NOVELSUncategorized

WA ZAI FURTA 20

???? *WA ZAI FURTA?*????
              2⃣0⃣
*Gargadi* Bana son ana rubuta mun komai a page din dana tura. Naga 1⃣9⃣ wat t rubuta *Anzo wurin* bana so. Duk wacce ta Kara taba mun page daga ranar *Wallahi wazai furta ya Kare*

  Labarin Nan saboda soyayyar makarantar ne nake rubuta tashi na fada don ku nakeyi to a daure a karbi iya abinda aka gani.
  Sannan masu cewa na Sanya sunan su a page ku sani cewa wallahi idan dambu yayi yawa bayajin Mai. Duk yanda kuke Sona wallahi nafiku. Akan KU nakan hana kaina abubuwa da yawa don kada na Bata muku. Dan Allah a bani uzuri. Ina kaunar duk Wanda ke Sona ko wanene wallahi bana Raina masoya.????????????????????????????

Tsoron Corona yasa har yau na kasa lekawa RIGASA KADUNA????

  

*Tukuici ne ga Aunty Rabi ( Hajia Rabi badawi Kano maman Ibrahim ), Allah ya Kara arziki ya shirya Miki zuri’a ya Kara Miki tsawon kwana. Amin.*


*KINA RAINA MAMAN WEEDAD*

*Domin ki…… beloved sister Khadija Dahiru wowo miji na gari I pray*

????????????????????  *RUKAYYA BAKO DAN BATTA I love you so much, remember this always*????????????.

