BA DON SHIBA HAUSA NOVEL

BA DON SHIBA 81-85

Page 8⃣1⃣ to 8⃣5⃣

Suna shiga cikin hall din gaba daya kallo ya dawo kansu musamman ma jiddah duka itama rabi tana kyau.

duk inda suka ratsa sai maxa sun bi jiddah da kallom maita ita kuma hakan yasa gaba daya take jin wani iri na rashin sabo.

a can baya suka zauna saboda cewar mansur wai baya son ana kalle masa jiddar sa.

sai a lokacin jiddah ta lura da irin mutanen dake zaune a hall din.

gaba daya yan matan wurin bamban cin kayan su da tsirara kadan ne.

ba abinda suke banda iskanci wannan na kan cinyar wannan wasu kuma suna can gefe suna matse yan matan su.

maganar da mansur yayi ne ya dawo da ita duniyar tunanin da ta afka sai a lokacin ta lura daga ita sai shi a wajen.

kara maimaita yayi yace”baby me zaa kawo miki”.

girgiza kai kawai tayi da alamu dai bata son komai.

ki gama jan ajin ki a yanzu zaki shigo hannu ne har sekin fi rabi budawa a harkar duk a zuciyar shi yake wannan tunanin.

matsowa yayi kusa da ita har cinyarta na gogar tashi sannan ya riko hannun ta ya fara murza wa a hankali.

tana son kwacewa amma hakanan sai taji kamar ana hanata.

haka ya cigaba da murza hannun ta har ita kanta ta fara jin dadin abun.

lura da yayi hakan ne ya tabbatar masa da ba zata wuyar bada kai ba.

mikewa yayi tare da fadin”ina zuwa”.

bai fi 5mnt ba ya dawo hannun sa rike kofi guda 2 zama yayi a inda ya tashi sannan ya mika mata kofi 1 kasa musawa tayi ta amsa amma bata shaba.

kallon ta yake irin kallon samarin da suka nutsa a harkar bariki kisha mana.

kadan tasha ta ajiye sunanan sunfi 30 mnt a zaune ba abinda yake banda kallon ta yanzu takai ma rabin jikin ta na jikin shi.

a lokacin duk yawanci samari da yan matan wurin duk a buge suke kowa jan tasa yake yi su fita.

sai da rabi ta kusan kwashe 1hr sannan ta dawo itama da alamu a bugen take kallon ta jiddah keyi amma ba bakin magana saurayin nata shima haka.

sai karfe 12 na dare suka bar wajen.

suna sauke su a kofar gida suka fito dukan su a motar rabi na jikin ameer saurayin ta ita kuma jiddah mansur na rike da waist din ta yana mata magana a hankali.

a nan ma sunfi rabin awa kafin mansur ya sake ta tare da fadin goben fa zan zo.

murmushi kawai tayi sannan ta rike rabi wadda har yanzu take a buge suka shige gida.

dakin inna asabe ta kai ta wadda ke ta sharar baccin ta cikin kwanciyar hankali.

fita ta koma dakin ta sai da ta cire kayan ta sannan ita ta kwanta.

✨✨✨✨✨✨✨✨✨✨

BAYAN WATA BIYU

A wannan lokacin sai dai mutane subi jiddah da fatan shiriya domin kuwa mansur ya riga ya bude mata ido da kudi kashe mata su yake kamar bai san zafin su ba waya me tsada ya siya mata ga suturu n alfarma.

idan kaga jiddah a yanzu ba zaka ce itace jiddan da ammar yake matukar so da tausayi ba mutanen unguwa kuwa ba abinda suke sai tsine mata da kiran ta da karuwar gida dan ita bata komai a boye.

maman salaha ce kadai ke bakin cikin irin rayuwar da jiddah kuma tana zargin inna asabe da hakan.

yanzu takai ba madmsur kadai take kulawa ba domin kuwa kowa burin sa a ganshi jiddah saboda tsabar kyanta gata kuma karamar yarinya.

burin innah asabe ya cika a yanzu domin kuwa yanzu bata yar gaban goshi kamar jiddah domin kuwa yanzu fanta mawa take da kudin da jiddah ke samowa gashi kuma ta fito da ATM din da ammar yaba jiddah zaron kudi take a koda yaushe tana kara siyoma mata kayan matsu.

INA LABARIN AMMAR MUTAN INDIA

KU BIYO NI A NEXT PAGE

Related Articles

Leave a Reply

Back to top button