NOVELSUncategorized

WUTSIYAR RAKUMI 14

NO. 14_* 

………….Farin cikin da Amarya Suhailat da  angonta Baseer ke ciki yau bayyanashi ɓata lokacine, a wannan dare dai kam babu ɗaga ƙafa saida ya amayar da kwaɗayinsa na kusan shekara biyu, tun tana biye masa da
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({}); marmarin soyayya harta koma jamasa ALLAH ya isa.????
     Da safe dai ya zage yanata lallaɓa kayarsa da riritata, yayinda itako taketa langaɓe masa, ko ruwa saitace saiya bata abaki, ita bazata iya shaba jikinta ciwo yake. Haka taita zuba masa taɓara a wannan yini.
      Da daddare yanemi sake morewa takoce bai isaba, yo kasheta zaiyi, daya matsa mata da magiyama kuka ta saka masa da ɗaukar waya wai zata kira Daddyn ɗinta.
       Da sauri ya warce wayar yana bata haƙuri da faɗin shifa da wasa yakeyi,  baki ta tura gaba tana jan bargo da juya masa baya. Dole ya haƙura ya kwanta shima ya rungumeta yana haɗiye kwaɗayinsa dan dole, amma harga ALLAH yaso sake ɗanɗanawa. (mijin Hajiya sai haƙuri to????).
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});

⚡⚡⚡⚡⚡⚡⚡⚡⚡⚡⚡

             Ƙarfe kusan biyu maman Ahmad ta sake aiko musu da abinci, Ummu na ɗaki ƴar aikin maman Ahmad tazo, A’i da suka taho da isa kawai ta iske zaune a falon tana kallo, rissinawa tai ta gaisheta dan A’i babbar mace ce sosai.
       “Aunty ce tace akawoma aunty Amarya”.
      Miƙewa A’i tayi tana faɗin “Tofa bara na kira miki ita”.

        Ummu na zaune ta idar da salla A’i tai sallama.
     Ummu ta amsa tareda bata izinin shigowa.
      tunda A’i ta shigo takebin ɗakin Ummukulsoom da kallo a kaikaice tana jin jina kai, lura da hakan da Ummu tayi yasata katseta da faɗin “Baba lafiya dai ko?”.
     “A babu komai uwar ɗakina, dama wata ƴar budurwace ta kawo abinci wai inji ko auntyn ta”.
       Miƙewa Ummu tayi tsaye tareda zame hijjab ɗin jikinta tana cewa, “Inaga maman Ahmad ce, ita bata gajiya tun jiya take ɗawainiya damu”.
       Ƴar dariya A’i tayi tana ficewa, Ummu ma ta biyo bayanta.
     Mai aikin Maman Ahmad ta gaidata cikin girmamawa, sannan tace “aunty amarya ga abinci inji aunty tace a kawo muku”.
      Fuskar Ummukulsoom ɗauke da murmushi tace, “Kice mata nagode sosai, ya sunanki?”.
     “Aunty Sunana Zubaida”.
   “Masha ALLAH Zubaida kice nagode kinji”.
       Bayan fitar Zubaida Ummukulsoom ta buɗe kulolin, abincine mai kyau yanata tashin ƙamshi, A’i sai leƙa kai take nason ganin minene itama?. Ummu ma batasan tanaiba, tafara kwashe kulolin tanufi dani dataga sunci abinci ɗazun. Tashi A’i tai ta tayata suka kai.
   Ana cikin haka saiga Yaa Amaan ya shigo, ita Ummu ma sai yanzu tasan baya gidan.
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});      Zubewa A’i tai tana gaishesa, ko kallonta baiyiba ya wuce cikin falon tareda amsa mata da “Lafiya”.
       Duk da zuciyar Ummu na rawa haka ta tako zuwa cikin falon tana masa sannu da zuwa.
     Fararen idanunsa ya ɗago yaɗan kalleta tareda janye idonsa lokaci ɗaya.
      Dukda bai amsa mataba saita sake daurewa tace, “Ga abinci maman Ahmad ta aiko dashi”.
       “Kuci kudai, zuwa ƙarfe takwas ina son ganinki”. ‘ya ƙare maganar da miƙewa ya wuce abinsa’.
     Kallo kawai Ummu ta iya binsa dashi a sace, hakama A’i dake laɓe a dani tana taɓe baki da naɗar gulma.
     Ummu ma data mance da ita ko kallon inda take bataiba tai wucewarta nata ɗakin itama.   
     A’i na ganin duk sun shige saita zaro wayarta dake saƙe a zani jikinta har ɓari yake, da sauri ta nufi ɗakin da aka bata ta zauna tana ƙokarin kiran Momcy ta fesa mata gulma, dan dama dalilin turota kenan danta sakama su Ummu ido kafin su Ummayya suma suzo.
      “Hajiya kun wuni lafiya?”.
     Daga can ta amsa mata cikin isa.
     Tsayuwa A’i ta gyara cikin kwarewa a gulma tace, “Uhm hajiya ai wannan ogan nawa nakula jan gwarzone sojan gaskiya, dan yarinyarnan kam bazataji da daɗiba a gidannan, kofa kallon arziki bata ishesaba wlhy, yanzunnan tagama masa iyayi da feleƙe akan abinci amma da kinga yanda yawani dizgata saima tabaki tausayi, kofa kallonta bayayi hajiya”.
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});        Wata ƴar dariyar mugunta hajiya jamila tayi daga can, “Nagode miki dakawo min labari mai daɗi A’i, dama ni na yarda da Fodio yarinyarnan sai taci ubanta a wajensa kafin kuma ya koro musu ita da jan kati, aiki na kyau A’i, adai cigaba da sakamin ido, nanda sati biyu su Aneesa ma zasu taho”.
         “To hajiya, insha ALLAHU zaki cigaba da samun bayani daki-daki kuwa daga gidan soja”.  

