GURBIN IDO

GURBIN IDO 66-70

          Zamowa yayi ta sauka qasan gadon,ya kewayo inda take facing,a nutse ya duqa gabanta ya lalubo hannunsa ya sanya cikin nasa,yatsunsu ya sarqafe waje guda ya kuma hade tafukan hannayensu waje daya,yasan koda ya buqaci ta kalleshi ba zata yi ba

“Am sorry,am really sorry angel,i don’t mean to hurt you,am out of my sense..ki yafemin” saukar kalamansa ga zuciyarta tamkar wani yayyafin ruwa yayi mata,kunya da nauyinsa da kuma ciwon da takeji ya hanata bude idanuwanta ko ta nuna masa tana jinsa,wani sashe na zuciyarta nason angizo mata tausayinsa,haquri yake bata don ya karbi haqqinsa?,ba fyade yayi mata ba,matarsa ce halak malak da musulunci ya mallaka masa,ya kuma bashi damar zuwa mata duk sanda yaso a kowanne irin yanayi,is he real ja’afar data sani?,gaba daya ya wani karaya yayi laushi?,ja’afar stubborn person sannan kuma Arrogant wasu lokutan,bashi da sauqi ko kadan ita shaida ce koda daga kan qannensa kuwa.

    Kwata kwata bashi da control a lokacin,tun daga bakinsa har zuwa zuciyarsa,kalaman neman afuwa ne ke fitowa a bakinsa,yana jin wami guiltiness a jikinsa,yana jin kamar yayi forcing dinta ne ko kuma ya aikata mata ba dai dai ba.

    Ja'afar din nada wata irin baiwa ta iya magana da kalamai,shi yasa sau tari anni kan ce

“Ubangiji shi yasan nufinsa da ya samyashi mara yawan magana,wala’alla hakan nada nasaba da baiwar iya magana da yake da ita”.

    Shanyayyun idanuwansa ya daga ya kalli agogon dake bedside bayan wani lokaci,dare ya fara nisa sosai,sai ya janyesu a hankali ya maida kanta,sannan ya miqa mata tafin hannunsa ya miqa mata

“Kiyimin wata alfarmar,ki taso na rakaki ki gyaran jikinki,nan din ya baci da yawa” ta jishi sarai,amma batasan ta inda zata fara tashi ba,na farko kunyarsa da takeji ta ninka ta baya sau dubu,na biyu kuma ciwon da takeji a qasanta da wanda dukka jikinta ke mata ta tabbatar bazai barta ta tashi din ba,sai tasa hannu a hankali tadan ture fuskarsa daya matso da ita dab da tata,sai a sannan taji zafin dake jikinsa har ya kusa fin nata,bai bata damar sakeyin tunani na biyu ba ya shammaceta ya dauketa cak,runtse idanunta tayi gam gam saboda motsatan da yayi ya fama mata mikin dake jikinta,duk da batace komai ba amma ta saki wani wahalallen numfashi

“Am sorry” ya fada a hankali sannan ya mannata da qirjinsa ya wuce toilet din da ita cikin riritawa da kuma kulawa,tamkar yana dauke da qwai.
[11/24, 10:10 PM] Safiyyatulkiram: 68

   Ruwan mai dumi ya hada mata cikin bathtub,bata da wani qarfin hanasa gasata don haka ba wani gardama ko yunqurin hanawar da tayi,saidai yadda yaga tana kuka gaba daya ya sake sanya masa tausayinta sosai,kukan da take ya tuna masa da shaheeda,sai ya sanyata a jikinsa sosai yana jin kamar itace,duk da cewa maimunatu ta fita jigata nesa ba kusa ba,son shaheeda a sannan daga shi har ita farin shiga ne,wasu abubuwan sai a hankali,amma maimunatu fa?,a matsayin qwararre yaje mata,baisan cewa cuta ya tarama gangar jikinsa ba sai yanzu,ya kuma juye mata dukka a jikinta,ashe duk tsahon shekarun yana da buqatuwa,amma damuwar da ya sanya cikin ranshi ya hana hakan tasiri,ya san cewa bai mata ta sauqi ba ko kadan,don haka bai hanata kuka ba,saidai kalmar

“Sannu,am sorry” har da ta kusa gajiya da jinta daga bakinsa.

