona menene, idan kinyi zaki ganki a waje*



????????????????????????????????????????

             *SOORAJ*

    *Written By*
Phatymasardauna

*Dedicated To My Life (Sardauna)*

*????Kainuwa Writers Association*

_{United we stand ans succeed; Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}_

*https://www.facebook.com/kainuwawritersassociation*

              *WATTPAD*
        @fatymasardauna

        *CHAPTER 6*

Tunda ya kwanta bacci bashi ya tashi ba sai da aka soma ƙiraye ƙirayen sallan Azahar.  Toilet yashiga yayo wanka.  Still riga da wando na jeans yasanya ajikinsa. Masallacin dake kusa da gidansa ya nufa donyin sallah.   Tun da yafita yin sallah baidawo ba sai ƙarfe huɗu na yamma, wanka yasakeyi.   Combat jeans ne ajikinsa baƙi sai kuma wata farar riga mai ɓaƙaƙen aninaye.    Yana tsaye agaban dressing mirror yana taje tulin sumar kansa, wanda yasha aski irin na zamani, screen ɗin wayarsa ya soma kawo haske, ɗan matsawa kusa da yawartasa yayi.   Sunan  Mas’oud ne ke yawo akan screen ɗin wayar, kasancewar ya sata a silent shiyasa batayi ƙara ba, ɗan ɓata fuska yayi haɗe da ɗaukan wayar yakara akan kunnensa.  

 “Ina falo” Inji cewar Mas’oud.

 “Okay”  kawai Sooraj yafaɗa akasalance tare da aje wayartasa,   bai fita falon ba yaci gaba da taje sumar kanshi, saida ya kammala duk wani abu dazaiyi kana ya ɗauki wayarsa dakuma car key ɗinsa yafita zuwa falo.

Cike da takaici  Mas’oud ke kallonsa,  duk da yasan cewa halin Sooraj ne shanya mutane, amma kuma abun da yayi masa yauɗin yayi masa ciwo.   

“Inakuma zakaje?” Mas’oud yatambayesa yana me ƙare masa kallo.

“Asibiti”
SOORAJ yabashi amsa ataƙaice.

“Abiti kuma? Baka da lafiya ne?” Mas’oud yajero masa duk waƴannan tambayoyin alokaci guda.

Ɗan ya mutsa fuska yayi haɗe da sanya hanu ya shafi kwantaccen sajen dake shumfuɗe akan fuskarsa.   
  “Accident mukayi, zanje na duba yarinyar dana bugene kota farfaɗo”  ya faɗi haka yana me nufar hanyar fita daga falon, kai kawai Mas’oud ya girgiza haɗe da miƙewa tsaye yabi bayan SOORAJ ɗin.   SOORAJ ne ke tuƙa motar yayinda Mas’oud ke zaune agefen mai zaman banza.  Tafiya suke babu wani wanda yace da   ɗan uwansa wani abu, ahaka har suka kawo asibitin,   sam Mas’oud baiwani damu da shirun da SOORAJ ɗin  yayi ba, because yasan hakan halinsa ne, bakoda yaushe yacika yawan magana ba, amma idan kafahimcesa yana da daɗin zama, dan bayashiga abun da babu ruwansa… 

Atare suka jera suka shiga cikin asibitin.   Office ɗin Dr.Salees suka nufa, shiyayi musu jagora zuwa ɗakin…  dama yana shirin zuwa dubata kenan suka shigo.

Tananan har yanzu bata farfaɗo ba, wasu allurai Dr.Salees yayi mata,  juyawa yayi ya kalli SOORAJ dake zaune akan wata plastic chair….  “Zata iya farfaɗowa akowani lokaci da yardan Allah, Yana da kyau katsaya atare da ita.” Inji cewar Dr.Salees.

Kai kawai ya iya jinjina wa Dr.Salees alaman yaji, fita Dr.Salees yayi daga cikin ɗakin.  