       ****************

*Federal University dutsinma*

……..Ta rude ta kidime Ni kake Kora….. Ya bude mota da karfi ya fita ya zagayo ya bude kofar bayan….get out I said are you dumb? 
    Kwalla suka zubo Mata sharrrr…… Ta sauko a hankali. Suleiman na gefe yaga ta fito.
  Ya koma gefe ya tsaya, tana fita ya maida kofar da karfi gammmm. Ta kalleshi da sauri, ya banka mata harara am I safe now??? Idanun sa sunyi jawur duk sun kawo ruwan masifa.
   Ta kawar da Kai ta nufi wurin driver ya finciko ta da karfi kada ki shigar mun mota…… Zan dauki plate ne ta fada kwallah naci gaba da shatatowa…..ya ingijeta ya kwaso plates din watso kasa….ya kalleta Yana zare ido you can go now!!!!!!…….. Anwar duk akan Suleiman……. Ya doka tsoki ya juya zai fada mota, wata zuciya ta debeta Bata San lokacin da ta fizgo rigarsa ba ya dawo da karfi…… Kai har ka iya kamun irin wannan wulakancin in kyaleka??…….. Ya zaro ido. Suleiman dake kallon su shima fiddo nashi……. Ya daskare ya sankame tare da tsareta da jajayen idanun sa…..Wai me yasa yarinyar nan bata tsoro na.????
……… Kwallah kwance cikin idanun ta, ta turashi da karfi bayanta ya daki murfin mota tayi kansa kamar zata matseshi duk ta fita hayyacinta……… Na rokeka kazo Nan????
Ya yunkura zai dawo ta mayar dashi da karfi wasu zasu wuce suka Dan tsaya kamar zasu fahimci wani Abu, hakan yasa Shi kasa biye Mata kada su Tara jama’a…….. Na ce kiranka nayi kazo??????
Matsa Bilkisu in wuce….. Ta galla mishi harara sannan ta juya kadan ta kalli inda ya watsar plates din ta ce “`dauko su day hanmunka“` …… Ya kalleta da sauri….. Wallahi tallahi ka dauko su ka Miko mun da hannunka ko Kuma nida Kai har abada mun rabu daga Nan…… Gabansa ya Fadi… Ya Kara kallonta.
  Ta matsa nesa dashi ta tsaya tare da rungume hannuwa….. Kaka kara Kaka…ya yi shiruuuu….. Ban tilasta maka ba, kana iya shiga mota ka tafi, wacce ka koreni cikinta kana ikirarin *motar ka*…….. Ya runtse ido, taci gaba da cewa Amma ka sani na fita motarka salin alin wallahi Alan plates din nan Zan rabu dakai rabuwa ta har abada…….. Ya Kara runtse ido tamau.
  In ba rainin wayo ba, Kai har yau baka ganin kowa da mutunci kana iya cin mutuncin kowa baka shakkar……kawai taga ya dauko plates din ya Miko mata. Fuskar sa murtuk……. Ta karba ta juya…… Kizo ki dauki maganin…… Bana so *jikan karuna*….. Ka hada da maganin da motar ka cinye nafi karfin dukiyarka da wulakancin ka Anwar…… Ya fizgota da karfi, Ni kike gayawa magana????…….. Ta fincike an fada maka ta nuna Shi da yatsa wallahi Ka Kuma taba ni Zan sharara maka Mari……. Ya zaro ido what?????
Ta kalleshi shekeke….kafi karfin hakan ne? To idan kana musu ka jaraba… mtsewww ta buga tsoki ta juya…..ya tari gabanta da sauri….
 Wai ke da me kike takama ne? Ya fada da karfi….. Lokacin ne Suleiman ya karaso.
…… Anwar meke faruwa ne……  Ji kakeyi tasssssssss ya ramtse Shi da Mari….. Ya kidime ya gigice….. Bilkisu ta ja baya da sauri tare da daura hannu aka…… Yana dagowa ya daga hannu zai Rama ya Kara wanka mishi biyu double one after another…..sai jini ta hanci……… Bilkisu ta kwada ihu zata ruga ya janyota da karfi ta dawo kanta ya daki kirjinta…….. Gashi na taba ki , Kuma na Mari wannan Dan iskan sai ki Rama mishi Kuma ki hukuntani da wani Marin Wanda Kika mun…… Ta zukunna kasa ta fashe da kuka …. Ya kalli Suleiman ko bar nan ko na halaka ka……. Suleiman Dan Allah tafi….. Dan girman Allah Suleiman tafi….. Sai nanatawa takeyi tana kuka, yasa habar rigarsa ya toshe hancin ya wuce kawai Yana huci,…  ya fizgi Wayarta ya Kira Aisha….. Anwar ne fito ina waje……