★★★★★★★★

          Ummukulsoom bata sakejin ɗuriyar Amaan a gidanba har akai sallar magriba, tana zaune tayi tagumi da tunanin ahalinta taji sallamar maman Ahmad, cikin mamaki ta ɗaga kai tana dubanta, mamaki ya ƙara kamata ganinta cikin kwalliya sosai.
      “Amaryarmu ya da kallo haka? Tashi maza kiyi sallar isha’i tunda gatacan ana kira, ga mai kwalliya zatai miki”.
     “Kwalliya kuma maman Ahmad tami?”.
      “Idan Ana salla ba’a magana amarya, kedai tashi kawai”.
      Babu yanda Ummu ta iya dole ta mike ta kabbara salla, Maman Ahmad tashiga buɗe kayan data shigo dasu  a leda tana bubbuɗewa. 
        Bayan Ummu ta idar maman Ahmad tace “zakiyi wankane?”.
      Cikin shagwaɓa Ummu tace, “A’a maman Ahmad yanzufa nai wanka”.
    Hafsat tayi dariya da riƙe haɓa, “Tofa amaryarmu ashe shagwaɓaɓɓace, kinga adana abunki sai Amaan na kusa”.
      Juyar dakai Ummu tayi tana murmushin jin kunya, har mai kwalliya ta shigo bata sake yarda sunyi magana da Maman Ahmad daketa kuma tsokanartaba.

★★★

      A ɗakin Amaan ma yanacan Attahir ya tsaresa akan saiya tashi ya saka wasu kaya daya kawo masa, suma dai na sojojine amma ba irin wanda suke fita aiki da suba.
      Haɗe fuska Amaan yakumayi yana harar Attahir, kafin ya janye idanunsa ya maida kan tv yana faɗin “Attahir kasanfa banason takura, wlhy harka fara samun ciwonkai, ina zamujene wai?”.
      “Nidai koma mizakace jekaita cewa, kamin alfarma katashi ka shirya, insha ALLAHU zaka gani ai, wlhy abune mai muhimmanci, kasan dai bana maka kalar wasannan ai, musamman danasan bakason fita ko ina idan 8 tayi sai dole”.
     Wani nannauyan numfashi ya sauke yana jan siririn tsaki, yakuma harar Attahir yana mikewa da jefar da wayarsa akan gadon dayake kwance da, “Banza kawai sarkin takura”.
       “Nadai ji bakomai”. ‘Attahir yabashi amsa yana ma bayansa gwalo’.
      Bayi yashiga kusan mintuna goma ya fito yana kuma tamke fusaka, sai da ya ɗakko best da boxer a Wadrobe ya juyo yana harar Attahir, “Dalla malam tashi ka fitarmin, Ko a gabanka zan shirya ne?”.
     Dariya Attahir yay yana miƙewa da faɗin, “Rufamin asiri, ni a suwa da kallon ƙato na shiri a gabana? Wannan sai Ummukulsoom”.
       Da sauri Amaan ya miƙa hannu zai damƙoshi, amma Attahir ya fice da ɗan gudu yana dariya.
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});      Amaan yay ƙwafa kawai yana lumshe ido da buɗewa daya zame masa jiki.

