NAFEESAT 1-END

NAFEESAT Page 1 to 10

Dafa kafaɗun sa da akayi shi ya dawo dashi hayyacin sa, Yusra ce tsaye kansa tana kallon sa, idan da sabo yaci ace sun saba da ganin Kakan nasu cikin wannan halin, kuma sun san da cewa ba komi yake saka sa a halin nan ba illa tuna Kakar su.

“Kaka har yanzu dai ka ƙi ka dena tuna wannan tsohuwar matar taka, har yaushe ne zaka cire ta arai ne kayi rayuwan ka cikin kwanciyar hankali? Mu nan mun ishe ka rayuwa ba sai ka tuna ta ba, me ake yi da tsohon Zuma bayan ga sabbin zuma? Don Allah ka dena ɓata time ɗin ka a kan ta”.

Hannu ya saka ya share hawayen yana murmushi yace, “Yusra kenan baza ki taɓa gane wa ba, amma kowa ya san da cewa tsohon zuma shi ne wanda ke magani, sannan ba’a iya manta shi ko wani hali mutum ya shiga, Ni Matata ta fiye min ku duk kan ku, idan da za’a bani zaɓi daku da ita in zaɓa, ita zan zaɓa in bar ku”.

Taɓe baki Yusra tayi tace, “to don baka zaɓe mu ba sai me Kaka? Our parents will vote for us because they love us.”

Kaka yace, “to naji ban ce kiyi min rashin kunya ba, said me to my room”.

“Da can Ni na ɗauko ka?”

Hararan ta yayi yace, “I have noticed that Yusra is jealous of my wife, but you will die. I will never love you. She is the only one who betrays me. kuma wlh idan baki gungura Ni kin mayar dani ɗaki na ba da Yayan ki zan haɗa ki, ke ce farko wacce zan kai ƙara wajen sa”.

Turo baki tayi ciki-ciki tace, “ka daɗe baka kai ɗin ba, in yaso sai ya kashe Ni kar ya bar Ni da rai”.

“What are you saying?” Kaka said looking at her 

“Me kuwa kaji na ce?” Tafaɗa tana huro hanci kafin ta soma tura sa

Murmushi Kaka yayi yace, “na san maganin ku dani kuke zan cen”.

Tana gungura sa cikin ɗakin sa ta fito tayi nasu part ɗin cike da haushin Kakan.

[5/21, 9:53 PM] Oummu Ɗahirah: ????????????????????????????????????????

             *FAMILY DOCTORS*

                         ????

????????????????????????????????????????

????????????????????????????

   *NAFEESAT RETURN*

????????????????????????????

*MALLAKAR:*

                 _NAFISAT ISMA’IL LAWAL_

*SARAUNIYAR TSOKANAR PERFECT*????????‍

*بسم الله الرحمن الرحيم*

*PERFECT WRITER’S ASSOCIATION*????

“`( WE AIN’T PERFECT BUT WE’RE ALWAYS, TRYING OUR BEST TO MOTIVATE AND ENTERTAIN OUR READERS ????)“`

/https://www.facebook.com/Perfect-writers-association-100452275039839/

               *P.W.A✍️*

*JIKAR LAWALI CE*✍️

*Wattpad: UmmuDahirah*????

         

_Godiya ta tabbata ga Allah me kowa me komi, tsira da aminci su tabbata ga shugaban mu Annabi Muhammad Sallallahu alaihi Wasallam, Allah Nagode maka da kabani daman rubuta wannan littafin, ????????ya Allah kabani ikon rubuta abinda zai amfani al.umma ameen._

       *EPISODE Two*

         Da shigan Yusra parlourn su ta sami Hajiya zaune tana kallo, ƙarisawa tayi ta zauna kusa da ita tana ci gaba da cunno baki gaba

Da ido Hajiya taraka ta dashi kana tace, “Ke dawa? zaki shigo min parlour Babu sallama?”

Yusra kallon Hajiya tayi har a lokacin fuska a turɓune tace, “it’s Kaka and I, wai cewa yayi zai haɗa ni da Ya Usman idan ya dawo”.

Tsaki Hajiya taja tana hararan ta tace, “ai maganin ku kenan tunda baku da kunya, idan ya haɗa ku dashi sai ku dawo hankalin ku”.

Yusra kamar za tayi kuka tace, “to Hajiya ba kakan mu bane menene in mun yi wasa dashi?”

“It’s up to you. Get up and go to Zainab’s house. I’ve been waiting for you for a long time. tun ɗazu ta kira Ni a waya kuma na neme ki sama da ƙasa ban ganki ba, sai ki kwana acan in yaso gobe kun taho tare”.

Miƙe wa Yusra tayi ta nufi hanyan ɗakin ta, har ta kusa shiga Hajiyan ta kira ta, dakata wa tayi ta juyo tana kallon ta bayan da ta’amsa

“Ki shiga ɗaki na ki ɗauko Flower kwata biyar ki tafi dashi, nima sai kuyi min nawa don bani da lokaci aiyukan za suyi min yawa, cincin ɗin na kwata biyu kaɗai za kuyi min”.

