NOVELSWASA FARIN GIRKI COMPLETE HAUSA NOVEL

WASA FARIN GIRKI COMPLETE HAUSA NOVEL

WASA FARIN GOIRKI COMPLETE HAUSA NOVEL

????sameemah a madubin gani????

Ina kallonsa lokacin daya fita,haka kawai na tsinci kaina dajin haushin yanda bai tambayi dalili ba saima kokarin gani laifina dayake yi,nasan a halin danake ciki da zuciyar mace ce dani da saina rushe da kuka,saidai babu yamda zanyi saidai na hadiye bakincikina kawai.
Bai dade da fita ba wani yah shigo da abinci a hannunsa a wani kwano irinna bawa dabbobi abinci.
Ina kallonsa har yah ajiye abincin,maimakon yah fita sai yah matso kusa dani yana tanɗe baki,hmmm maza wani lokacin suna bani mamaki dole sai mutum yasakawa ransa taba abinda ba nasa ba.
Hannunsa yah miko har yakusa taba cinyah ta na kalleshi.
“Karka kuskura wannan kazamin hannunaka ya taba cinyata in kanason zama da lafiyarka,idan kuma ba haka na ka gwada”
Baiji gargadin danayi masa ba sai ma kara matso da hannunsa dayake kokarin yi.
Shiru nayi masa har yakai hannunsa yagama shafa cinyata kafin yah dauke,
“Yanzu kaji dadi daka taba cinyata koh?,saidai inaso na sanar maka cewa,bazaka kara yin komai da hannunba,domin babu abinda zaiso hannunka yah karisa kusa da shi ko kuma abinsa “
Ina gama fadin hakan na kalli hannunsa wanda shima hannun yake kallo.
Wasu kurajene suke bullowa daga hannunnasa cikin kankanin lokaci,ihu yafara yana jijjiga hannun,yayinda nikuma nake Murmushi da ganinsa cikin yanayin hakan.
Fita yayi da sauri yana ihu,saidai bashida ikon fadan abinda na aikata masa,sannan duk maganin da zayyi bazai warke ba.
A haka na cigaba da zama a cikin wajwn badan bazan iyah fitaba sai dan ban ra’ayin hakan,masu yimin bulala goma kuwa kullum sai sunzo sun yimin da safe kafin su tafi.
Yanayin halittar da jikina yake nunawa kullum kara gaba yakeyi,dan yanzu ina iya control din warkewar da ciwon dayake jikina zayyi,sai sun gama yimin dukan da ransu yakeso,nikuma sai na bari idan sun fita saina sake jikina wajen ya koma yamda yake,sannan nakan jiyo hayaninyar mutane daga nesa,sannan kullum inajin muryoyin wasu halittu suna kara yawa a cikin kokon raina.
Yaseer kuwa ko yaushe yakan zo yah fadamin halin da karnukana suke cikin,watarana yacemin reza ta haifi ƴaƴa guda hudu,biyu sun mutu saura biyu,sannan itama ta mutu,tabbas naji haushin hakan amma raina bai baciba kaman yamda akayi mata wannan duian,saboda yanzu zuciyata ta saba da rashin wanda ta fiso,tunda ummah ta ta rasu na rayu to zan iyah rasa kowama a duniya ta.
Duk da bandamu da mutuwarta ba saidai kuma wata zuciyar tana cin na fita kodan na yiwa ƴaƴan ta rainbow da duk cikin barrack dinnan babu wani kare da akayiwa irin horon.
Can cikin darene na fara jin karar mota tun daga get dinner farko na shigowa wajen,daga yanda motar take tafiyah,sannan kuma da karar bindiga danaji yatabbatarmin da koma wanene bada zaman lafiyah ya zoba.
Waigawa gefena nayi naga babu kowa,shikansa mai gadin bakin kofar bacci yake irin mai nauyinnan,dan yacika wajen da minshari shi kadai.
Duba sarkar dake hannuna nayi domin gano inda zan cinke ta,zuwa yanzu na fara jin hayaniyar mutane da kuma harbin bindiga,duk mutanen da zasu shigo har cikin barrack su kawo hari gaskiyah abin ba karami bane dan harda kukan yara da mata nakeji.
Zan salary hannuna nayi saida ta cinke da karfin gaske,nufar bakin kofar nayi na balle ta,ban damu da tashin mai gadinba kawai bindigar da take gefensa na dauka,sai a sannan yatashi yana dawurwuri cikin yanayin gaga’a.