    Cikin hanzari ta fito, ganin Bilkisu duke tana kuka yasa ta rikice wata kila ya Mata halin nasa..
      Ya fiddo kwalin maganin ungo kije Mata dashi ciki, ko soke soken wuka mukayi hakan bazai shafi neman lafiyarta ba…….. Bana so Ina ruwanka da lafiyata??? Aisha bar mishi tsiyarsa bana so, ta rushe da kuka…….. Kin dai ga halin kawarki ko? Kiyi Mata fada…….. Haihuwata tayi da zata mun fada?
   Wai me ya faru Bilkisu??? Aisha ta bukata cikin damuwa……. Wai daga Suleiman ya kirani a waya fa, Ina abinda ya dameshi da wayata Ashe Yana son yace mun yazo ne …… Uban me yazo yi?…….. Kai me ya kawo ka? Ta daka mishi tsawa….. Ta kalli Aisha Kinga Marin da yayi mishi ya fasa mishi hanci…….. Innalillahi yaushe? Aisha ta fada a rude. Yanzu Mana, 
Ya buga tsoki, idan Baki ja mishi kunne yayi nesa da ke ba wallahi Zaki janyo mishi nasifa da bala’in……. Kai a wa? Ta Mike tare da rike kugu….. Ya kalli Aisha Kinga irin action dinta da mood ko? To a duk lokacin da wancen Dan iskan….. Ka daina zagin sa wallahi….. na ce mishi Dan iska ko Zaki Rama mishi?…….. Don darajar Allah kuyi hakuri……… Bilkisu ta buga tsoki ta juya kawai ya fincikota da karfi…….. Ta kuwa Kama hannunsa ta gantsara mishi cizo da karfi…..ya saketa da sauri Yana fadin Kai Kai Kai Kai, ta kwashi kasa ta watsa mishi a jiki sannan ta kwasa da gudu tayi ciki…….. Tana shiga daki ta Sanya sakata ta ciki……. Ya biyota a guje, kafin ya karaso ta garkame……..Aisha ta rude ta rikice gidan ya harmutse Jin irin hargagin da yakeyi akan ta bude….. Wallahi zan karya kofar nan ki bude kizo ki fada mun dalilin watsan kasa…… Ban budewa…….har daya yayi ma kofar ta fada ciki tayi tsalle ta Haye katifa ganin zata bigeta…….. Aisha ta Fara rokonsa yayi hakuri ita Kuma ta makure ta Fara ihu tana kuka…….. Ni Zaki watsa ma kasa saboda wancen Dan iskan…….. Wallahi ba saboda Shi ba……. Ya sungumeta a kafada yayo waje Aisha da sauran mutane suka biyo su……. Ya juya duk shegiyar data fito sai na karya ta. Aisha zo muje…….. Ko wace tayi dakinta tana surutai……… Kafin kace kwabo magana har kunnen mufeeda.
Ya direta jikin mota ya kalli Aisha tambaye mun ita dalilin watsan kasa…….Dan Allah kayi hakuri Anwar.
Kika kawai Bilkisu keyi……
 Ya kalleta ke kina da gadara da taurin Kai ko? Kina tunanin duk wannan abun ba shine Kika janyo wa fitina ba?…… Dan Allah kayi hakuri Anwar. Aisha ta Kara fada.
Aisha na fadawa Yarinyar Nan bana son yaron can me yasa bazata kyaleshi ba?…….Akan wane dalili Zan kyaleshi Kai meye naka aciki da zaka hanani mu’a mala da wani?…..saboda….. Sai Kuma yayi shiru.
Saboda me?
To baka Isa ba, Yanzu na Fara kula Suleiman…… Kinji ko Aysha? Kinji abinda take fada ko?
    Dan Allah kayi hakuri Anwar zata daina kulashi…….. Yaudarar ka zatayi, ba Wanda ya Isa ya rabani da Suleiman Kuma ka sani daga yau bani bakai, bana son abotar kaje ka nemi wata idan na Kara ganin ka anan ko kamun waya Kai ko tunani na kayi a zuciya ban yafe………. Ya buge Mata Baki.
Ke kin Isa ki yanka mun doka?
Ta rike bakin tare da runtse ido…… Ya kalli Aisha kina Jin halin kawarki ko? Duk garin nan akwai yarinyar dake mun haka?
Ta girgiza Kai da sauri Babu kayi hakuri…..