“To”. Yusra tace hakan tana wuce wa ɗakin Hajiyan.

            _*****_

        “Calm down, what can I tell you? Shakira, kin san Buri na shi ne In ga ranan da za’a ce mun fi kowa a wannan familyn, I want to see the future of the  *AL’AMEEN FAMILY HOSPITAL* back under us. wannan dalilin ne yasaka na saka wa Baffa sunan Kakan ku, kuma dalilin ne yasaka na matsa wa Abban ku yabar Ni na koma makaranta na zama Likita, I know that one day my dream will come true. ”

Shakira looked at her mother and said, “Hajja, how do you think this hospital will be ours alone? Kar ki manta fa Familyn mu babba ne kuma kowa yana da gado idan har Kaka akace ya mutu, sannan taya kike tunanin sunan Ya Baffa zai taimaka mana don samun Asibitin nan?”

Hajja Fatu smiled and said, “Hmm, I know what I am thinking. Please keep your eyes peeled. Insha’Allah sai mahaifin ku ya gaji asibitin nan, sai mun fi kowa fice a cikin asibitin nan, sannan sunan Baffa da na saka don ina so ne nan gaba koda bayan ran Kaka ya zamana shi ke juya Hospital ɗin, ma’ana kowa yayi tunanin sunan ɗana ne sannan a manta da kakan ku, Ni a ganina hakan zai yi sauƙin zama namu”.

Shiru Shakira tayi tana kallon ta sai kuma ta kwashe da dariya

Hajja Fatu dake faman kallon ta baki hangame tace, “Ke ban son iskanci! Why are you laughing like that?”

Wlh Hajja you laughed at me, wai taya ma kike tunanin Jika zai mallaki Hospital ɗin Kaka idan har don kin saka sunan sa? Bayan kin san da cewa ABBU ma sunan Kakan yaci, to ki faɗa min da ɗa da jika wanne mutane za su yi tunanin Hospital nashi ne?”

“Hmm ai fata nake yi sannan cewa nayi ina so kowa ya ɗauka cewa Al’ameen ɗina ne aka saka, kin ga Ni da Abban ku da ke da Baffa duk muna aiki a cikin asibitin, don haka nake so nan gaba asibitin ya zamto na mu, ke dai kawai ki mayar da hankalin ki da zaran akace kun soma aiki, duk abinda baki fahimta ba kizo waje na ki sanar dani kinji?”

Gyaɗa kanta Shakira tayi tana kallon uwar nata

“Now call me Baffa and we will talk to him.”

“Ok”.

Tashi Shakira tayi ta nufi corridor’n da zai sada ta da ɗakin Yayan nata.

        *****

         The next morning gidan Doctor Al’ameen sosai ya cika da mutane ƴan uwa, Hajiya Ikram da Hajiya LAILA har sun iso da iyalan su, haka ma su Aunty Zainab da Aunty Zulaiha, nan da nan gidan ya rincaɓe da hayaniya sai shirye-shiryen abubuwan da za’a yi suke yi.

…….. ……. ……. ……. ….

        Baƙar Mota ce ta sanyo kai cikin ƙaton gidan da ya tsaru iya tsaruwa, kai da gani kasan mamallakin gidan ba ƙaramin hamshaƙin me kuɗi bane, sosai gidan yake da girma da yalwa Two upstairs ne, idan ka shiga haraban gidan yana da yalwa sosai wanda aƙalla zai cinye motoci kusan ashirin, sai kuma Part ɗin masu aiki da akayi daban, da akwai Garden a ta bayan gidan tare da abubuwan more rayuwa, the home of Doctor Al’ameen and his family.

Motar na packing wata mata da a ƙalla baza ta wuce 45years ba ta fito, sai kuma wata matashiyar budurwa da shekarun ta ba zai fi 25years ba itama ta fito, tana sanye ne da wani Abaya green colour Wanda a gefe da gefen rigan an sanya ratsin blue, sai kwalliyan Flower da akayi da stone masu matuƙar ƙyalƙyali daga sama har ƙasa, tayi Rolling kanta da ɗankwalin Abayan da ya kasance Blue, sai ta saka wani ɗan siririn farin glass Wanda ya ƙara fito da zallan kyawun ta da kwarjinin ta; tare da fito da manyan idanuwan ta da ƙwayan idanun suka kasance sky Green, kallo ɗaya idan kayi mata zaka san da cewa ba ƙaramar mugun haɗuwa tayi ba, fara ce sosai tana da kyawun fuska tare da ƙira me kyau, sai dai ta kasance siririya ce sosai kuma matsakaiciya, kana kallon ta kasan cewa za tayi yanga ne da yawa, don ko maganar ta da tafiyan ta idan tayi zaka san cewa Nature ɗinta ne hakan

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9Next page

Related Articles

Leave a Reply

Back to top button