BABU SO HAUSA NOVEL

BABU SO 66

, dolene mu koma gidan…. Basai na faɗa ba.
[11/25, 10:30 AM] Hajiya Qarama: jimawa, Anaam dafe da kanta dake mata ciwo

saboda kukan da tasha ɗazun, ga jikinta har

yanzu sam baya mata daɗi irin na shiga

sabuwar rayuwar da ba’a saba ba. Aysha ce ta

amsa masa sallamarsa, ya ƙaraso ciki idonsa

akan Anaam. Ya miƙama Aysha dake masa

sannu ledar hanunsa.

“Ita wannan lafiya kuwa?”.

“Kanta ne ke mata ciwo, nayi-nayi tasha

magani kuma taƙi”. Zaune yakai kusa da ita,

ya janye hanunta dake dafe da kanta. Kasa

kallonsa tai, dan haka kawai take jin wani irin

matsanancin kunyarsa. Shiko ya matuƙar

shagala ne a kallon kwalliyar dake zane akan

fuskarta, a kasalance yakai hannunsa kan

haɓarta ya ɗago fuskar da ƙyau, hakan sai ya

tilasta mata ɗago nata idanun dake cike da

ƙwalla ta kallesa. Ba ƙaramin jarumta yay

wajen jawo numfashinsa dake neman

kufcema ƙirjinsa ba, ya matsota jikinsa tare

da ɗaura hanunsa saman goshin nata.

“Wannan idon naki kinyi kuka da shi, ko

muje asibiti ne?”.

Ya faɗa a hankali cikin kunenta. Kanta ta

girgiza masa da ƙara lafewa a jikin nasa har

hakan ya so bashi mamaki. Dan yasan dai

koshi ya ringumeta turesa take kota janye

jikinta, amma yanzu ga saɓanin hakan yanagani, koda yake tunda abin nan ya faru ya

fahimci ta zama wata shiru-shiru, tsiwar taɗan

ragu kaɗan ko likimo ne, mata sunji maza

kenan. Fitowar Aysha ta sakata janye jikinta,

shima sai ya miƙe yana faɗin, “Bara na watsa

ruwa sai a samo miki magani”.

Baki ta ɗan tura masa da kaiwa kwance. “Ni

basai nasha magani ba fa”.

Juyowa yay daga niyyar barin falon da yayi,

“Oh tunda hakane tashi na fasa barinki anan

ɗin”.

Dole badan taso ba ta miƙe, dan ya tsuke

fuska babu alamar wasa, duk da dama dai

tunda ya shigo babu fara’ar tattare da shi.

Aysha da tuni ta koma kitchen yay kira. Fitowa

tai da sauri tana amsawa.

“Gyaramin fruits ɗin nan”.

“To Yaya. Ko’a haɗa salad?”.

“Duk yanda kikai is ok”.

Kanta ta gyaɗa masa, shi kuma ya kama

hanun Anaam suka fice. Ta bisu da kallo

murmushi bayyane akan fuskarta. Tana fatan

ALLAH ya hana su Mommy raba wannan

auren har abada. Dan sun kasance abin

birgewa best couple ever matuƙa”.

Koda suka iso sashen nasa a falon ya zauna,

ya riƙota saman cinyarsa ya zaunar. Yanzun

ma cikin mamaki yaga ta lafe a jikinsa. Ya ɗan

murmusa da shafar fuskarta idonunsa na binfuskarta dake ƙwaɓe alamar rashin jin daɗi

da kallo.

“Kodai har yanzu garden ɗin na zafinne?

Noorie!?”.

Kanta ta sinne a ƙirjinsa da riƙo hanunsa

dake kaiwa jikinta, dan zuwa yanzu ta fahimci

mi yake kira garden ɗin. “Yaya Please ka

daina”.

“No Aunty babu wannan zancen”.

Ya faɗa cikin kwaikwayon muryarta.

Murmushi ya kufce mata tare da ƙara cusa

kan nata cikin jikinsa. Dan yanda yay maganar

ya matuƙar bata dariya. Shima murmushi yay

da kaima wuyanta kisses. Tsoro ne ya kamata,

tai ƙoƙarin jan jikinta baya amma ya hana

hakan.

“Wayyo kaina zai fashe Yaya”.

Dakatawa yay daga ƙoƙarin cusa hanunsa

cikin rigarta. Ya riƙo kannata. “Ayya. Sorry,

sorry”. Sake langaɓewa tai kamar gaske. A

ƙasan ranta kuwa dariyace ke taso mata tana

dannewa. Da gaske kan nata na ciwo, amma

yanda takeyi ɗin yanzu harda pretending. Yin

hakan kuma shine mafita a gareta saboda

ganin yana neman sakin layi, itako a yanzu in

ba giyar wake tasha ba mizai kaita sallama

masa ya kasheta. Ai anyi kenan babu ƙari

tunda abun azaba kawai akesha a ciki. Ita jiya

tunaninta gaba ɗaya akan tayaya wasu matanke iskanci a cikin wannan wahalar? Ko kuwa

su basajin abinda taji da bazata taɓa

mantawaba har duniya ta tashi.