Kallon Mas’oud daya kafe yarinyar da idanu SOORAJ yayi, tsayawa yayi yana kallon yanda idanun Mas’oud ke yawo ajikin yarinyar ko ƙyaftawa ba yayi,  takaicin Mas’oud ɗinne yakamashi, sam shi kam baiga wata mace aduniya dazai tsaya ɓata lokacinsa wajen kallonta ba, yaga manyan mata da suka amsa sunansu mata baiji komai gamedasu ba balle wannan ta tsitsiyar yarinyar, inbanda ƙaddara ma maizai haɗashi da ita,  sam shi baya shiga sha’anin mata, saboda yasan menene matsalarsa, wannan ma don dolene kawai, amma dazaran ta farfaɗo zaisa amaidata inda ya ɗaukota.

“Tunda kana nan ni inaga kawai zantafi yau nakeso nakoma Abuja, please kakula da ita, idan tafarfaɗo tagayama garinsu saika maida ita!” SOORAJ yafaɗi haka yana me miƙewa tsaye. 

Da sauri Mas’oud ya kallesa cikin mamaki yace “Zaka koma Abuja kuma?”

Kai SOORAJ ya jinjina masa alamar “Eh”

“Hmmm lallai SOORAJ baka da imani, kabuge yarinya kuma katafi kabarta? wato nine marainin wayonka shine kakeso katafi kabarni da ita ko?”

Murmushin gefen baki SOORAJ yayi wanda yayi masifar ƙarawa fuskarsa kyau. 

“Mene matsalarka Mas’oud idan kakula da ita? Kasan inada abubuwan yi da yawa, banjin kuma zan iya ɓata lokacina akan mace” SOORAJ yafaɗi haka yana me kai dubansa ga agogon dake ɗaure a tsintsiyar hanunsa.

“Nima ai bazaman banza ne sana’ata ba, kai kabugeta kuma kai kake da alhakin tsayawa akanta kakuma bata kulawa harsai ta warke, saboda haka ni kaga tafiyata” Mas’oud yafaɗi haka aƙufule, don ya lura tsagwaran iskanci ne ke damun SOORAJ ɗin.

Still murmushin gefen baki yayi haɗe da bin Mas’oud ɗin da kallo harya fice daga cikin ɗakin.      Kan kujera yakoma ya zauna, yayinda ya juyawa gadonnata baya, wayarsa yaciro ya soma latsawa..

Ahankali take ware manya manyan oily eyes ɗinta masu kyau da burgewa,  dishi dishi tasoma gani, kafun daga bisani idanun nata suka soma washewa,    ɗakin tasoma ƙarewa kallo, yayinda ƙwaƙwalwarta ke tunano mata abubuwan da suka faru, amatuƙar razane ta ƙwalla ƙara..     “Wayyo Allah Nashiga Uku dan Allah karku cutar dani!!”

Azabure yajuyo jin ihunta abayansa,   yunƙurin tashi zaune tasomayi amma ina jin kanta take yayi mata wani irin nauyi, ga wani raɗaɗin azaba dake ratsata…

Tsuka yayi ƙasa ƙasa tare da maida kansa ga wayarsa yacigaba da latsawa, yatsani mutumin da baida nutsuwa.

Babu yanda ta iya haka takoma ta kwanta tana gunjin kuka, saboda kotafi kowa ƙoƙari ayanzu bazata iya tashiba.   Idanunta ne suka sauƙa akan bayansa, domin dama yabata baya.   Ganin namiji na zaune ya bata baya yasa taƙara volume ɗin kukanta,  jikinta na rawa tace “Dan Allah kuyi haƙuri ku ƙyaleni, nakoma inda nafito, wallahi nayarda ma ni Zan auri tsoho ɗan dashe’n, nidai kada ku cutar dani, wallahi ni marainiya ce, dan Allah ku ƙyaleni natafi!” kuka take tsakaninta da Allah tana zabga magiya da roƙo, amma ko motsi baiyiba balle tasaran zai juyo gareta, duk atunaninta shiɗin ɗaya daga cikin mazan da suka ka mata ɗazu ne.  