   Idan kin lura ta na nemana da rigima sosai……
     Kayi zuciya ka kyaleni daga yau a fita harkar Bilkisu….. It’s alright take care, Kawai ya fada mota yaja ya tafi …. Gabanta yayi mummunan faduwa, ta yi shiruuuuu kafin Ta figi hannun Aisha zo muje.
Suna zuwa daki ta fada katifa ta saki kuka…. Ai kinyi kuskure me yasa zakiyi mishi irin wannan wulakancin Bilkisu…… Ta dago fuska jage jage da hawaye…. Aisha na rasa gane inda Anwar ya dosa, masifar nan tashi ta isheni gara ya kyaleni na huta…. Wallahi bazaki huta ba. Ta Kara kallon ta da sauri, yes bazaki taba hutawa ba saboda kina matukar kaunarsa…. Bilkisu nasanki nasan wacece ke, gwargwado nasan waye Anwar shima wallahi tallahi matukar baku fito Kun fadawa junanku surrin da ke zukatanku ba tabbas zaku kashe kanku a banza…… Ni na taba ganin jarababbiyar soyayya irin taku?
Ko wane idan kishin Dan uwansa ya motsa sai ya Kare kansa?…… Ta kife Kai a filo …ta Kara sakin kuka a hankali…….
Idan kin gama ki tashi kiyi parking, ga maganin nan na dauki kwaki goma …. Ta fice jikinta duk ya mutu tana mamakin irin wannan soyayya wacce ko a littafi Bata taba karanta irin ta ba.
    Gaban sadeeq ya Fadi……. Anwar lafiya na ganka a firgice haka ko jikin……. Tashi ka shirya mu tafi Kano.
What?
 Ya mishi wani kallo gaban Sadeeq ya Fadi ya tsorata Anwar lafiya?
Zaka je ko na tafi?
Ya kamo Shi ……ya fizge sadeeq Dan Allah ka kyaleni *I hate this world*…….. Ya ci gaba da harhada Kaya…… Dole sadeeq ya Mike shima ya Fara hada jaka….. Amma wallahi bazaka tuka mu cikin wannan mood din ba … Bai rufe Baki ba ya wurga mishi keys din a kirji ya figi jakar sa yayi waje….. sadeeq ya bishi da gudu tare da rufe dakin….Sha biyu da Rabi na dare suka bar dutsinma yana kwance a sit ya Dora kafa daya a dash board ya kwantar da sit yayi filo da hannayen sa idanun sa rufe….. Kadan kadan sadeeq na lura dashi sai faman tsoki yakeyi.
   Batayi tunanin abin zai dameta ba sai da ta koma gida, kwana daya , biyu…sati. Anwar bai nemeta ba.
Suleiman kuwa yayi Kiran duniya ta kasa dauka kamar tana son Jin haushin sa ganin shine jigon wannan fitina.
  Gaba daya gidan an ga canjinta, bata walwala, kullum tana daki kwance.
  Ranar da tayi sati biyu da dawowa mommy ta sameta daki, ta zauna bakin gado, Bilkisu mi ke damunki? Na lura tunda Kika dawo Baki da walwala, meke damunki? Saboda har dadyn ki ya Kai ga yin magana…… Ko maganin da Kika ce Anwar ya siya Miki ne kike ganin yayi yawa?….sai kawai taga kwallah na zubo Mata…. Hankalin momy ya tashi ko dai daukar magana Yar tata taje……subhanallah. tayi saurin kawar da tunanin. Ta janyota fada mun menene?
Ta goge hawayen mommy bana Jin dadin abinda Anwar keyi mun…… Ta Bata labarin duk abinda ya faru….. Sai kawai taga mommy na dariya.
  To Bilkisu Anwar ai kishi ne ke damunsa tunda baya son ki kula Suleiman din sai ki kyaleshi….
Ina wayar ki?
Ta Mika Mata kawai….. A’a Anwar din Zaki Kira kice yayi hakuri tunda ke kin damu bai Kira ba….. Tabbb wallahi bazan kirashi ba mommy….. To ya Zama dole ki fitar dashi a Ranki domin Shi da alama ya manta da ke kamar yanda Kika mishi gargadi…… Kirjinta ya buga da karfi kwallah suka Kara cika idonta …mommy ta mike wannan shine sai ki zabi daya cikin biyu, Amma bazan dauki wannan dararewar ba da kikeyi cikin gidan Nan… Tana Gama fada ta fice tare da Jan kofa  gammmm.