Zaunar da ita yay a kujerar ya shiga bedroom

ɗinsa. Dai-dai nan Fadwa tai sallama. Anaam

tai kamar bazata amsa ba sai kuma ta amsa

ciki-ciki. Sam Fadwa bataji an amsa ba, sai dai

sanin halin mai sashen da kuma halin da suke

ciki na fushi da juna ya sata shigowa a ganinta

kobai amsa ɗin ba zata shigo. Turuss ta ɗanyi

na ganin Anaam, sukaima juna kallon cikin

ido kowacce ta janye da takaicin ƴar uwarta

da tsagwaron kishi.. Basuyima juna magana

ba, Fadwa ta nema waje ta zauna.

Fitowarsa ta saka Fadwa ɗaga kai tana

kallonsa, shima ita ɗin yake kallo da mamaki

a ƙasan zuciya, sai dai a fuska babu ko ɗigon

hakan sai ma janyewa da yay cikin halin ko’in

kula ya nufi Anaam dake kallonsu ta ƙasan

ido. Ita dai bata san sunada wata matsala ba a

gidan. Dan haka bata kawo komai a ranta ba

game da ɗaure-ɗauren fuskar tasu. A hanun

kujerar da take kwance ya zauna,

“Tashi kisha. Kimmaci abinci kuwa?”.

Sai da ta ɗan saci kallon gefen Fadwa sannan

ta ɗan tura baki da narke fuska. “Ni banajin

ci”.

“Uhhm baƙya son ci, yarinyar nan ki ragetaɓaran nan naki, yanzu abincin ma sai kin

nuna masa hali? Yanzu dai kinga ba’a shan

magani sai da abinci, faɗamin mi zaki ci?”.

Kallonsa ta ɗanyi da juya ƙwayoyin

idanunta, sai kuma ta narke fuska da girgiza

kai. “Da gaske bana son ci, barci nakeji kawai”.

“Uhm-uhm fa, bana son zama da yunwa

sam! Ki dai sha ko fruits ɗin can ne idan Aysha

ta kawo. Zakisha ko?”. Ya ƙare maganar da

ranƙwafowa kanta yana sinsinar wuyanta. Ta

gefen ido ta saci kallon Fadwa, sai taga su

take kallo fuskarta ciɗin-ciɗin kamar zata

fashe har wani jajaja takeyi na alamar ɓacin

rai abunka da fari. Murmushi tai mai sanyi

dakai hannu ta shafi fuskar tasa a ranta tana

faɗin (Ashe kin san akwai ciwo ni kike yi masa

kiss a gabana, zan koya miki iya zaman

duniya). Hanunta da take neman janyewa ya

cafke da sauri yana maidashi akan tattausan

gashin kumatun nasa. “Kin yarda zaki sha?”.

“Ni dai ɗan kaɗan”.

Ta faɗa a shagwaɓe.

Da ƙyar ya iya jan numfashi, dan shagwaɓar

tata ba ƙaramin susutashi take ba. “Good

girl”.

Murmushi tayi da janye hanun. Riƙeta yay, ta

marairaice masa. “Nifa fitsari zanyi”.

“Okayy to ana buƙatar abokin rakkiya?”.Ta faɗa da zille masa tana ƴar dariya.

Bedroom ɗinsa ta nufa batare da ko sashen

Fadwa ta kallaba. Tana shiga ta zube a

gadonsa dan babu wani fitsari dama. Kawai

dai taba Fadwa space ne. Domin rama abinda

tai mata bashike nufin bazata mata adalci ba.

Kuma koba komai yanzu kawai ta nuna mata

cewar alwashinta tabbatacce ne akan mantar

da Yaya MM ita in har tana a tare da shi.

Shiko daga can da kallo ya bita har saida ta

shige, a hankali ya haɗiye murmushi kan

fuskarsa. Miƙewa yay kamar zai bar falon.

Tasan idan tai wasa da wannan damar zatafi

haka shan wahala. Kamar yanda Mama

(Gwaggo halima) ta faɗa mata ba haka ake

buƙata ba, taje ta shirya dashi kodan

kasancewar gobe ne zata amshi girki, suna

buƙatar tai aiki da wasu fitinannun maganin

mata da aka kawo dominta tun daga ƙasar

sudan.

“Dan ALLAH kayi haƙuri” ta faɗa da sauri

tana ƙoƙarin haɗiye hawayen da tun ɗazun

take son su zubo ko zata samu sassauci.

Ratseta yay zai wuce tai azamar riƙosa. Bai

juyoba amma ya dakata. Ta share hawayenta

hanunta riƙe da nasa. “Dan ALLAH kayi

haƙuri, nasan nayi kuskure. Amma wlhysharrin shaiɗanne”.

Ransa a ɓace ya dubeta da wani mugun kallo

daya matuƙar neman gigitata. Saurin sakinsa

tai da girgiza masa kai. “Nasan nayi kuskure

amma dan ALLAH kayi haƙuri haka bazata

sake faruwa ba”.

“Tashi kibar min falo”.

“Please Soulmate dan ALLAH”.

Sallamar Aysha ce ta sakashi haɗiye maganar

bakinsa, ya koma ya zauna da amsa mata.

Itama hawayenta ta shiga sharewa idonta na

satar kallon ƙofar bedroom ɗinsa, dan

zuciyarta raya mata take Anaam na wajen

laɓe tana saurarensu. Sosai takejin raɗaɗi da

1 2Next page

Related Articles

Leave a Reply

Back to top button