JIDDATUL KHAIR COMPLETE HAUSA NOVELNOVELS

JIDDATUL KHAIR COMPLETE HAUSA NOVEL

Hansai ce xaune kan takalmanta da kawarta Zulai da ita ma ta xauna kan takalman nata a karkashin bishiyar wani tsakar gida, Mata ne sun fi talatin a d’an tsakar gidan, ko wacce da hijabinta yarkace yarkace, wasu da goyo wasu da ciki, Hansai tace “Anya Zulai xa mu samu ganin mutumin nan yau kuwa, ni d’an cinikin awaran yau ma nake ji, don wllh Bibalo ba yi xata yi ba ta gwammace in ma kwantai ne awaran yyi, nan gaba fa sai na koma xan fara tuya, ga layi kamar baxa a xo kanmu ba, to ko wacce da matsalarta a kugunta” Zulai ta gyara xama tace “Shi sa nace maki mu fito da sassafe Hansai, amma kika tsaya dafa awara, mutumin nan aiki yake kamar yankan wuka shi sa ake masa layi wllh, idan ba da asuba mutum ya shigo ba sai ya kai magariba ma bai gansa ba, don ma mutumin baya tashi sallah kenan” Hansai tace “Toh ko dai mu je mu dawo goben da asuba Zulai? kinga fa uban layin yaushe aka xo kanmu” Zulai tace “Kin ji ki, mu kashe kudin mota kusan dubu daya kice mu tafi mu dawo Hansai??” Hansai tace “To ni ya xance? Wllh kwantai awarata xata yi yau, Allah ma yasa ta yanyanka min in dai bibalo ce, kinga idan ya so gobe sai in sake xaran dubu daya cikin kudin awaran mu taho” Zulai ta mike tace “Toh shhkn, mu tafi” Mikewa Hansai tayi tana sa6a bak’in gyalenta da duk ya takure suka fito waje tana cewa “Ni dai fatana Allah ya sa na xo gun karshen wahalata” Zulai tace “Ahaf ai fada ma 6ata baki ne wllh, in dai kika saki kudi rass xai maki aiki bbu algus, kina xaune rana tsaka xaki ga Jiddah har gida kamar an korota, wnn ai karamin aiki ne a wajensa, shi fa mutumin nan har haukata mutane ance yana yi” Hansai ta sauke wani ajiyar xuciya tace “Ae ban san amfanin shegiyar yarinyar ba sai da ta tafi, ashe ita ce rufin asirina ban sani ba, gaskiya idan Allah ya dawo min da ita auren ma wllh baxata yi ba har ta mutu, tun bayan bacewarta har yau banyi cinikin awara da yafi na dubu biyu ba, shi ma da kyar, snn xan ce ma malamin ya sa mata bak’in jini yanda bbu wanda ma xai yi sha’awan aurenta a bar min a bata kawai” Zulai tace “Da dai ya fi wllh, kinga bbu ma saurayin balle yace xai aureta” A haka suka isa bakin titi Hansai tace “Allah dai ya kai mu goben, in sha Allahu komai ya xo min karshe, wahalata ta kare”