Kasan bindigar na kwada masa a Kansas yah koma baccin dole wato suma,saboda idan na tsaya batamin lokaci zayyi.
Gyara zaman bindigar nayi na fita da sauri,babu kowa a hanyar danake da alamar duk duna gidansu,tafiya nake cikin sanda har nashiga ainihin cikin bori camp inda yawancin gidajen ƙanannan sojoji yake,da kuma ɗaliban da suka karatu a army acadamy .
Hasken fitilar mutanen na fara gani daga dan nesa kadan,har nayi niyyar karisawa saikuma na koma zuwa gidan major Nazeer wanda shine akabawa oder kamani kuma shine babba a yanzu tunda sauran basanan duka.
Kallon rigar jikina nayi wanda bazata yimin dadin tafiya ba a haka,domin riga tace ta bacci tun wanda aka kaini cikin cell din da ita.
Kamata nayi na yage kasan ta ya zamo bata gi iyah gwiwa ta ba,sauran kuma na daure a kunkumina,gyara zaman bindigar nayi na nufi hanyar headquarter inda gidan mu muma yake,tum daha bakin kofar na gano wani mutum sanye da bakin kaya rike da bindiga a hannunsa,hakanne ya tabbatarmin da cewa suna cikin wajen basu fita ba.
Tafiyar nake a jikin inuwar dare cikin kwarewata a fannin sanɗa,har na kariso inda yake bai saniba,sai jin dukan bindiga da yayi a kansa,saurin murde masa wuyah irin wanda bazai mutuba amma kuma zai iya yin sati a kwance bai tashi ba.
Shiga nayi cikin harabar wajen babu alamar tsoro a tattare dani,dannasan duk cikinsu babu mai iya ja dani,saidai idan da ayar Qur’an yake tafe,amma bada bingida ba kam.
A hangar shigata cikin gidan ma saida na hadu da wani a bakin kofa,shikam ya kulada zuwana saboda babu damar na bi ta bayansa a yamda yake tsaye,kokuwa muka fara na bugashi da jikin tiles din wajen, haka na barshi dan baya bukatar karya wuya tunda kashin bayansa yah karye.
Sashen gidanmu babu haske ko kadan saboda ba kowa a ciki,iyah sashen major nazeer ne kawai da wuta,itama ba sosai ba dan daki dayane kawai yake da wutar.
Hanyar gidan na nufah cikin tafiyah na mai yin fako,ban hadu da kowa ba tun daga wancan guda biyun har na je kusa da gidannasa.
Wani window nasamu mai matsakaicin girma,a fuska bazai isa na wiceba,amma tunda nayi kaurin suna wajen iyah shiga gidan mutane na yashe kudi a baya wanann bazai bani wahala ba.
Ina dira cikin wajen naga ashe kitchen ne inda na shigo.ƙoƙarin bude ƙofar na fara cikin dabara yamda baza’a gane ba ko jin motsin hakan.
Cikin sa’a kuwa ƙofar bata da kara,har na fito daga kitchen din babu wanda ya ji,wani corridor na bi wanda zai kaini inda nakejin hayaniyar,dan sake dukkma karfin ji na kunnena nayi domim gano ta ina numfashi yake fitowa da kuma motsi ko bugun zuciyah,dan a cikin satinnan kunne yafara daukomin sautin bugun zuciyar duk wani abu mai rai dayazo wucewa ta kusa dani.
Dakin da na hango da haske a cikin sa lokacin ina waje,ta nan nake jiyo alamun rayukan mutane a ciki.
Window dakin na fara lekawa dan ganin mai yake faruwa a ciki,yara ne mata guda biyu bazasu wuce shekara sha biyu zuwa sha biyarba,dukkan su wasu mutane sun saka musu bindiga a kunne,da alamun wani abu suke nema,sannan kuma da yaran sukeyiwa major nazeer barazana,dan yana gefe yayi kneel down idonsa yayi jawur,matarsa kuma tana gefensa said sheshshekar kuka takeyi.
Kofar wajen na nufah ina gyara rikon bindigar dake hannuna.
Saida na saita tukunna kafin na afka cikin dakin da karfi cikin zafin nama wanda na dade banyi aiki da shiba.

