NOVELSUncategorized

YAU DA GOBE 1&2

????YAU DA GOBE????

????????????????????????????????????????

Story & written by mmn fareesa

*Gargadi*….banyarda wani ko wataba yajuyamun novel ta kowace siga….inhar hakan yafaru…mutum yyi kuka da kanshi….

Bissimillahir rahamanir Rahim…

????️1&2

  ….Afusace yashigo cikin parlourn fuska atamke bbu ko sallama yadubi zarah daketa  latsar waya”yace Wai meyasa bakyajin shawarane?” Saunawa zance Miki kidaina sakarwa  samari fuska ko wad’an can tsaffin  banzan suna zuwa gunkine?”

Sorry broth! Wlh nima bansan kowaye ba ” nadena kayi hakri karka b’ata ranka….tafada cikin sanyin muryarta”b’ata Rai har yaushe inkina gudun b’acin Raina ai hakan bazai faruba …nacire hannuna a al’amarinki tun….sannu uwarta sannu ubanta nace! Cewar ummi fuska a’daure ta katsema  musty mgn”

Turo Baki yyi had’e da cewa “ai dama ummi Keke goyan bayanta..eh nagoyi bayanta shasha Sha…inbacin fitinarka Aida yanzun tayi aure duk Wanda yazo gunta saikace beda kaza da kaza koka koresa”in anyi mgn kace karatu kukeyi to ai gashidai saura watanni ku Ida shi k’addararran katun” inbatayi aure ayanzunba sai yaushe zatayine?”Wai ummi duka duka baby shekaran ta nawa?”27 fa”meye aciki da za’aga ta jima…dak’k’uwa ummi tamasa had’e da cewa…Inka Gama Mata fad’an sai kawuce air port kaje kad’auko yayanku sbd yanzun muka Gama waya yace sunkusa sauka…musty da zarah atake suka saki murmushin farin ciki sbd jin yayansu Wanda yamaye musu gurbin uba zai dawo dg UK amatsayin babban likita…

     Zarah tadubi musty tace broth zanje na rakaka inmundawo saika kaini gun kamun aminar da marece ko”had’e Rai yyi yace bazakijeba duka da kamun da bina airport d’in…bejira cewartaba yabar parlourn..

Ummi taja tsaki had’e da cewa duk ikon dayakeyi dake kekikaso”Yana k’aninki…Amma in har yagindaya Miki umarni saikinbi”kina Masa biyayya tamkar wani ubanki ko yayanki”

Ajiyar zuciya zarah tayi had’e da cewa “to dudu ba2 yrs naba shiba” da yawa zatonsu Yayana ne sbd karamin jiki danike dashi…kumafa   ummi kinsan  yanzun inhar naje” to gaba ce zai fara dani yadena walwala har abinci zai iya Dena ci”kinsani inhar Yana fushi haka yake yi… tab’e Baki ummi tayi had’e da cewa kwaji dashi…ki wuce kitchen kihad’a mun lemon kwakwa,kicewa laraba ta gyara ko Ina n kitchen d’in tunda mun Gama komai!

   Da to zarah ta amsa tana ficewa dg parlourn”ummi tayi ajiyar zuciya”had’e da  cewa ohni Aysha me yaron nan yake nufi da zarah?”

Inna fahimcesa wlh sontane da kishinta yake nunawa k’arara”Anya hak’ansa zai cimma ruwa?” Dole natake Masa burki gsky gudun abinda zaije yadawo….



    “Ahankali yake sakkowa dg matattakar jirgin”fuskarsa sanye da had’add’an eye glass bak’i..sanye yake d suit red…yanata xuba fitinannan k’amshi” kallo d’aya zaka Masa kasan hutu da wayewa sun zauna ajikinsa” DR ALIYU UMAR SAFANA….Wanda ake ma lak’abi da (Dr safana)matashin saurayi Mai jini ajika Dan kimani shekara33 aduniya….kyakykwane ajin farko akwai Kamala had’e da kwarjini atare dashi”wankan tarwad’a ne Shiba fariba bakuma bak’i ba”tattausan murmushiin farin ciki yasaki sbd yashak’i iskan k’asarsa ta haihuwa(Nigeria)idon sa k’yam akan kaninsa “ALMUSTAPHA”saurayi Dan kimani 25 years”da hanzari musty yanufesa da gudu Yana dariya yyi hugging nasaa..