Sai da ya gama gasata sosai sannan ya bude wancan ruwan ya tsiyaye tas,ya hada musu wa na wankan tsarki,ta dan samu qwarin jiki kadan tayi da kanta,bayan sun gama ya sake hada wani dai still da zasuyi wankan sabulu,sai kawai ya shige bathtub din ya jata cikin jikinsa,dumin ruwan yana ratsasu shida ita,lafewa tayi sosai cikin qirjinsa,lallausan gashinsa ya zame mata kamar matashi,sosai bugun zuciyarsa ke mata tasiri a jikinta,tana jin yadda yaketa sauke qananun ajiyar zuciya kamar yaron da yaci kuka ya qoshi,sai ta lumshe ido kawai tana jin wani sauyi da yake samun duniyarta.

Yaye bedsheet din yayi sanda suka fito,sai ya maida abun rufar a madadinsa,wata lallausar mini gown ya sanya mata,ya fidda sock’s doguwar socks cikin kayansa ya zura mata,sannan ya sake saka mata wata zip up hoodie jacket mai dogon hannu,don ya fuskanci itadinma zazzabi ne sosai a jikinta,shikam Three quater kawai ya zurawa jikinsa,ya sake rufesu da duvet ya sanyata cikin jikinsa sosai yayi mata rumfa, numfashinsu da dumin zazzabin dake jikkunansu suka fara gauraya da juna.

Dukkaninsu haka suka kwana da zazzabi me zafi,har gwara ja’afar gab da asuba nashi ya sauka sosai,nata dinne dai babu sauqi,don rawar sanyi takeyi sosai,ya sake kunne room heater ya kuma lullubeta da kyau amma a banza,dole ya dagata,ya zare mata dukka kayan dake jikinta,ya mannata da fatarshi suka samu good skin contact,nannauyar ajiyar zuciya ya sauke,don sake haduwar jikkunansu sake kunnashi ya soma yi,musamman tudun qirjinta da ya tokareshi da kyau,kai kace da gayya tayi hakan,numfashinsa ya fara canzawa tare da bugun zuciyarsa,ya lumshe idanunsa yana jin yadda take sauke numfashi a hankali cikin galabaita da gajiya,yana tausayinta,bazai iya sake tabata,taci wahalar daya kamata ace ya barta ta sake hutawa da kyau,da yaji abun yana neman fin qarfinsa,sai ya zare jikinsa daga nata bayan yaji zazzabin yadan sauka,ya sanya mata pillow,cikin bacci ta kama pillow din da hannunta da kyau,qaramin murmushi ya subuce masa,yadda tayin fuskarta a hade kamar idanuwanta biyu ya bashi dariya,ya gama saara mata wajen shagwaba da raaki,auta ce ko ‘yar fari?,baisan a good awanne ajin zai ajjiyeta ba,yadda ta qanqame pillow din ya tabbatar da idanuwanta biyu ba zata yarda tayi hakan ba.

Alwala ya shiga ya daura da ruwa me dumi,abun sallah ya shinfida,ya tsaya sosai akai yana fuskantar ubangijinsa,ya masa baiwa a rayuwa har karo biyu,a cikin wannan rintsin rayuwar da mata na gari ke tsada da wahala,duk kuwa da cewa duniya cike take da tarin mata birjik,amma ta aure wahala take,saidia shi din ya kebanceshi da baiwa ta musamman.

°°°°°°°°°sai data yi kusan minti biyar da farkawa amma bata motsa ba,a hankali take shaqar tattausan qamshin dake fita daga jikinta jacket din nashi da har yanzu itace a jikinta,qamshin da babu abinda yake tuna mata sai daren jiya,abubuwan da suka faru suka runga dawo mata,sai ta dinga jin komai kamar a mafarki,kwanyarta ta dinga tuno kalaman da bakinsa suka dinga furta mata,sai ta sauke ajiyar zuciya me nauyi,ta kasa kunnenta taji ko zataji motsinsa ta koma ta sake lafewa?,jin shuru ya tabbatar mata da baya dakin kwata kwata,don haka ta miqe ta zauna sosai tana kallon lokaci,qarfe kusan sha daya da rabi na rana,tun asuba data yi wuf a daddafe tayi sallarta ta koma bata sake farkawa ba sai yanzu.