    Cikin mintuna kaɗan saiga maman Ahmad ta fito riƙe da hannun Ummukulsoom dake sanye da wata haɗaɗɗiyar doguwar riga sky blue, ta mata ƙyau sosai, an naɗa mata dark blue ɗin ɗankwali dayay mugun zama a kanta, tayi kyau harta gaji, babu wanda zai mata kallo ɗaya ya yarda Ummukulsoom ce ta ƙauyen ɗilau maima su Baba yalwa bauta.
     Attahir yaɗan zunguri Amaan dake ƙoƙarin ɗaura agogo, yayi ƙyau cikin Uniform kalar green shima,  kayan sunyi masifar zauna masa a jiki tamkar an hakiccesa dasu.
    Ɗago ido yay a fusace zaima Attahir masifa, danya fara kaisa bango da takurarsa, karaf idonsa ya sauka akan Ummukulsoom dake tsaye kusada Maman Ahmad kanta a sunkuye ta kasa kallon kowa. Haɗiye maganatsa yay cikin sarƙewar yawu, yay saurin ɗora hannunsa a baki saboda tahowar wani munafikin tari dabai shiryawa zuwansaba.
     Juyar dakai Maman Ahmad tai tana danne dariyar dake neman ƙwace mata da ƙyar, shiko Attahir saida ya dara kaɗan, kafin ya ɗauki ruwa ya tsiyaya masa a glass cup ya miƙa masa”.
     Harara ya dalla masa ya karɓa ya shanye yana kuma satar kallon Ummu da itama take kallonsa a sace, Sosai yay mata ƙyau, lallai ya cancanci zama soja tako wanne fanni, da’ace zata iya bashi shawara datace yayta zama da Uniform ajikinsa a kowanne lokaci.
     Ajiye kofin yay ya fice tamkar baiga komaiba, dariya Attahir yay yana kuma girmama halin abokin nasa, shi yasan abinda yafima haka zai aikata, amma yanaji a jikinsa komai zai wuce tamkarma ba’ayiba, dan irinsu Amaan basu iya shagala a soyayya ba, daga lokacin data kamasu saisu koma tamkar wasu bayin mace.
        A’i na laɓe tana kallon duk abinda ke faruwa, ƙwafa tayi tafito sosai bayan taga Amaan ya fita. Cike da ladabi tace, “Anguwa za’a ne Uwar ɗakina”.
     Su duka kallonta sukayi, kafin Ummu tasamu damar bata amsa Attahir yace, “Zamuje wani wajene, zuwa 12 haka zasu dawo insha ALLAH”.
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});     “To ALLAH ya tsare”. ‘Tafaɗa tana kuma satar kallon Ummukulsoom ɗin’.
    Amsawa sukai da amin suka fice abinsu da barinta da ƙududun baƙin ciki da gulmar dake cinta. Jikinta har ɓari yake ta dannama Momcy waya ta fesa mata zance.