Ganin baijuyo gareta ba yasa tacigaba da kukanta,    yana zaunene kawai amma jiyake kamar ana hautsina ƙwaƙwalwarsa, kuka yana ɗaya daga cikin abun daya tsana,   wata tsuka yaja me ƙarfi haɗe da juyowa ya watsa mata wani irin kallo, idanunsu ne suka sarƙe acikin na juna,  wani irin shock Ziyada taji acikin jikinta, lokaci guda ta haɗiye kukanta,  ɗauke idanunsa yayi daga cikin nata yaci gaba da latsa wayarsa.  

Ajiyar zuciya tashiga sauƙewa akai akai, neman kukannata tayi ta rasa, sai jikinta daya ɗauki wani irin zazzaɓi mai zafi.   Idanunta na kallon bayansa, cikin wata irin murya mai sanyi tace…. 
“Kamaidani gidanmu kaji!” 

Tsayawa yayi daga latsa wayar  da yake yayi shiru…  Bugun zuciyarsa ne ke ƙara tsananta, lumshe kyawawan idanunsa yayi, tare da sauƙe wata irin ajiyar zuciya.   Tashi yayi ya fice daga cikin ɗakin batare daya kalli koda ɓangaren da take ba.

Ganin yafita daga cikin ɗakin yasa  Ziyada fashewa da kuka. 

“Shikenan na mutu yatafi ƙiran sauran ƴan uwannasa, shikenan zasu zo su lalatamin rayuwa!” Cikin gunjin kuka take maganar.

Jin anbuɗe ƙofar ɗakinne yasa, tayi saurin kallon bakin ƙofar,  murmushi Dr.Salees yasakar mata haɗe da cewa 
“Yauwa Patient kintashi ko? sannu, yanzu inane ke miki ciwo ?” 

Kasa amsa masa tayi saima kafesa da idanunta dake ɗigan ruwan hawaye da tayi,  kamar yasan tunanin da take acikin ranta, murmushi yakumayi akaro nabiyu haɗe da cewa “Ki kwantar da hankalinki nan asibiti ne, ba wai wajen da za’a cutar dake ba.”

Rumtse idanunta tayi da ƙarfi sai alokacin tatuna da cewa tana cikin gudu taji wani abu ya doketa har saida ta ɗagu sama, to daga wannan lokacin bata sake sanin maiya faru ba sai yanzu data ganta cikin wani ɗaki.

Hanu Dr.Salees yakai jikinta ya taɓa, zafi zau yaji ajikinnata,   alluran daya shigo dasu yasoma ɓarewa,  ganin allura ahanunsa yasa Ziyada sake fashewa da sabon kuka, murya adashe tace “Don Allah kayi haƙuri karkamin, wallahi bazan sake guduwa ba!”

Mamakine yakama Dr.Salees sai kawai yatsaya yana kallonta.  Dai dai lokacin SOORAJ yashigo cikin ɗakin.

Kallonsa Dr.Salees yayi haɗe da cewa. “Yauwa SOORAJ gwamma daka shigo ai, kaga wannan ƙanwartaka tsoron allura takeyi, kuma akwai zazzaɓi ajikinta dole sai anyi mata allura sannan zata samu relief, bayan haka kuma yakamata kanemo mata ko tea ne tasha, akwai yunwa ajikinta sosai”

“Okay, kayi abun daya dace kawai!” SOORAJ yafaɗa a gajarce, domin baison yawan surutu. 

Kai kawai Dr.Salees yagirgiza aransa yana mamakin miskilanci’n SOORAJ.

Ziyada na kuka haka Dr.Salees yayi mata allura, SOORAJ kuwa yana zaune ko kallon inda suke baiyi ba, earpiece ma yasa akunnensa yana sauraran cool music.   Dr.Salees nagama aikinsa yafita daga cikin ɗakin.

Cusa kanta tayi acikin pillow tana kuka, hakanan taji haushin  mugun mutumin daya sanya akayi mata allura, dama ance mata turawa mugayene to gashi yau ta tabbatarwa kanta, domin kuwa tana da tabbacin  cewa shiɗin idan ba bature bane to kuwa balarabe ne, don wannan farinnasa ba’a banza ba. 

Yana zaune aka soma knocking ɗin ƙofar ɗakin. 

1 2Next page

Related Articles

Leave a Reply

Back to top button