BABU SO HAUSA NOVEL

BABU SO 66

ɗacin hakan, amma taci alwashi komi zai faru

a yanzu ɗin bashi ne Anaam ɗin zataci itama

zata rama.

Aysha ta dire tray ɗin hanunta a gabansa,

fuskarta da murmushi ta gaida Fadwa da taƙi

kallonta saboda kar Aysha ta fahimci tayi

kuka. Kanta kawai ta jinjina mata. Ayshan

bata damu ba, dan tasan halin Fadwa wani

lokacin itama akwai yarfi. Hankalinta ta

maida akan Share!, “Yaya a zuba?”. Kai ya

girgiza mata alamar a’a, sai kawai tai musu

sallama ta fice a ranta tana ayyana akwai

matsala gaskiya, sai dai rashin ganin Anaam

yasa taji wani iri.

Kusa da shi ta taso ta dawo, “Soulmate……Hannu ya ɗaga mata a fusace. “Fadwa! leave

me alone. Tashi ki fita”.

Idanu ta tsura masa zuciyarta na mata

raɗaɗi, tasan a cikin fushi yake, kuma shi baya

son yanke ma mutum hukunci cikin fushi. Jiki

a saɓule ta tashi ta fice wasu hawaye masu

zafi da jin matuƙar tsanar Anaam na ƙaruwa a

ranta. Dan a ganin duk an mata hakane

saboda Anaam, ta kuma tabbatar ba haka

iyayen Anaam suka bar Share! ɗin ba kamar

yanda Mama ta sanar mata yanzun.

Ya jima zaune a wajen zuciyarsa na masa

raɗaɗi da ƙuna, baya son ɓacin rai da

damuwa, yama rasa ina zai kama da halin

matan nasa. Ya samu ita Anaam ɗin ta sakko

ya fara samun kwanciyar hankali ita kuma

Fadwar na neman rikita masa lissafi. dole ne

ya musu sabon shiri na zama da kowacce da

halinta. Yasan duk abinda Anaam zatai tana

yinsane a karan kanta sannan bata da ɓoye-

ɓoye. Fadwa kam ya fahimci akwai zugar

mutane baibaye da ita, dan tun zuwan Anaam

gidan ya fahimci ta ajiye wasu halayenta na

zahiri ta aro waɗansu daban, idan bai tashi

tsaye a kanta ba zasu iya laɓewa a bayanta su

tarwatsa masa farin cikin gidansa, shi kuma

harga ALLAH yana sonta itama. Ya furzar da

numfashi mai ɗaci, tunawa da Anaam dakecikin bedroom ya sashi miƙewa ya nufi

bedroom ɗin. Da mamaki yake kallonta

kwance a gado har tayi barci, ya tsugunna

saitin fuskarta yana sakin murmushi da kai

hannu ya shafa kanta. “Dama fitsarin ƙarya ne

kenan?”.

Idanu ta buɗe a hankali dan dama barcin

baiyi nisa ba, sai kuma ta maida zata lumshe

da ture masa hannu. Hannun nata ya riƙo

cikin nashi, fuskarsa gab da tata, “Tunda kin

tashi muje kisha fruit ɗin”.

“Ni na ƙoshi barci nakeji Yaya”.

“Ni kuma ban yarda ba idan kika sha sai kiyi

barcin”.

“Uhhum-uhhum”. Ta faɗa tana noƙe

kafaɗarta. Miƙewa yay yana murmushi, ya

ɗagata gaba ɗayanta. Watsal-watsal ta farayi

da ƙafafunta. “Wayyo Yaya! Wayyo Yaya ni ka

saukeni na ƙoshi”.

“Wayyo Aunty! Wayyo aunty ni bazan

saukeki ba sai kinsha”. Ya faɗa dai-dai suna

kaiwa falon………

Previous page 1 2

Related Articles

Leave a Reply

Back to top button