NOVELSUncategorized

YAR SADAKA 17&18

???????? *’YAR SADAKA..*????????


*STORY & WRITING BY…*
         *BY*
*MOMN SULTAN*


*DEDICATED TO…..*
*MMN AMATULLAH*


*SPECIAL GIFT TO…*
*DALA…..*



1⃣7⃣&1⃣8⃣


Kallan kallo aka riqayi a falon yayin da mummy ta riqajin Dakin Yana juya mata,,sedai Wani bangare na zuciyanta Yana gayamata Karya yarinyar take,,kallan mashkur nijlah tayi tana murmushi tace..
Dan birni kayi Shiru Baka Basu amsa ba,, mashkur be Iya kallan inda nijlah take ba yacigaba da qoqarin Zama Kan kujera..binshi nijlah tayi tana kallan mummy dake binta da Wani irin kallo Wanda batasan kona menene ba.
Marin da aunty ladeefah tayiwa mashkur ne ya dawo dashi Daga duniyar suman tsaye dayayi..
Dan iyayenka ba tambayanka akeba,,Yaya kaduba yadda ya maida mu mahaukata,,
Kinga lateefah abi komai a hankali shida kanshi zeyi  bayani cewan yayan Yana mamakin abinda mashkur ya aikata duk da yasan halin mahaifiyar tasu..  
Mummy Bata Iya Magana ba Dan a yadda take Bata Jin abinda suke fada kallansu kawai take sabida gaba daya komai nata ya tsaya ya Dena aiki…
Kallan aunty lateefah mashkur yayi kafin ya safke kansa kasa nan take idanunsa ya kada yayi jajur ga Wani tuquqin bakin ciki daya tokare masa zuciya,,kasa hadiye yawu yayi Yana Kallan kafet..
Lah lah lah,,Amma dai kado anyi mugu,,Babu abinda mijina yamiki Zaki mareshi,,aradu Kaci sa’a kai babbane Dana sheqeka da Sanda,,ka zube anan..
Ke Dan ubanki bamasan hauka kai mashkur ka Bude baki kayimana magana,,a Ina ka samo wannan aljanar yarinyar??
Dakyar mashkur ya Iya tsayar da nutsuwarsa ya dago kanshi dake saramasa Yana kallan yaya,,kafin ya Bude bakinsa Wanda zuwa yanzu yayi masa nauyi yace,,
Dan Allah Yaya kubani lokaci saina yi bayani Amma Daga zuwana kun tsareni da tambayoyi..
Au Allah lallai yaran nan ka samu sake yaya kake Gaya haka,,mummy kingani Duk soyayyar da Kika nuna masa ce tajamana haka,,gashi muna magana Yana mayar mana sabida be daukemu da qima ba,,aunty lateefah ta qare maganan tana huci,,mummy ko Ido ta zuba musu,,zuwa yanzu tana fatan maganan nijlah ya Zama karya Kai inda halima ace nijlah ba cikakkiyar me hankali bace..
Aunty kiyi hakuri niba haka nake nufi ba,,da hakane bazan tabajin magananku a daidai lokacin da kuka buqaci na dawo gida ba,,

