Uncategorized

TAKUN SAKA 1-10

        Yah Ammar dake kujerar gefenta yana ƙoƙarin fara cin indomie ɗin data dafa masan ya zubomata uwar harara shima yana faɗin, “Dama can kin saba makararki yarinya zaki wani jingina dani”.

       Baki ta sake buɗewa zatayi magana Yah Usman dake duba wasu takardu dake gabansa a dining ɗin shima ya watso musu harara ita da Ammar ɗin, “Dalla malamai karku cika mana kunne kuma ko”.

     Ummi dake turama Hibbah kofin kunu data zuba mata tace, “Ai inda sabo sun saba, Ammar da Tanee basa taɓa zama waje guda basu isheka ba, sai kace suna ganin hanjin junansu. Nikam babu mai barina da ciwon kai kowa yayi ya gama ya kama gabansa”.

       Baki Hibbah ta kuma cikawa da iska tana duban Yah Muhammad da Yah Abubakar masu kareta. Yaya Abubakar dake hidimar haɗama kansa shayi yayi murmushi, “Auta yada kallona kuma? Nimafa yau gashi kina neman makarar dani bayan nace da wuri zan fita”.

       Cikin shagwaɓar da takema yayun nata saboda so da ƙaunarta da sukeyi ta ce, “Yaya kaima ko?” ta faɗa tana maida dubanta ga Yah Muhammad da ke ta faman latsa wayarsa. Ƙaramar dariya yayi tunkan tace komai, ya ajiye wayar tasa yana amsar kunun da shima Ummi ta zuba masa dan kusan halinsu ɗaya da Muhibba shima bai cika son tea ba. “Kinga autan Ummi manta da kowa ki karya, yau da kaina ma zan kaiki makaranta bazakibi Ammar ba, maza lokaci na sake ja”.

    Jin Yah Muhammad yace da kansa zai kaita makaranta yau ya saka bakinta washewa. Ta kalli Yah Ammar abokin tsamartata tana masa gwalo. Kusan duk sai da sukai murmushi kowa na girgiza kansa cike da mata kallon so da ƙauna.

     Basai an faɗa ba, yanda ƴan uwata da Ummin su kema Hibba a gidan zaisa kowa fahimtar ita ɗin ƴar gata ce kuma shalele. A kullum kowa burinsa yaga farin cikinta. Koda laifi tayi suka zaneta ko mata faɗa daga baya sai su koma mata nasiha da lallashinta har sai sunga ta koma rayuwata ta ƙiriniya da rashin ji suke samun nutsuwa. Sai dai kuma a ɓangaren Abba da sauran matansa sam ba haka bane. Sun tsani Muhibbat tamkar ita kaɗaice ƴa a gidan. Hakama sauran ƴaƴan gidan duk basa sonta. Kafin Hibbah takai haka kullum tambayata mi sukai musu? Amma babu mai bata amsa a tsakanin Ummi da yayunta guda biyar. Sai da tayi hankali ne zuwa yanzu take ɗan fahimtar wasu abubuwan duk da dai ba wani ya taɓa zama ya sanar da ita gaskiyar dalilinba har zuwa yanzun. 

     Itace farkon kammalawa, ta miƙe tana faɗin, “Alhmdllh”. 

         Yaya Abubakar ya dubeta da kulawa cikin lallashi yace, “Auta ki dingacin abinci ko zaki ƙara girma fiye da haka dan ALLAH, ke kowa na girma yayi ƙiba banda ke, makarantar nan kamar ƙara tsiyayar dake take ma”.

      Murmushi tayi cike daso da ƙaunar Yayun nata masu sonta. Tace, “Yah Abubakar duk wannan ƙatuwan dana zama, da kaɗan fa Yah Ammar ya fini tsaho”.

    Harara Yah Ammar ya galla mata da faɗin, “Tunda nine marainin wayonki ko? bar ganin Ummi a wajen, na tashi ɓarar dake zanyi ALLAH”.

         Dariya duk suka sanya masa, dan da alama da haushi yake maganar. Hibbah tai masa gwalo da ɗaukar bag da gyalenta ta fice da gudu saboda ganin zai miƙe, tasan kuma kanta zaiyo.

        A ƙofar fita falon taci karo da Abba. Tai saurin komawa baya jikinta naɗan rawar kaɗuwa. Dan duk da rashin tsoro na Muhibbah a rayuwarta tana matuƙar jin tsoron Abba tun tana ƴar ƙarama. Hararar da yake wulla mata ya sata sake sata duƙar da kanta idanunta na tara ƙwalla.

        “Wane kalar shashanci ne kuma haka? Da girmanki amma kullum lalacewa al’amuranki ke ƙarayi saboda ke ƴar ido ce!!”.

        Sam Hibbah bata son tsawa, shiyyasa da zaran Abban ya mata ita take rikicewa, yanzu ɗinma duk sai jikinta ya hau ɓari, muryarta na rawa alamar tahowar kuka tai saurin faɗin, “Kayi haƙuri Abba bansan ka tahoba ALLAH. Ina kwana”.

         Ciki yay batare daya amsa mataba yana jan tsaki. Hibbah ta bisa da kallo wasu hawaye masu zafi na sakko mata bisa ƙyaƙyƙyawar fuskarta. Ido suka haɗa da Yah Usman. Ya girgiza mata kansa alamar kar tai kuka. Dan tun tsawar da Abban yay mata duk hankalinsu ya dawo kansu.

