GOJE

GOJE 39 and 40

Wani irin bugawa! gabanta yake kanta yana juyawa! tunda ya fara maganar ta nemi yawu ta rasa a bakinta! wani rikitaccen yanayi ta shiga wanda ta kasa fassarashi! kuka take ta gayyatowa amma fafur! yaki amsa gayyatarta idanuwan ma soyewa sukayi sai wani dan banzan zafi suke! jijiyar idon data kanta sun had’u sun d’aure guri daya wanda hakan ya janyo mata mugun ciwon kai irin na ‘bari guda, sama-sama takejin maganarsa a lokacin da yake bata umarnin tafiya.

Jiki a masifar sanyaye ta iya kai kanta dakinta, kawai ta zube kasan kafet tana janyo numfashi da kyar! ke kace ita din mai jinyya ce wacce ke fama da cutukan dake da ala’ka da numfashi.

Wai ace kamar ita jinin saurata gaba da baya, sannan kuma bata rasa komai ba na matantaka ba, Matar manya manyan mutane masu kudi da mu’kamai! aka dauketa kacokan aka bawa wani ma’kaskanci kyauta! mutumin data riga ta raina masa hankali, bashi da komai na rayuwa! bak’auye dashi, wanda ko direbanta be kai matsayi ba amma wai yau shi mahafinta ke ikirarin bawa auranta, koda wasa ba tayi tsammanin hakan na iya faruwa ba! har yanzu ta kasa gano dalilin da yasa mutane suke k’aunarsa! a’iya nazari da tunaninta, ta fahimci cewa jarumtarsa ce take kawai ke burge mutane…….Wannan shine babban dalilin da sanya mahaifinta yin sha’awar bashi ita a matsayin matar aurensa, tabbas kuwa idan ya sake akayi auran nan to zai gane shayi ruwa ne a hannunta, domin sai ta nuna masa bakin rijiya ba gurin wasan makaho bane, sam-sam! ba zata yarda wannan karan ya samu nasara a kanta ba, babu ruwanta da jarumtarsa! tunda a zahiri ta fishi komai, to dole shi zai rusana mata!!!!
TURKASHI!!

Tofah! yanzu za’a fara wasan馃槂 ko ya zaman auran nasu zai kasance oho? ni ban san ma me zance muku ba, amma dai muje zuwa…………..!

[/indeed-social-locker]

Previous page 1 2 3 4

Related Articles

Leave a Reply

Back to top button