Abuturrab na tsaye balcony misalin karfe takwas na safe wayarsa kare a kunnensa yana sauraran wani abokinsa, sai da ya jira abokin ya kai aya snn yace “I thought xa a samu mata ne, in dai ba a samu matan ba kawai a bari, i will think of another alternative” Daga daya bangaren abokin nasa yace “Amma wa kake nema ma lesson teacher din?” Ya xauna saman kujeran dake balcony din yace “Wata daughter na ne” Abokin nasa me suna Farouq yace “Ohk in dai an samu matan i will let u know Capt, kasan maxan ne sun fi juriyan koyarwan” Abuturrab yace “Eh haka ne, nagode da kulawa” Daga haka suka yi sallama, ya koma parlor ya xauna, daukan wayarsa da yyi haske yyi, ya dinga kallon screen din ganin El-Basheer ke kiransa, it’s been a while da suka yi magana, duk da shine baya daukan kiran nasa, can dae ya daga ya kai kunne, daga daya bangaren El-Basheer yace “Sai aka yi yaya da baka daga kirana?” Abuturrab ya jinginar da kansa da kujera yace “How are you doing?” El-Basheer yace “Saboda baka da bayanin da xaka min kan auren da kayi ma kanka ne yasa baka picking call dina??” Abuturrab ya gyara xama yace “Babu xancen wannan auren ne yanxu, shi sa ma na samu kwarin gwiwan daga kiran ka” El-Basheer yace “Ohh really? amma few days ago mun yi magana da Ahmad kuma yace min kana gidan ka da matarka….” Abuturrab ya daure fuska yace “Matar da ya aura min?” El-Basheer yace “But wait…. On a serious note Captain don kaje ka yi ma kanka aure babu shawara da kowa shine kake ignoring mutane, why are u avoiding good frnds? mu baxa mu hanaka xama da matarka ba ae no matter who she is” Abuturrab yace “Look Bashir, am serious babu xancen wannan auren yanxu, kasan ni bana karya, i don’t have any god-damn wife now…. amma this is just between i nd u don ‘yan gida basu sani ba har ynxu” El-Basheer yace “Ban gane ba, sakinta kayi?” Abuturrab yace “Ba sa’ar aurena bace ita ae, kawai tsautsayi ne da kaddara ya fada min” El-Basheer yace “Then why are u still hiding it from people at home in har da gasken ka saketa?” Abuturrab yace “Bcos we are staying under same rood with her har ynxu, and Abba won’t take it likely if he finds out na saketa, i think we should change topic now dude….” El-Basheer yace “Anyway… Ina kaduna, turo min address din gidan naka, i will be leaving in two days time in sha Allah” Abuturrab yace “Really? Yaushe ka shigo, kuma me ka xo yi” El-Basheer yace “Forward to me ur address now” Abuturrab ya d’an yi shiru, sae kuma yace “Ohk” daga haka ya katse wayar….. Ya d’an yi jimm, bayan kusan 5 minutes kawai ya tura masa Address din sannan ya mike ya wuce sama, dakin Jiddah ya bude ya ganta tana faman shafa man gashi a dogon gashinta da ya cika ko ina na kanta, atamfa ce jikinta, ta daga kai tana kallonsa, fuskarsa bbu yabo bbu fallasa shi ma yake kallonta, a hankali tace “Ina kwana” yace “Idan da abinda xa ki yi a kasa ki sauka ynxu kiyi, xuwa anjima bana son ganin ki a kasa” Ita dai bata ce komai ba, ya juya ya bar bakin kofar. Mikewa tayi bayan tayi parking gashin ta saka hula ta sauka parlon, xaune ta gansa parlon yana rike da remote, ta sunkuyar da kanta ta wuce kitchen, dankali ta shiga ferewa ta soya da kwai, sannan ta fito kitchen din rike da plate din Irish da egg din, ya bi ta da ido ganin xata wuce sama yace “Ina shayin?” Shiru tayi bata ce komai ba, yace “Koma” Ba musu ta juya ta koma kitchen din ta sa ruwan xafi sannan ta hada shayin a cup ta kara fitowa kitchen din, still yana kallonta yace “Wani ruwan kike sha gidan nan?” Tana kallonsa tace “A bandaki nake sha, ko a pampon kitchen” Bude baki yyi yana kallonta with shock, can ya mike yace “Ruwan bandaki?” Sosai gabanta