     Suma koda suka gaishesa bai amsa musu ba. Sai faman mazurai yakeyi. Basu sakebi takansaba duk suka kwashi kayayyakinsu sunama Ummi sai sun dawo. Itako amsa musu take da fara’a tamkar batasan da zaman Abban a wajenba ma.

        Yah Muhammad ne ya kama hannun Hibbah da ko motsi ta kasayi har yanzun. Sai da sukazo har wajen motarsa yasa handkerchief ya share mata hawayenta batare daya ce komaiba. Sauran ƴan uwansa ma kuma bai basu damar cewa komai ɗin ba. Sai umarnin yin addu’ar fita gida kamar yanda suka saba yay musu. 

      Suna kammalawa kowa ya hau abin hawansa. Yah Muhammad da Hibbah. Abubakar ya ɗauka Usman da Umar a motarsa dansu basu da mota har yanzu sai mashina. Ammar ma ya hau mashin ɗinsa lifan shi kaɗai tunda yau Hibbah tabi babban yaya………..✍

_BONANZA, BONANZA, BONANZA 20% OFF ZAFAFA PAID BOOKS, OFFER ENDS ON 31st DEC 12AM INSHA ALLAH!_

_ASSALAMU ALAIKUM!!_

_ZUWAGA MASOYA, KUMA MAKARANTA LITTATTAFAN ZAFAFA BIYAR._

_KORAFI YA KARBU, DAGA YAU LARABA 29 GA WATAN DECEMBER IN SHAA ALLAH, ZUWA 31 GA DECEMBER RANAR JUMU’AH KENAN. BISAGA KORAFI DA NEMAN RAGE KUDIN ZAFAFA NA DUBU DAYA KAN LITTAFAN BIYAR, IN SHAA ALLAHU, KORAFIN KU YA ISA GARE MU. KUMA MUN AMINCE. ZAMU KARBI 800 GA LITTAFAI BIYAR DIN DA KUKE BUKATA, A MAIMAKON DUBU DAYA NA BOOKS BIYAR. YAU LARABA ZUWA JUMU’AH KARSHEN WATAN DECEMBER KENAN. ZAMU RUFE KARBAR 800 KUDIN ZAI KOMA DUBU DAYA KARFE 12 NA DAREN RANAR JUMU’AH INSHA ALLAH._

_GA WATAN JANAIRU (3st JANUARY, ZAMU CIGABA DA KARBAR DUBU DAYA KAN LITTAFAN BIYAR._

_A KUMA 1 JANUARY DINNE IDAN ALLAH YA KAI MU, ZAMU FARA SAKIN PAGES DIN LITTAFAN NA KUDI, WATO PAID PAGES????????????????NA BOOKS DIN._

_LITTATTAFAN SUNE: *DABI’AR ZUCIYA (FALL IN LOVE)* NA SAFIYYAH HUGUMA_

_*HALIN GIRMA (GLAMOROUS LOVE)* NA HAFSAT RANO_

_*DEEN MARSHALL: (INTENSE LOVE)* NA MAMUH GEE_

_*SO DA ZUCIYA (A LOVE SO BEAUTIFUL)* NA: NANA HAFSAT MSS XOXO_

_*TAKUN SAAKA(LOVE IN TIME)* NA: BILLYN ABDULL._

_KAI DAGA JIN SUNAYEN KASAN ZA’A SHA GWAGWARMAYA A KUMA KARU DA DARUSSAN DA ZASU KOYAR, NA FADAKARWA DA NISHADANTAR WA HADI DA TACACCIYAR KAUNA MARAR GAURAYE_

_DOMIN KASANCEWA CIKIN MABIYA LITTAFAN ZAFAFAN SAI A TUNTUBE MU TA.????????_

*_WAIWAYE……ADON TAFIYA inji masu salon iya magana_*

*ZAFAFANKU BIYAR ????????????????sune suka sake dawo muku da wasu nau’in QAWATATTU kuma TSARARRUN LABARAN,masu dauke da SABBIN JIGO na MABANBANTAN LABARAI masu tsuma ZUCIYA*

*_SANIN HALI…..yafi sanin kama,indai kasan TAFIYAR ZAFAFA babu dana sani ko nadama cikin zuba kudi wajen siyan litattafansu,koda jin sunan ma kasan cewa tafiyar ta dabance_*

*GWADA IDAN BAKI TABA BA!!!,HAUSAWA SUKACE SAI AN GWADA AKAN SAN NA ƘWARAI,burinmu kowa ya shigo cikin tafiyar a dama dashi*

*JERIN SABABBIN LITATTAFAN NASU NA WANNAN KARON SUNE*

*_DEEN MARSHALL???????? Mamuhghee_*

*_HALIN GIRMA????????hafsat rano_*

*_TAKUN SAƘA????????billyn abdul_*

*_SO DA ZUCIYA????????miss xoxo_*

*_ƊABI’AR ZUCIYA????????huguma_*

*DUKKAN WADAN NAN LITATTAFAN ƊAI ƊAI HAR BIYAR…ZAKU SAMESU AKAN KUDI NAIRA 1K KACAL*

2????????400

3????????500

4????????700

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21 22 23Next page

Related Articles

Leave a Reply

Back to top button