   Tayi zugummm, dabara ta fado Mata kawai Bari ta Kira Sadeeq……
      Anwar kuwa yafi Bilkisu shiga tashin hankali, ya koma kurman karfi da yaji, hankalin Hajiya yayi mummunan tashi tana zargin ASIRI ne ke son kamashi.
    Ita kadai ke shiga dakin sa sai kuwa sadeeq, kullum sai ta lallasheshi yake cin abinci….
  Abun har ya Fara affecting kasuwar sa, kowa shakkar kiransa yakeyi a waya saboda masifa da bala’i.
   Tana zaune ta tsareshi ya shanye tea  din ta Sha mur alamar ba wasa kamar kullum, ya Sha mur, ya tsuke fuska rabonsa da dariya tun ranar da ya rabu da Bilkisu Yana cusa kwai a Baki jinsa yakeyi kamar madaci.
  ……. Sadeeq ne ya turo kofa Assalamu alaikum.
Hajiya yau kina ciki?
Eh sadeeq maraba, Wa’alaikumus Salam.
   Kamar zatayi kuka ta kalli sadeeq na rasa ainahin meke damun Anwar, shin ko ta sanar dakai ……ya wurga mishi harara Yana horonsa da ido kamar kullum akan kada yace wani Abu…… Hajiya ina ga malaria ce, kin San fa dutsinma akwai sauro sosai Daman ya Saba duk hutu sai ya kwanta ….. Ba irin wannan kwanciyar ba. Yaro ya takure ya makure sammm Anwar ko murmushi ya daina yi…… Zai dawo normal hajia aci gaba da addu’a.
     Ta Mike , kaima ai bakin ku daya, ko ma menene bazan yarda da wasa da abinci ba… Ta fita.
   Ya kalleshi …ya kamata ko don tsohuwar nan ka daina wannan abun, nasan wallahi duk wannan damuwar Bilkisu ce… Ta kirani dazun ta fada mun duk abinda ya faru hada kukanta, ta ce wallahi Babu abinda ke tsakanin ta da Suleiman, Anwar hakuri akeyi….. Please sadeeq ka kyaleni….. Bazan kyaleka ba tunda kaima baka kyale kanka ba .
  Ta ce na baka hakuri….bazanyi ba tace na Kyaleta hakurin me zata bani?….. Har wannan maganar ta fada mun ta ce kuskure ne bacin Rai yasa ta Fadi hakan….. Karya takeyi. Tana son bani haushi ne don na Mari Suleiman…… Wannan zafin kishin naka bazai taba sany…. Kishin ubanwa zanyi? Ya Mike ….ya kamoshi da karfi ya mayar…. Dan Allah kayi hakuri Anwar tunda wallahi Koda mukayi ways kuka takeyi….. Kaine zata Kira taba hakuri ba ni ba? Tunda Kaine tayi wa laifi ko?
Ikon Allah…. Tana tsoron kada ku Kara  wani fadan ko kaki dauka ……. Ni zaka zo ka tsara sadeeq??? 
Tsari??? Wallahi da gaske nake ita ce ta kirani….ya fiddo waya aljihu…duba ka gani ni na Kira ko ita? Minti nawa ka gani?
  Sai kawai yayi murmushi ko kadan bai San yayi ba…..ya zaro ido are you smiling????? 
Ya Kai mishi duka ya goce….. Munafuki ni na dade da sanin wannan cutar taka Bilkisu ce…. Dan Allah fada mun tayi maganar cikin damuwa?
   Wallahi kuka takeyi lokacin da muna  maganar alamar abun ya dameta…… Mtseww ita ce ke Sanya mu damuwa ai….. Iye? Sadeeq ya fada , ya banka mishi harara Yanzu dai kirata kace ta kirani da kanta ta bani hakuri….. Message ya shiga wayar Anwar din karammm….. Ya dauko da sauri jin alamar shigowar  message din ta ne,
“`I’m sorry very sorry please and I don’t mean to hurt you“`….. Sai kawai ya washe fuska…. Sadeeq Bilkisu ce….
   Dan Allah Kira mun ita…. Suna Kira wayar a kashe. Abu kamar wasa kusan kwana uku duk lokacin da aka Kira a kashe….. Shi kansa ya nema Amma bai Samu ba…. Hajiya dai taga Anwar lokaci guda an warware har Yana fita tawon *Bike* da suke zuwa da marece Shi da yaran governor.
  Ta warware amma duk ta Dan rame kadan….. Kullum tunanin Anwar. 
  Ta kasa bude wayar ta saboda tana Jin kunyar idan ya Kira me zata fada mishi bayan ita ce ta bayar da hakuri?
    Ta Kama lahadi suna gida duka har daddy, tana sanye da Riga da skirt na atamfa super Holland Mai flower yellow dinkin ya bi jikinta, dogon hannu ne na *net* yellow duk atamfar yayyabe flowers din suke da stones masu sheki kamar diamond.
  Kanta ba kallabi ta maida gashinta baya ta kulle jelar kwance bisa bayanta….. Motsin get suka jiyo. Daddy ya Mike da sauri ya daga labule….jibga jibgan motoci ne bakake suke shigowa…. Ya ce innalillahi.. waye zai bamu surprise visit Haka?.. aka Fara fitowa yaga securities ko wane da abin magana a kunnensa ya saki labule da sauri, ya kallesu inajin foreign affairs minister ne ….. Yayi ciki da sauri..
 Suka tashi duk suka fada daki. Bilkisu ma ta shige nata.
 Ya fito Yana gyara hula, falon kamshi kawai ke tashi na freshner ta ko Ina …. Ga A.C ta gauraye ko’ina…. Ring bell ya Fara kadawa a hankali… Da daddy da kansa ya bude….. Ya bude ido sosai cike da mamaki compound din gidan makil da securities suna tsaye ya Sha fararr gizna dinkin falmara ce yasha aiki kansa cikin kube murjin kanawa…… *Waye in ba Anwar ba*……. Anwar??? Daddy ya fada ….sukayi saurin zubewa shida Sadeeq daddy Barka da yammaci…… Ku tashi …. ku tashi…. Ya kamo Anwar…. Ya riko hannun sa suka shigo ya kwadawa mommy Kira ta fito da sauri…. Tayi turus ganin Anwar tare da washe Baki *Anwar a gidan mu*?
 Sai sumke Kai yakeyi…. Daddy ya zauna suka gaisa sosai ya kasa hada ido dashi sai sadeeq ne ke faman amsawa .
 Tuni mommy tayi ciki tasa Rahina Mai aiki ta fara kawo musu abin Sha….
 Daddy ya Mike ya haye sama.
  Mommy ta shigo suka Kara gaisawa ta koma ciki….  ya kalli sadeeq Dan ubanka ka tamabaya kace Ina Bilkisu?????…… Ya zaro ido ya Kai mishi duka……
  Tana kwance ta kunna t.v din ta tana kallon wani Korea series *Innocent man*
Mommy ta shigo, ke kullum idan anyi Baki sai  ance kizo ki gaishesu??? Tayi zumbur Ina da niyya mommy ayi hakuri….. Ta galla Mata harara…. Tabbas kowa yasan surprise visit ya Bata don me zata fada Mata…. Gara ta fita idanunta su gane Mata.
  Ta dauki dan mitsilin gyale ta Yana a fuska bai ko rufe rufe rabin gashinta dake kwance a baya ba….. Ta raba momyn ta wuce ..
   Assalamu alai…….. Ya dago da sauri sukayi tozali…. Sai kawai ta dafe kirji tayi baya da sauri kamar wacce taji tsoro , mommy na tsaye bakin kofar dakinta Bata fita ba…. Ta ruga ta makalkaleta….. Mommy da gaske Anwar ne?………✍????


*Zainab wowo*????

Related Articles

Leave a Reply

Back to top button