Uncategorized

TAKUN SAKA 1-10

       “Shikenan bara na kira Abubakar naji idan yana kusa ko Muhammad”.

       “To Ummi”. Zahidah ta faɗa tana share hawayen da suka gangaro mata akan kumatu. A kallo ɗaya zaka fahimci a matuƙar firgice take. Gashi ita kaɗai ce yau dan Hafsat batazo ba saboda ƙafarta.

     Hango Yaya Ammar da ke nufota da sassarfa ya sakata tunawa da yana a cikin makarantar shima. A zabure itama ta nufosa. 

       “Zahidah! Ina Muhibbah?”. 

  Ya faɗa cikin furzar da hucin hakkin gudun da yayi dai-dai isowarsa gabanta. 

        Bayanin abinda ta sani da wanda taji a bakin mutane tai masa tana share hawaye. Hankalinsa ya ƙara tashi matuƙa shima. Dan duk tsokanarta bata taɓa kaiwa matakin hakaba, a yanda yaji wai ƴan sanda da manyan bindugu ya matuƙar harmutsa tunaninsa. 

    Babu shiri ya shiga neman no ɗin Yaya Abubakar, sai dai kuma number busy take nuna masa alamar yana waya da wani kenan ko makamancin hakan. Maida akalar kiransa yayi akan Yaya Muhammad. Bugu biyu ya ɗaga. Ko sallama bai masa ba ya shiga masa bayanin abinda ke faruwa.

      Ko tari kasa yi Yaya Muhammad yay. Sai numfashinsa ne dake tafiya a sarƙe tamkar mai ciwon Asthma. Batare da ya iya furta komai ba ya yanke wayar. Kamar jira sai ga kiran Ummi ya shigo masa. 

     Sam baiyi tunanin taji mike faruwa ba itama. Dan haka yay ƙoƙarin saita kansa dan ganin bai tada mata hankali ba. Sai dai a yanda yaji muryarta tun a sallama ya matuƙar tada masa hankalin. A hautsine ya shiga tambayarta lafiya? Dan ko kaɗan basason tashin hankalinta.

          Duk yanda Ummi taso danne damuwar dake a cikin muryarta ta kasa hakan. Cikin gwamewar numfashi ta shiga yimasa bayanin duk yanda sukayi da Zahidah.

         Da sauri ya ce, “Ummi dan ALLAH ki kwantar da hankalinki, insha ALLAH zamu nemi idan take bara na nema Abubakar yanzun nan”.

   Bai jira cewarta ba ya yanke wayar dan bayason shima ta fahimci rauninsa kai tsaye…………..✍

*TATATTUN FITATTUN LABARAN ZAFAFA BIYAR NA 2022*????????????????????????

*ALSHIRINKU MASU KARATU!!!*

*_NAJI DADI SHINE GARI……_*

*KINA DA BUQATAR TSAFTATATTUN LABARAI DAKE CIKE DA*

_ILIMI_

_NISHADI_

_TSUMAMMIYAR SOYAYYA KUMA MAI TSAFTA DA ZATA SAKI SHIGA SHAUQIN SOYAYYA DA DUKAR DARUSSA KALA KALA A FANNIN ITA SOYAYYAR DA RAYUWA?_

*MAZA GARZAYO KI NEMI LITATTAFAN ZAFAFAN MARUBUTA GUDA BIYAR*

     *NA SABUWAR SHEKARAR 2022*

*WADANDA SUKA ZAUNA,SUKA TACE LABARANSU,SUKA MUSU ADO DA SABUWAR FASAHA!!!*

*SABBIN LABARAI*

*SABUWAR SHEKARA*

*SABON NISHADI*

*_FARINCIKIN KASANCEWA DA MARUBUTAN CIKIN SASHEN DA AKE GWABZA RUWAN SHARHI DA MUSAYAR RA’AYI NA DABANNE_*

*MAZA ‘YAR UWA SIYA NAKI KI SHIGA SAHUN WANNAN TAFIYAR,TARE DA SAMUN DAMAR SHIGA SASHEN COMMENTS NA MUSAMMAN MALLAKIN MARUBUTAN*

*_TAKUN SAAƘA!!_* _Bilyn Abdull_.

*_SO DA ZUCIYA_* _Hafsat (miss xoxo)_

*_DEEN MANSHAL_* _Mamu gee_

*_ƊABI’AR ZUCIYA_* _Safiyya huguma_

*_HALIN GIRMA_* _Hafsat Rano_

*ta hanyar tura kudin littafinki zuwa ga wadan nan lambobi dake qasa*

6019473875

MUSAA ABDULLAHI SAFIYA

keystone bank

Saiku tura shaidar biyanku zuwa ga wannan number 

08184017082

*IDAN KATI NE KUMA KO VTU,SAI KU TURA ZUWA GA*

09134848107

Littafi daya

1____300

2____400

3____500

4____700

5____1,000 (1k).

*INGANCI DA NAGARTAR RUBUTU,BABU NADAMA KO DANA SANI*????????????????????????????????????????????????

#team ZAFAFA BIYAR????????????????????