ya fadi ta fara komawa baya, ya lura da hakan gudun kar ta saki ruwan shayin hannunta tunda ya san ba setin kirki gareta ba, calmly yace “Je ki ajiye abun hannunki ki dawo” A sanyaye ta wuce sama bayan ta ajiye plate da cup din ta mike ta fito a sanyaye, lkci daya hawaye ya kawo idonta, tsaye ta gansa har sannan yana jiranta, ta makale jikin stairs bayan ta sauko cikin rawan murya tace “Gani” Juyawa yyi yana kallonta, ta sunkuyar da kanta da sauri, daga sama har kasa yake kallonta, riga da skirt na atamfa da ya kamata, babu abinda kayan ya boye na surarta, ya rungume hannunsa yace “Daga yau kada ki sake sa atamfa a gidana” Ta d’an kallesa, sae kuma ta kara sunkuyar da kanta, yace “Idan baki son Abayan da nake siyo maki kiyi yawo ba kaya kawai” Ita dai bata dago ba balle tace komai, yace “Sannan kika ce ruwan bandaki kike sha?” Ta marairaice ta girgixa masa kai, strictly yace “What??” Tace “Sae cikin dare ne nake shan na bandaki, amma da safe da rana da yamma na pampon kitchen nake sha” Gani tayi ya nufota ta juya da sauri xata koma sama yace “Allah idan kika motsa daga nan xan maki abinda ban ta6a maki ba, wato xan gaura maki mari” Kuka ta fara yi, tana hawa stairs din da daddaya da daddaya cikin rawan murya tace “Don Allah kayi hakuri” Yana isa ta fasa kara, ta durkushe wajen tace “Kayi hakuri don Allah” Bai karasa kusa da ita ba yace “Shi ruwan fridge din na waye?” Ta boye fuskarta tace “Naka ne” yace “Ni nace maki nawa ne?” Ta girgixa masa kai, yace “Toh daga yau kika sake shan ruwan pampo a gidan nan Allah sae na mareki” Ta gyada masa kai da sauri, yace “Tashi ki bar nan” mikewa tayi da sauri ta haura sama, sae a snn ta juya tana kallonsa a downstairs, yana tsaye yanda ta bar sa, da sauri ta shige dakinta. Bayan azahar El-Basheer ya iso gidan, Abuturrab ya fita ya shigo da shi, Abuturrab ya sakala hannu a kafadar cousin din nasa yana murmushi yace “The prince himself” El-Basheer na murmushi yace “It’s been long Captain….” sosai suke shige da Abuturrab sai dai ya fi Abuturrab din haske, don shi ya fi shige da larabawa wanda hakan ke nuna kilan shi din ruwa biyu ne…. El-Basheer na bin gidan da kallo bayan sun shigo yace “Everything seems perfect, sai dai unfortunately ba Aneesah ta fara shigowa gidan ba….” Abuturrab ya shafa sajensa kmr baxai ce komai ba, sae kuma yace “Kwanan nan xata shigo gidan in sha Allah, bikin Ahmad saura few weeks so, bayan bikinsa sai inyi ma su Abba magana….” El-Basheer ya shiga bin parlon da kallo yace “But wait…. Where is…. I mean the wife u married?” Abuturrab ya hade rai yace “Wacce wife din?” El-Basheer yace “Warce muka ji labarin ka aura ma kanka mana…” Abuturrab yace “Pls hakan na bata min rai wllh, Nace maka she isn’t my wife any longer” El-Basheer yace “Yes haka kace, but why not ka sanar ma kowa bbu auren??” Taku suka ji a stairs, Abuturrab ya saci kallon Stairs din da sauri, El-Basheer dai bai juya ba sae kallon Abuturrab yake yana jiran amsan sa Jiddah ta sakko walking slowly ta shigo parlon da ganin kasan a d’an tsorace take, Kallon Abuturrab dake kallonta tayi ganin irin kallon da yake mata ta d’an tsaya ta ki karasowa, El-Basheer ya juya ya kalli inda Abuturrab ke kallo, lkci daya Abuturrab ya mike, ta marairaice tana kallonsa tace “Kai ne kace in daina shan ruwan bandaki, wllh kishi nake ji” Fuska daure yace “Juya ki koma” Juyawa tayi da sauri ta koma sama, Sai a sannan ya koma ya xauna yana kallon El-Basheer da ya bi ta da kallo…..

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21 22 23 24 25 26 27 28 29 30 31 32 33 34 35 36 37 38 39 40Next page

Related Articles

Leave a Reply

Back to top button