    Shima hugging nasa yyi back” suna murmushii da farin cikin ganin juna”kafin musty yacikasa Yana janyo trolley’s  d’in yayansa…Yana cewa barka da dawowa k’asarka ta haihu Yaya! murmushii yyi yace thanks autan ummi…Ina zarah…Bata fuska yyi yace Yaya baby batajin mgn ta”nabarta agd..yafada suna nufar mota…Dr safana yashiga ya na cewa zaku shiryane soon… Saikallon juna suke sbd kowa ganin d’an uwansa yake yacanza dukda suna vedio call ga pics ta what’s app suna sharing ma junansu…duka ba wani jimawa yyiba a UK din”shekararsa 3 acan”musty yace Yaya I’m very happy wlh” yanzun kaga ankammala komai na asibitinka har anzuba ma akaita…duk Kuma aikin Yaya Nasir ne…Kai gsky bantab’a ganin aboki na gari irinsaba”Allah yabarku tare”ameen yafada atakaice yanata aikin kallon musty mamakin girmansa dank’a re aransa”tunani yakeyi wanima ai saiyace abokinsane ba kaninsaba”shikuwa musty be damuba da rashin maganar yayansa sbd dama yasanshi miskiline dukda shima bawai cika mgn yyiba Amma garashi akan Dr safana…

Dr safana yace gsky autan ummi kayi girma sosai ai wani sai yazata ka ajiye family! Wani miskilin murmushii musty yasaki Yana driving hankali kwance yace hmmm ai Yaya very soon Zan ajiye family tunda Kai kak’i Yi…tab’e Baki Dr safana yyi Yana latsa wayarsa..da haka suka iso gd…



Ummi na zaune tana lazimi byn ta idar da la’asar suka shigo…da gudu zarah ta rungume yayanta tana ihun murna”yaja hancinta Yana cewa baby Baki girma dube musty saikace yayanki”haba Yaya ai namiji babbane ako Ina “saikuyi ta cemun nayi girma…cewar musty Yana turo Baki…ummi tamasa dak’k’uwa”yyi dariya”Dr safana ya rungume mahaifiyarsa cike da farin cikin ganin ta…kafin su zauna  agaisa… sannan Dr safana ya wuce part nasa Dan ya watsa ruwa..



     Zaune suke gaba d’aya adining area suna lunch”bakajin komai sai k’arar cokulla”fuskar kowa awashe dukda musty k’asan ransa akwai damuwa…d’ago kansa yyi yadubi zarah daketa cin abincinta hankali kwance shikuwa sai tsakura yakeyi”

Yyinda ummi ke hankalce dashi…ajikinta taji kallonta yakeyi…dubarsa tayi aikuwa sukayi4 eyes”tamke fuska yyi had’e da mikewa tsaye zai bar Gurin”ummi ta dataka tar dashi Gurin cewa Ina zakaje ne,har ka koshine??”

Kaina ke ciwo ummi!Dr safana dake jin dad’in abincinsa yake loda hankali kwance yace hmmm ummi k’arya yakeyi”ummi tace yaji dashi ai”in anjima inaso muje mu duka gdn abbanku alh Usman “kunsan jiya yyi amarya ta tare “inaso muje aga juna agaisa asami ladar zumunci”musammun Kai babana tunda baka k’asar sai yau kadawo “tafada tana kallon Dr safana”cikin karfin hali yace to ummi ALLAH ya kaimu anjiman”Amma k’asan ransa yaso ace a office din abban k’anin mahaifinsa yaje yagaidashi basai yaje gdn ba”gashi ance yasake aure…can Kuma yatabe baki”sbd tuna mugayen halayen hjy jamilah  matar abban”shiyasa gaba d’aya yaran gdn besakarwa kowa fuska inba Sadiq ba! Shima sbd yafisu hankali”

   Inbe mantaba kafin ya tafi UK jidda tadubi tsabar idonsa tace Wai tana sonsa”gaba d’aya hjy jamilah tab’atawa yaran tarbiyya… da wannan tunanin ya Ida cin abincin “ummi najansa da fira”yyinda zarah tayi shiru tana son fakar idon ummi taje tasami musty tabashi hakuri….



*************

*Gidan alh Usman*


Gaba d’aya suke zaune a babban parlourn gdn “hjy Jamila hakimce kan kujera..dattijuwa Yar kimanin shekara 45 aduniya! ta aza kafa d’aya kan d’aya tanata wata yatsina had’e da tsare Mai gdn nata da ido tana aika Masa da mugun kallo” sbd k’ule take dashi namata kishiya da yyi..yyinda yaran su4 suke zaune akan carpet”Abba tattijon artsik’i d’an kimanin shekara 55 aduniya Yana zaune” sanye da farar jallabiya  da medical glass afuskarsa.

Yanata aikin kallon wata k’ofa dake fuskantarsu…Wai alh lfy ne? Ina Zaman zamana  kasa ankirani “kakuma kinyin  mgn”in bakada abin fad’a nakara gaba”cewar hjy jamilah tana huci….hakan yyi daidai da shigowar mutum2 Mata ta k’ofar da Abba keta kallo… murmushi yasaki Yana kallon amaryarsa da y’arta…sallama sukayi yarinyar ta zauna ak’asa mmnta ta zauna kan kujera…tadubi hjy jamilah tace hjy Ina wuni?”cikin yatsina hjy jamilah tace oh wai Dani kike?”batace komaiba”hakama Abba”yyinda yarinyar tagaidasu Baki d’aya…

1 2Next page

Related Articles

Leave a Reply

Back to top button