Lambar asusu:3131951977
Lambar waya:09035784150

Dan allah karki karanta koh karka karanta baka biyah kuɗin ba,domin akwai hakkina na naira jaka ɗaya(200) a kaknka koh akanki idan baki biyaba kike koh kake karantawa.

????Sadi-Sakhna________✍????????

(¯’•.¸,¤°’✿.。.:քʀօʄɨƈɨɛռȶ աʀɨȶɛʀֆ.:。.✿’°¤,¸.•‘¯)

????•°• WASA FARIN GIRKI •°•???? {cigaban gidan gandu}

????21~22????

Ina Shiga ban Bata lokaci ba na saita bindigata a kan ogannasu wanda yake zaune a bakin gado yah rude fuskarsa da wani bakin kyalle,kallonsu nayi ina cewa,
“Koh Ku dauke bindigarku daga kan yarannan ko kuma yamzu ku debi kwakwalwarsa a kasa”
Har sunyi niyyar ajiye bindigarsu naji yah buge bindigar dake hannuna da karfi yah rike wuyana tareda manna ni da bangon dakin dayake kusanmu,matsewar dayayimin nasan da ni mutumce kaman saura da idan ban mutuba toh zan shiga coma,
“Ke yar gida uban waye da namiji bazai iyah tunkara ta ba bare ke figyagygyiya dake?”
Muryarsa kadai ta isa ta bawa mutum tsoro yanda take fidda amo,murmushi nayi masa kafin nace,
“niba yar uban kowa bace saboda ba da matsayin uban kowa nake taka rawata ba,sannan babu mai sakani koh hanani sai na ga dama”
Nima nasa wuyan narike kaman yanda na rike nawa,wani yunkuri nayi muka juyah yazamo shine a jikin bangon ina rike da wuyansa sabanin da shine yake rike da nawa wuyan.
Kakarin amai yake yanda na rike masa maƙogaro a hannuna gam,kallon idonsa nake wanda yayi ja saboda rikona,
“Yanzu waye figyagygye tsakanin ni dakai,bar raina allura karfece
Saida na tabbatar yayi laushi kafin na jefar dashi a tsakar dakin,kallon wanda suka dora bindiga akan yaran nayi amma sai suka kara manna bindigar jikinsu yah fara karkarwa,barazana suke min amma ban fasa isa inda sukeba,har saida dayah yah fara nuna ni da bindigar,banyi tunanin zai harba ba amma saijin karar shigar bullet nayi a kafada ta ta hagun.
Karar iskar shigarsa ce tasa na fada can gefe sannna na bugu da gado,gsnin hakanne yasa ogan yayi saurin tashi yana rike da makogaransa suka fice da sauri tareda sauran yarannsa,matarce tayi saurin matsowa kusadani amma na dakatar da itah,tareda cewa,
“Ki dauke yaranki tukunna,sune suke da bukatarki bani ba a halin yanzu”
Tashi nayi na fita daga dakin ina rike da inda aka harbenin,saidai ina fita waje na jefar da bullet din nayi hanyar gidanmu.
Shikuwa dama major nazeer tun sanda suka fita ya bi bayansu da guda lokacin da ya dauki bindigar dana shiga da itah.
Ina Shiga Gidan ban same KO inaba sai dakin sameer,dayake dama akwai key din kowanne daki a jikin na kofar shiga gidan ,wanda aka bawa kows idan ya dawo gida zai shiga.
Kunna wutar dakim nayi kafin na bude drawer kayansa,cikin sa’a kuwa na samu abinda nake nema wato kayan aikinsa,dauka nayi nasaka cikin sauri sauri,duba gefen kayannayi na dauko bindgarsa ita ma a wajen kayan amma a kasansu.
Gyara zaman bullet dinnayi,harda Murmushina danajita a cike da bullet gata kuma dama favorite ɗina kenan.