Karyar banza cewar aunty lateefah tana nuna nijlah,,wacece wannan?
Hade fuska mashkur yayi,,Zan gayamusu yanzu nagaji da yawa saina huta,,mummy kinajin abinda yake fada kinyi shiru??
Mummy bata iya motsawaba Saida lateefah tayi saurin girgiza ta kafin ta safke nannauyan ajiyar zuciya tana kallan mashkur Daya kafeta da Ido Yana mamakin halinda mummy ta shiga..
Dasauri yayi gurinta Yana cewa,,lafiya sweet mom,,waya tabamana ke”” dasauri ta daga masa hannu alamun karya qaraso inda take,,chak ya tsaya tare da hadiye yawun Daya taru a bakinta,,tinda yake mummy bata taba yimasa irin wannan karbar ba to kodai shima ya shafo abinda take kyama tattare da Fulani,,yayiwa kanshi wannan tambayan..
Bakin mummy na rawa tace,,auta wacece wannan?
Shiru mashkur yayi Yana tinanin amsar dazeba mummy sai ya maida kallansa ga nijlah yanasan yimata magana da ido,,aiko nijlah ta washe Baki tana tinanin amsa mashkur yakesan tabada..
Tace ehhh,,a kankan ya dauko ni kuma Malam ya daura mana” tsawa mashkur ya Daka Mata Yana hararanta tini nijlah ta rufe Baki tana karkarwa tare da komawa bayan aunty lateefah tana boyewa,, da mugun gudu lateefah ta dawo bayan yaya tare da Dora hannu aka..
Dan ubanka kabani amsa kafin yanzu na Saba ma,,yaushe kazama haka mashkur ni nake ma tambaya kana kallona,,,to kodai na chanza ma,, dasauri yace ah ah mummy dama dama.
Dama me,, gaskiya zaka gayamin ko angayama idan zakayi taimako saika kawomin irin jaraba har gidana,,Bama ta tsaya iya get ba shine saida Ka kawomin ita har cikin falona..
Zuciyarsa na dokawa yace mummy kiyi hakuri tare zamu zata zauna da ita”
A ina?mummy ta tambaya..
Batare da fargaba ba mashkur yace anan gidan,,sedai Ka zauna da ita Amma badai mummy ba” shima baze zauna da wannan annobar ba mummy taba lateefah amsa..
Kai Dan birni me suke fada,,Allah dai yasa badani suke ba,,cewan nijlah tana kallan mummy sai kuma ta sunkuya tace sannu ina yini..
Ke tashi anan kafin kimin barbaren kudin cizo Naga alama a wannan jikin naki babu abinda bazaa samu,,Kai mashkur Ka fitamin da ita a falo Ka kuma dawo kayimin bayanin inda Ka daukota..
Mummy marainice shiyasa na kawota ta riqa tayaki aiki,,mummy yarinyar bata da matsala Dan Allah karkice ah ah  yafada Yana hada hannu alamun roqo.
A tare mummy da lateefah har ma da yaya suka sa salati suna tafa hannu” lateefah ce tace cewa akayi mummy na buwatar ‘yan aiki,,to koma ina buqata saina rasa Wanda Zan dauka sai wannan..
Duk da yarinta da shirme irin na nijlah saida tagane kyamarta suke gashi taji Dan birni Yana maganar aiki zata tayasu,,to wai me suke nufi?
Wanne irin kallo suke min nijlah ta tambayeni kanta,bata dawo daga tinanin ba taji mashkur Yana cewa..
Mummy Dan Allah kiyi hakuri ki tayani riqe amanar da Allah ya doramin,,yarinyarnan marainiyace bata da gata shiyasa na kawomiki ita,,
Karya kake mashkur Idan Zaka fadi gaskiya ka fada ayita ta qare..
Haba Aunty lateefah,,ki tausayamata..

