HARIJI COMPLETENOVELS

HARIJI 21 AND 22

21&22

Oum Aphnan✍????

Ummi kam sukuti tayi da rai ta kasa ko cewa uffan ,Abun duniya ya haɗu ya cunkushe mata rai,yanzu meye mafita? Taje ta auri wannan qasurgumin alhajin ne ,ko kuwa ta zauna a gidansu ,gida me kama da gidan bariki? Ina mafitar yike,amma kuma yanda ta fuskanta akwai tarin ƙalibale a zaman auren ta da ƙuliya,duba ga yanda ta lura yina jinjina zaman kishinta da sauran matarsa ,ina mafita?
Jin shirun nata yayi yawa yasa ya ɗan yi murmudhi irin tasu na manya ,kafin yayi gyaran murya
“Zan baki dama ,ummi nasan wannan maganan zai kasance me girma a gareki duk da ke kika nema ,cikan ɗan mutunci kenan,so yanxu yau zanje wajen aminina sarkin ku,mugaisa zuwa anjima zan wuce abj…inkin gama shawara tsakanin yau da gobe ke har jibi ma ina sauraronki,amma kar ya wuce that range,promised?”
Jinjina masa kai tayi cikin duƙar da kai batason su haɗa ido dashi ,saboda tsananin kunyarsa da takeji.
Fakaitan idonta yayi ya saƙa mata rafan kuɗi guda ɗaya ƴan 1k a ƙarƙashin tabarman da ya zauna ,sannan ya ɗauko complementary card ɗinsa ya miƙa mata
“In akwai damuwa ,you can let me know,ina tsumayin kyakyawan hukunci daga gareki ummi,amma plz banson yayatawa cikin gari,just you’re mother is ok”
Jan guiwa tayi ta ƙaraso gabansa,a sanyaye ta ɗan sake sunkuyawa cikin sigar girmamawa ,sannan ta kar6i card ɗin tana masa godiya ,kamar wanda ya bata wani abu…
Bayan fitar ƙuliya ,saida taji wucewan motocinsa ,sannan ta miƙe a saluɓe kamar wanda ƙwai ya fashe mata aciki,tana ƙarewa motocin da suka doshi giggiftawa ta ƙofar gidansu ,wai wannan duk na mabiyan ƙuliyan nan ne da yazo wai yina sona! Anya ummi baki saka rayuwarki a masifa ba kuwa? Karfa kije kijawa kanki salalan tsiya ,ayi cinikin kanki,don ko an yanke kanki ƴan uwanki bazasu damu dake ba.
Cikin zancen zucinta ta naɗe tabarman ,tana bibbigewa a ƙasa don ƙuran ya fita,abun mamaki,kuɗi ta gani sababbi kwatakwal ƙulli ɗaya a ƙasa tsorone ya kamata ta kasa ɗauka,saidai ta zura wa kuɗin ido,a kuma daidai nan umma ta shigo gidan…
“Assalamu Alaikum ,yarinyata ɗiyar Albarka,ai naji labarin arzuƙin da ya raɓemu…”
Shiru tayi saboda ƙafarta da ya caki damin dubu ɗayan
“Nayi tuntuɓe da mazumunta na haƙiƙa…lallai nayi farar haihuwa naƙudarki bai faɗi abanza ba ” ta duƙa ta ɗauke kuɗin bakinta har kunne ta fara karkaɗa kuɗin tana cafewa tana musu rawa da waƙa
“…kuɗi abokan aiki ,kin gani ko ɗoyar arziƙi?
Kawai saita rungumeta ta fashe da kuka
“Ai ni Dama tun ranar da na haifeki nasan ban haifo talaka ba na ga sha tara na arzuƙa…Allah dai yatabbatar da,wannan abu”
Kinga idu haka ta watsa mata ba um,ba um um,wai uwa kenan

Uwar ɗaki ta shiga kurum ta rushe da kuka ta daga waya ta fara dialing numbobinsa da ta gani a jikin card ɗin
Sai dai abun takAici takira yafi a ƙirga ya ƙi ɗagawa…


Da gudu mai wada ya kinkimi uwale duk nauyinta ya cusata a drawer kayan matarsa,sannan ya kwashe kayanta ya cusa a ƙarkashin gado,yina ƙoƙarin maida wando ta turo ƙofar
Turus tayi cikin mamaki,ko ina a birkice,duk an yamitsa mata kan gado,gashi tsirara yajiƙe jagwab da zufa ,yina ganinta ya fara washe mata baki yina inda inda,da kame kamen magana ,wucesa tayi fuskarta a haɗe taje gaban madubi ta ɗauki pos ɗinta,har zata wuce sai taga wani yayyauƙan Ruwa akan bedsheet ɗinta mai kamada maniyyi,a hankali ta tako ta ɗage shi da yasha tana ƙarewa wajen kallo,ko shakka babu zina akayimun,akan gadona na sunna…
Juyowa tayi da nufin tayi masa masifa ,amma kawai taga ya haɗe rai kamar hadari
Dukda tsoronsa da ya tsirga mata bai hanata magana ba cikin muryar kuka²
Maiwada karuwa,har kan gadon sunnata!gadon da muke tarayyar aure dakai? Haba maiwada mai na gaza maka?in bana gamsar da kaine,wallahi na sahale maka kayi aure,amma don allh meye haka…
Katseta Yayi ,cikeda borin kunya “ke wata irin macece mai zargin tsiya,ba dama in yi wasa da zakari na ,sai kice zina!!! Ke ƙazafin zina wuya gareta yau ko tare da mace kika ganmu ,indai baki ganmu turmi da taɓarya ina cinta ba ,baki da hujja ,amma tunda kince inyi aure da bakinki,to ki sha kuruminki,zanyi,zo ki fice ki bani wuri ,kar hushin zuciya ya kaini ga ɓaɓɓallaki yanzun nan” girgiza kai tayi cikin ƙunar rai hawaye na ,gangaro mata ,a hankali ta taka gaban durowarta da nufin ta ɗebi kayanta,wani tsawa ya doka mata yayi Tsalle ya kange,durowan” me zaki ɗauka?” “kayana zan ƙara wanda na ɗiba ba zasu isheni ba “
“To ban amince ba,ke na ma rage maki kwanakin tafiyar ,kuma kina matsa min ince na fasa”
Sosai yike bata mamaki,kawai sai ta juya ta fita…binta ya dingayi a baya har ta fice get ɗin gidan,saida ya datse sannan ya sauke gauron ajiyar zuciya
Wai yau da na banu da taga uwale,amma tunda har ta bani izinin qara aure aikam ba Wanda ya dace in aura sai uwale don a gaskiya yarinyar nan ta had’u ,akwai ni’ima wai…wai ,carkwai mazakwai ,a take yaji alhajinsa ya cika masa wando ,da hanzari ya juya d’akin don ya fiddota daga drawer su koma network…
Hariji

Related Articles

Leave a Reply

Back to top button