Kallon kaina nayi a madubinsa nayi murmushi danna fito sak raudah abdulsalma dina,saiya tuna min abu dayawa.
Fitowa nayi ina rataye da bindigar har haraba headquarter,anan na samu su major nazeer suna ta magana,tsitt sukayi dasuka ganni na iso wajen,musamman yanda nake tafiya kaman mamallakin kayan,tun kafin major nazeer yayi magana nace,
“Mai ake baza’abi bayansu ba har yanzu karfe hudu na asuba yah kusa”
Wani ne daga cikin sojojin yace,
“Eh wato ranki yadade ogah ne yace bazaiyiyu a bisu yanzuba saboda ba’asan mai suke dauke dashiba”
“Dole sai an bisu kuma yanzunnan,natsani naga mata suna tsoro bare maza,saboda shi iyalansa sunanan kalau ko?,na wasu ko oho,yamzu za’a bi bayansu kuma babu dawowa sai an karbo matan dasuka dauka,su basu ji tsoron zuwa daukar abinka ba sai kaine zakaji kunyar zuwa karbo naka abin”
Ina gama fadan hakan na nemi a kirawomin hackers da kuma tracker,suma zuwa sukayi gaba,hadasu nayi a mota dayah nikuma na shiga tsakiyarsu,saboda akwai wani abu danakeson yi a game da wanda suka tafin,shima major nazeer dayaga mun shiga mota mun fara tafiya sai yah hau mota suka biyimu a baya.
Wani abu na hada a system din da sauri sai ga hoton inda za’a saka yatsu yah fito.
Nawa hannun na dora sannan nayi search dinsa a area inda muka tafiya,cikin sa’a kuwa saiga hoton yatsan yah fito wanda yake wuyan shugabannasu a area wajen.
Kara gudu mukayi su major nazeer suna bin mu a baya har muka fita daga ainihin cikin mutane,wani jeji muka shiga inda hoton yake nunawa,har muka,zo inda mota bazata wuceba dole saidai mu tsaya a mushiga da kafa.
Ana zuwa wajen major nazeer yah daga hannu akan nida wanda suke tracking mu tsayah a wajen,harda ajiye mana soja guda dayah yah kulada mu,tunda nake na dade banyi dariyah ba sai a wannan lokacin,tashi daya kuma na murtuke fuska.kallona yake cike da mamaki ganin a halin da ake ciki hakan ma ina mace amma kuma bai girgijani ba.
Gyara zaman bindigar sameer nayi a hannuna kafin na wuce gaba,har shidin ma na barshi a baya na fara kutsawa cikin jejin,har yah bude baki zayyi magana nayi masa alama da yatsana akan yayi shiru kawai ya biyoni,bai yi musuba yah biyoni a baya tareda sauran sojojin, muna tafiyah muna duba inda zanen hannuna yake har muka zo bakin wani gida wanda akayi shi da ya jingar ciyawa.
A Hankali muka cigaba da sanda har muka iso bakin kofar gidan.
Wasu nayiwa alama da hannuna akan su zagaya,wasu kuma su saita taryar wanda zai fito,wasu kuma su yi shirin afakawa,a masu afakawar harda ni da kuma major nazeer,ina kallonsa yana min kallon mamaki ganin yanda nake bada umarni cikin kwarewa.
Kirga numbobi mukayi zuwa biyar kafin muka shiga da sauri.
Wayam muka gani babu kowa da alamun ansan da zuwammu.
Kara naji tana tahowar makami hakan yasa nayi saurin jan su major nazeer muka fadi a kasa,kifiyoyin kuma suka wuce a iska,kallona yake da taya akayi na sani,saidai ba lokacin tambaya bane yanzu,alamar karar mutane naji wanda idan an rufe bakin mutum take fita,nuna musu nayi tareda cewa,