     Ran Momcy a ɓace takira wayar Amaan danson jin ina suka nufa?.
    Lokacin Ummukulsoom na ƙokarin shiga Motar da aka buɗe mata inda tun fitowar Amaan ya shiga.
    Ko motsi baiyiba dukda jin wayarsa na ring, Ummu data zauna ta saci kallonsa ta gefen ido, a mamakinta sai taga yanajin wayar amma ya share.
    Kauda kanta tayi gefe da roka masa ALLAH shiriya a zuciyarta.
      Suna fara tafiya ya maida kansa ya jingina da kujera ya lumshe idanunsa yana shaƙar daddaɗan turaren Ummukulsoom na haɗin khumra.
    Tafiyarsu ta ɗanyi Nisa taji muryarsa mai cike da amo na faɗin “Abbas mu shiga wajen nan”.
      Satar kallonsa Ummu tayi ta gefen ido, amma sai taga har lokacin yana kwance jikin kujerar idonsa a lumshe, aranta tace toshi wannan zuciyarsace idonsa halan?. Bata da mai bata amsa dan haka ta tsaya sauraren miza’ayi a wajen.
         Abbas daya gama parking ya juyo ya kallesa, cikeda ladabi yace, “Sir mun tsaya”.
      Batareda ya buɗe idoba ya miƙa masa ATM card ɗinsa yana faɗin “Shiga wajennan kasamo gyale dark blue”.
       Amsar ATM ɗin Abbas yay ya fita, yayinda Ummu tama kasa fahimtar maganar tasama gaba ɗaya.
     Shi kansa Abbas bai fahimtaba, amma gudun yin laifi saiya kasa tambaya ya buɗe motar ya fita.
    Ganin su Attahir ma sun faka saiya nufi motarsu danya tambaya.
     “Abbas lafiya kuwa naga kun tsaya?”. ‘Attahir ya faɗa yana fitowa daga tasu motar’.
      “Sorry Sir!, Boss ne yace nashiga nan nasayo gyale dark blue, nikuma nakasa ma fahimtarsa wlhy”.
      Attahir ya haɗiye dariyarsa gudun yin abun kunya gaban yaransu su Abbas, nuni yayma Abbas da hanya alamar suje to”.
    Cikin sunkuy dakai da girmamawa Abbas yabi bayan Attahir.
     Mintuna kaɗan suka fito hannun Abbas ɗauke da jikka ƙarama mai ƙyau????.
      Saida ya shiga mota sannan ya miƙama Amaan.
       Koda ya karɓa saiya ɗora saman cinyar Ummu batareda yako kalleta ba balle tasamu arziƙin ƙarin bayani.
     Kallonsa taɗanyi, cikin dauriya tace, “Yaya miza ai dashi?”.
      Da gefen ido ya kalleta yana maimaita kalmar yayan data faɗa a zuciyarsa, toshi yaushene yama zama yayanta?.
    Sharewa yay yaki bata amsa, dan haka itama ta tsuke bakinta.
      Babu wanda ya sake magana a motar har suka isa inda zasuje bisa jagorancin Attahir.
       Wani hotel ne mai aji a cikin anguwar tasu ta da babu yawan hayaniya, Sojojine birjik zagaye da Hotel ɗin, ga motoci a zube ko ina, tsoro yakuma mamaye zuciyar Ummu ganin sojojin……..
     Bata kammala tunaninta da neman amsaba taji an buɗe musu ƙofa. Ganin yaƙi koda motsi sai ita tai yinƙurin ficewa abinta.
      Harta zira ƙafa ɗaya taji an cafkota da wani lallausan hannu, juyowa tayi a firgice danson ganin wanene haka?.
      Gabanta ya faɗi ganin hannunsa riƙe da tsintsiyar nata hannun, sannan yana nan zaune yanda yake ido kuma a rufe. Sai kawai ta maida kanta ta sunkuyar, dan wannan faɗan kam yafi ƙarfinta.
      Jin Attahir ya kuma cewa, “Amaryarmu fito kinji”  saita kuma yunƙura zata fita.
       Wata irin figowa yay mata data haye saman jikinsa gaba ɗayanta, take jikinta ya fara ɓari, kafin tagama fahimtar manufarsa ta tsinci kakkausar muryarsa cikin kunnenta yana faɗin “Idan har ƙafarki ta taka wajennan ahaka babu mayafi saina lallasaki wlhy”. Yana gama faɗa ya tureta daga jikinsa ya fice abinsa.
       Daga Attahir har maman Ahmad galala sukai suna kallon ikon ALLAH, dukda kuwa basuji miyake faɗa mata ba.
        Da ƙyar Ummu tasamu damar haɗiye yawun daya toƙare maƙoshinta, ganin mutane ta danne firgicin data shiga da ƙyar tana ƙokarin buɗe jakar daya ajiye a jikinta. Ganin mayafi kalar ɗan kwalinta saita shiga ƙokarin buɗeshi daga leda.
     Maman Ahmad data ɗan fahimci lamarin nasune ta leƙo motar ta amshi mayafin ta buɗema Ummu shi, daƙyar take danne dariyarta da mamakin Amaan, tace, “Amarya angon nakifa na lura akwai kishi, wlhy ina bayansa, konine bazan yarda kishiga wajennan ahaka ba”.
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});       Kasa fahimtar ta Ummu tayi, dan ƙwaƙwalwarta bata gama dawowa daga ruɗanin data tafiba har sannan. Bayan ta kammala yafa mayafin ta fito da taimakon maman Ahmad.
      Ɗan kama hannun da ango kema amarya shi ƙinyi yayi, yadai tsaya suntafi a jere su Attahir na binsu abaya da gayyar sauran abokansu sojoji.
     Shigarsu ƙaton hall ɗin dake dinɗim da duhu ne yakuma tsurar da Ummu, taɗan matsa jikinsa batareda ta shiryaba. Yana ƙoƙarin zaro wayarsa ya haska aka kunna hasken fitulun hall ɗin da suka ƙawata adon da akai masa, ɗunbin jama’ar da aka tara suka saki ihu suna masa murnar aurensa, barin jikinsa da Ummu taɗan jingina tayi tana ware idanun mamaki, shikansa sai yanzu ya fahimci abinda ke faruwa, dan haka ya ɗan lumshe idanunsa yana buɗewa akan jama’ar hall ɗin………….✍????

Related Articles

Leave a Reply

Back to top button