     Zaune tayi tana qiyasta da yadda zata miqe,ko ina ciwo yake mata a jikinta,cinyoyinta kamar anyi ajiyar dutse,duk da ya ragu ba kamar daren jiya ba,sai ta yanke shawarar ta sake shiga bandakin ta hada ruwan zafi ta yiwa kanta yadda yayi mata jiya,tana zuro qafarta qafa taqi bata hadin kai,sai ta narke gaba daya zuciyarta ta karye,kada dai ace ya illatata gaba daya ba zata sake moruwa ba?,idan haka ya tabbata da wanne ido zata yima mutane bayani?,take qwalla ta cika mata idanuwa,ba dadewa kuma suka fara bin kuncinta,dai dai lokacin da ya turo qofar ya shigo.

       Fes fararen idanuwansa da suka sake wani haske suka sauka a kanta,yana sanye da wata hoodie jacket wine color da baqin wando,ya sauke hular a bayansa,sai tattausan baqin gashinsa sake sheqi cike a kansa,ya sake wani fresh dashi,jikinsa na fidda rikitaccen qamshin nan nasa.

       K'as tayi da kanta tana jin inama bata farka ba,yayin da murmushi ya subucewa fuskarsa,cikin zuciyarsa ya furta

“Yanzun ne ya kamata kiyi tsoro me dalili yarinya ba tsoron baya ba na sakalci da shagwaba” takowa yaci gaba dayi zuwa gabanta,yana ayyana yadda zai dasa zazzafar soyayyarsa a ranta,tunda ya fahimci ya ribatu da samun empty heart da bata taba daukan soyayya me zafi irin wadda yake buri ba,so yake tayi masa soyayyar da ba’a taba masa kwatankwacinta ba,yana buqatar ya samu qauna data ninka wadda shaheeda tayi masa,soyayyar da zata zama abar kwatance,ya riga da ya gama sallama mata rayuwarsa,saboda haka bayajin akwai wani abu da zai musu shamaki a tsakaninsu shi da ita.

        "Gudmorning moon" ya fada da wata murya dake cike da shauqi,shauqin da tunda ya tashi har ya fita ya dawo shine taf a zuciyarsa,wani irin memorable night da bazai taba shafewa a rayuwarsa ba muddin yana da rai

“Ina kwana?” Ta fada cikin girmamawa,bai amsa mata ba,sai ya duqa a gabanta,wata kima da daraja ta samu farat daya a wajensa,ba ita kadai ba,hatta anni a yanzun yana jinta fiye da yadda take a wajensa a baya,bare kuma ita maimunatun,hannayensa ya zura ta qasan fuskarta,sannan a hankali in a low sound yace

“Kwana na yana gurinki…..get up dear” fuskarta a narke ta tabe baki irin na mutumin dake shirin sakin kuka,sannan ta langabar da kanta gefe guda,ha fahimci tana son ce masa ba zata iya ba,amma baki ya gaza fada,sai kawai ya miqe a hankali,yasa hannu kamar daren jiyan dai a tausashe ya dauketa ya nufi toilet din da ita,yana tafe yana kallonta duk da ta cusa fuskarta a qirjinsa,da zata iya da tace masa ya sauketa,yanzun ma da ranar Allah sake kalleta zaiyi haihuwar daadarta?.

Bai sanyata dole kan cire kayanta ba,amma ya tsaya ya gasata kamar daxun,mai ciwo yaji dadin jikinta,sai ta fara son qwacewa,sai ya kamata suka antaya ciki gaba daya shi da ita,dole tayi luf,tun tana jin zafi har ruwan ya fara mata dadi,ya sake tara mata wani sannan ya fito ya barta don ta qarasa.

Manyan towel guda biyu tayi amfani dasu,daya tayi daurin qirji dashi,dayan ta lullube kanta ruf,baka ganin komai sai kwantacciyar sumar gaban kanta mai salki,yana tsaye gaba mirror yana kurbar coffee din da ya hado a hankali,ya bude idanuwansa a kan fuskarta.

Sosai yaga fuskartan itama tayi fresh,farinta kamar ya qaru ya kuma sirkuwa da jaja jaja,tsigar jikinsa ta zuba gaba daya,ya hadiye sauran ruwan coffee din daya kurba,sai ya dora cup din saman morrow din,ya nufota a inda take tsaye daga gefan qofar toilet din,tana ta karatun ta yadda zata shirya yana cikin dakin,da kuma kayan da zata saka wadanda ba zasu fidda tsiraicinta ba sosai.

Previous page 1 2 3 4 5 6Next page

Related Articles

Leave a Reply

Back to top button