*_ALLAH ka gafartama iyayenmu????????????_*

   

*_Typing????_*

*_Chapter Seven_*

……….Lokaci da aka basu da ga gidan gwamnati na kamo wannan gagarumin ɓarawo da babu wanda yasan ainahin kamanninsa na zahiri yay matuƙar tada hankalin kowacce hukuma ta ƴan sanda dake a jihar. A ɓangaren jami’an ƴan sanda na farin kaya tuni sun duƙufa wajen bincike suma. Musamman da ya kasance jami’ansu ne suka sami nasarar samo wheelchair da sauran kayan da ɓarawon yay amfani da su a waccan ranar.

            Tabbas wannan ɓarawo yana da matuƙar wayo da dabaru kala-kala da ganosa ke bama duk wasu jami’ai wahala kai tsaye. A duk ɓarnar da zai aikata yana aikatata ne da maban-banta fuskoki da salo daban-daban kuma. A kusan shekara biyu kenan da fitowarsa a bayyane babu wanda zai iya cewa ga fuskarsa ta ainahi ko samun wani labari nasa koda ƙanƙani ne.

        Duk da dai wasu a cikin jami’ai da suka ƙware sosai wajen aiki da binciko mai laifi sun taka rawar gani sosai wajen kafa masa tarkuna na musamman amma yana tsallakesu saboda duk tsiyar da zai shuka ba gaba gaɗi yake aikata ta ba sai ya shirya da shiri na gaske.

          Bayan zama na musamman da sukayi jiya game da binciken da sukeyi akansa furucin matashiyar budurwa ya shigo cikin jerin abubuwan da suka zauna domin tattaunawa. Lokaci ne da bai kamata suyi sakaci da duk wata dama da zatazo musu ba komin ƙanƙantarta. Dan haka basu tsaya sanya ba wajen bibiyar matashiyar budurwa mai cikakken suna *_MUHIBBAT ALIYU HAMZA_* da jami’insu ya kawo musu labarin alwashinta akan abin farautarsu. Dan haka suka kasance biye da ita tun a safiyar yau, tun daga ƙofar gidansu har zuwa cikin makaranta, shigarta class da fitowarta zuwa Computers room. Dukkan binciken data gudanar har zuwa kiran da taima Yaya Abubakar duk akan idon wanda ke biye da ita ne batare data sani ba…

        

         Sosai tashin hankali ke tattare da Muhibbah ganin inda aka kawota. Duk da Yayanta jami’in tsaro ne na ƴan sanda mai muƙamin d.p.o bata taɓa zuwa police station ba. Amma a yau sai gata a cikin headquarters na ƴan sandan farin kaya tsumu-tsumu batare da tasan laifin data aikata ba.

         Wani lafiyayyen office aka kaita da yaji kayan more rayuwa tamkar ba’a hukumar ƴan sanda ba. Ta saci kallon dattijon mutumin dake zaune kansa duƙe yana aiki kan takardun dake a gabansa. Cikin girmamawa wanda ya shigo da ita office ɗin ya ƙame yana salute ɗinsa.

        Sai a lokacin ya ɗago fuskarsa ɗauke da murmushi ya dubesu ita da shi. Kansa ya jinjinama wanda ya kawota ɗin idanunsa a kanta. Gurin zama ya nuna mata da faɗin, “Ɗiyata bismilla zauna ko?”.

        Ajiyar zuciya ta saki dan har cikin ranta ta ɗanji sanyi. Gaishesa tayi da girmamawa zuciyarta na sake samun nutsuwa da shi. Ko ba’a faɗa mataba a yanayin shigarsa da shekarunsa ya isa tabbatar mata shi ɗin mai faɗa aji ne a hukumar.

           Ɗan kafeta yay da idanusa na kusan sakan ashirin ko ƙyaftawa bayayi. A take tsigar jikinta ta fara tashi tsoro na sake faɗaɗa a zuciyarta. _Hasbinallahu wa-ni’imar wakil_ ta shiga maimaitawa tare da sunayen ALLAH. 

          Murmushi ya sakar mata da yin ƙaramar gyaran murya yana ɗauke idanun nasa a kanta. Cikin taushin murya yace, *“Muhibbat Aliyu Hamza ko?”.*

        Hibbah ta jinjina masa kanta cikin dakiya da dauriyar hana bayyanar gazawarta tana faɗin, “Eh yallaɓai”.

       “Ɗalibar koyon kimiya da fasaha a babbar jami’a ta jihar nan?”.

     Nanma kanta ta jinjina masa da faɗin, “Eh yallaɓai”.

        “Uhm masha ALLAH. ALLAH yay riƙo da hannayenki ki zama abar alfahin ƙasarki baki ɗaya. Ina matuƙar son naga ƙananun yara musamman ma mata masu himma da ƙwazo akan abinda yay mana ƙaranci irinki”.

      A karon farko Hibbah ta saki murmushin jin daɗin yabon data samu da ga garesa tana faɗin, “Thanks you Uncle”.

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21 22 23Next page

Related Articles

Leave a Reply

Back to top button