Ya mashkur kodai Suma Suna bakin cikin aurena,,Naga alama Suma irin kakane” Kuma ita wannan qatuwar wacece,,sukaji nijlah Na tambaya???
Ke kimin Shiru Nace dame kikeso Naji,,to wallahi naqara Jin maganarki Saina zaneki anan” turo baki nijlah tayi tana dire diren qafa,,a hankali mashkur yace menene Kuma,,Nina gaji Zama zanyi,,Kuma Dai ka Tina Allah Yana kallanka,,Kuma a wuta yakesa me Karya haka malaminmu ya Gaya a islamiyya,,gwara kawai kace matarkace Ni Kamar yadda ka Gaya Bello..
Gaba daya jikin mashkur yayi sanyi Dan haka ya zauna Kan kafet Yana Kallan mummy…
Mummy kiyi hakuri Nima ba haka naso ba,, mummy ki dauka kaddarace tasa nayi, Sai ya kasa qarasawa..
Qaddara tasa kayi me auta,,ka gayamin Ko hankalina Ze kwanta..
Mummy auren nijlah nayi a,,kafin ya qarasa magana mummy tasa kuka tana cewa..
Shinkenan ka cuci rayuwata ka nuna Kaine da kanka,me kakeso mu Gaya iyayen Yasmeen,,yanzu wannan abun Abar aure ce,,kadubeta kama an daurawa muciya zani..
Kallan jikin nijlah ya riqayi Shima Yana hawaye,,Dan Allah mummy kidena wannan kuka wallahi kukanki masifa ne a gareni da rayuwata mummy na tuba yafada Yana kama qafanta..
Saida mummy tayi kuka me isarta kafin tace ina Baka umarni Daka mayar da yarinyarnan inda Ka daukota kafin..
Mummy kiyi hakuri nijlah amanace agareni nayi alqawarin Zan riqeta duk rintsi,,bazan taba rabuwa da itaba..
Zaro Ido mummy tayi tana kallansu kafin tace a ina zaka zauna da ita?
Mummy Dan Allah ko dakin Baki Kona ‘yan aiki ki kaita nasan zata zauna” Kai wallahi ko a dakin Karen gidannan bazan ajiye wannan irin jarabar ba,,gwara tin muna arziqi Ka fita da ita..
Kafin yayi magana aunty lateefah tafara Jan nijlah da niyyar kaita waje,,cikin ihu mummy tace ke lateefah Baki da hankali zaki tana jikin wannan nida Zan iya da tinanin na kaita lahira hannunane bazan iya Sawa a jikinta ba,,Amma zanyi maganinta idan har be fita da ita a gidan nan ba..
Cikin kuka nijlah ta Koma Bayan mashkur tana riqe rigarsa tace,,Dan Allah ka fita Dani zasu kasheni,,Bata sona..
Kiyi hakuri nijlah komai zeyi daidai kinji,,mummy.
Karka qara Kiran sunana saika fara fita da wannan annobar,, mummy Bazan iyaba haqqinta Yana kaina.kiji tausayinmu.
Kaima kasan Bazan taba Zama da ita a gida daya ba Dan haka ka zabamata inda ya dace Kuma a yanzu nakeso ka saketa saki uku.
Mummy kiyi hakuri tinda bazaki Bata gurin Zama ba nizan zauna da ita a dakina,,batin saki Kuma kiyi hakuri Baz…
Lafiyayyun Mari Har guda uku Yaya ya safkewa mashkur Yana nunashi da yatsa,,kayi kadan ka wulaqanta mana uwa,,wallahi sedai kabar gidannan..
Beyi Magana ba ya kama hannun nijlah dake kuka tana Kiran Sunan kaka ya Shiga dakinsa da ita,,a qasa nijlah ta zube tana birgima tana ihu,,shiko bakin gado ya zauna ya dafe kansa Yana Jin Wani irin faduwar gaba..
Cikin kuka lateefah tace,yanzu haka zamu zuba ido mashkur yayi yadda yakeso,, ba Wanda yabata amsa..
Nan mummy ta dauka waya ta Kira daddy tana kuka,tace Alhaji ka dawo gida yanzu,,tana gama fada ta katse Kiran Bata jira amsar Shiba..
Wani layin ta Kira ta miqa lateefah wayar..
Yasmeen dake kwance Kan cinyar mama tana game a waya taga Kiran mummy,,kallan mama tayi jikin Jin Kunya tace,,mama mummyn mashkur ce.
Ki Daga mana cewan mama tana kasa kunne,,Yasmeen Na dauka lateefah tace ..
Sunana lateefah yayar mashkur,,mummy nasan ganinki yanzu….



Wash,, typing da wahala,,mu hadu a page na gaba..

Karku manta da share.



*Momn sultan ce*✍✍✍

Related Articles

Leave a Reply

Back to top button