“A can hanyar suke kuma ba a cikim gidannan bane saidai babu damar mu tashi tsaye saidai muyi rarrafe”
Basuyumim musuba haka muka fara rarrafawa har muka fita ta wata kofa a cikin gidan,wani jejin ne yayimana salamma irin na farko,kafin mu mike daga rarrafen muka ji karar wani abu a kawunan mu giffff,ina kallon sanda suka suma nima sai nayi suman karya domin na samu damar yin plan.
Suna ganin mun suma suka fara fitowa daga inda suke boye,ina kallon su ta gefen ido har suka kaimu wani waje inda sauran yara da matan suke.
Suna fita na bude idona, tashi nayi hannuna a daure har na isa wajen wata mace,wanda da alama tafi sauran jarumta dan ita bata kuka kaman yanda sukeyi,sunkuyawa nayi har zuwa inda igiyar dake hannunta take,wata karamar reza na fitar daga bakina na fara yanke igiyar a hankali har na yi nasarar hakan,tana ganin na kunceta ta daga hannun tana kallo,suma sauram mutanen kallon suke da mamaki.
Juya mata baya nayi da niyyar ta kwance min,cikin sauri hannunta yana rawa ta gama ciremin kafin tafara cirewa sauran mutanen da suke wajen,
Nikuwa ban dauki bindiga ba wani kulke na dauka mai fadi na nufi wajen da barayin suke.
Duk wanda muka hadu dashi saina saita murfin keyarsa nake sauke masa har muka zo inda ogan yake kwance a kan gadon kara an nannaɗe masa kai inda na bugashi a gidan major nazeer.
Kallonsa nake shima ni yake kallo da alama yagane ni,jefar da kulkennayi wanda yayi ja saboda jinin dayake jikinsa,tsalle nayi na hau kansa tareda kafa masa hakorana a wuyansa,saida na dade kafin na daga.
Murya na fara ji a cikim kaina ana shewa tareda cewa saura daya takk.
Kwata kwata na manta sai a sannnan na tuna saurana kaiwa biyu na kasance ɗaya daga cikinsu,kuma konaso zama da mutane a lokacin bazan iyaba,nadama ce ta zomin dan yanzu nasan control din danke kokarin yi zayyimin wuyah a yanzu dan a kowanne lokaci dada zama hatsari nake ga mutanen da suke kewaye dani.
Ina cikin tunaninne naji sautin tafiyar mutane,saurin goge bakina nayi tareda ture gawar mutumin daga kan gadon dan kar aga hoton hakorana a kan wuyansa.
Motocin da muka zo dasu har da na barayin muka hau domin komawa gida,kowa sai murna yake,nidai jinsu nake kawai dan na auka cikin kogon tunanin wannan juyayyar rayuwartawa.
Har muka isa na wuce gida babu wanda nakula a cikin masu yimin magana da tambayoyi dan bata su nakeba a lokacin.
Burina nayi wanka na kwanta sannan kuma nayi tunanin a wane mataki nake na rsyuwa a kusa da mutane.
Washagari da safe ko nace da hantsi dan sannan na nayi wanka na karyah saiga yaseer ya kawomin kwikwiyon da reza ta haifa,bakakene wuluk babu fari a jiknsu kuma gasu bulbul sunyi wayo,godiyah nayi masa na karbesu na kaisu garden inda iyayensu suke tun farko,dama bingone shikuwa yanzu ba zama yaje ba tunda yake zuwa wajen karen sojoji.

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21 22 23 24 25 26 27 28 29 30 31 32Next page

Related Articles

Leave a Reply

Back to top button