NAFEESAT 1-END

NAFEESAT Page 1 to 10

Dariya Shakira tayi tace, “kai wlh Ƴanmata yau kin bala’in burge Ni, ashe zaki iya kai ƙaran Ya Usman? Shin wai ina tsoron da kike mishi ya tafi?”

Taɓe baki Ɗahira tayi kana tace, “ai dama ɗan hakin da ka raina wataran shi ke tsole maka ido, kema da kanki kin faɗa da ba yanzu ba, Ɗahiran Da; da na yanzu sun sha banban”.

Miƙe wa Shakira tayi tana sakin murmushi tace, “gaskiya ne ƴan mata, don yanzu ba lokacin Da damuke yara bane, yanzu mu ɗin DOCTORS ne manyan yara, kinga kuwa baza mu iya ɗaukan raini ba, wlh kin burge Ni amma Ni kam ba na tunanin zan iya fa”.

“Dama ai ke matsoraciya ce, Ni dai ɗauko min in tafi Mama jira na take yi”.

Drower Shakira ta buɗe ta soma kwaso mata Books ɗin tana cewa, “hmm baza ki gane bane, Ya Usman ya wuce gaban kwatance, wlh ko wacce mace idan har zata haɗu dashi sai dai ta kalle shi da idon soyayya amma ba faɗa ba, kwarjinin sa da kyawun sa tare da isa da izzar sa su kansu sun ishe ka, ina matuƙar shakkan Ya Usman kuma ba na son abinda zai haɗa ni dashi da har zai saka mu saka ƙafan wando ɗaya dashi, but ke kam nasan kashin ki ya bushe wlh don ba ƙyale ki zai yi ba, ya lafiyan Kura ma bare ace tayi hauka, uhmm ke dai kawai ki guji ranan haɗuwan ku”.

Ɗahira takowa tayi tazo gaban ta ta soma kwashe Littafan tana zubawa a leda, batare da tabi ta maganarta ba tace, “Ni kin ga tafiya na ba ni da lokacin ku daga ke har shi ɗin”.

Tajuya tayi ƙofa zata fice, dai-dai lokacin da Yusra ta turo ƙofan ta shigo suka kalli juna suka ɗauke kai sannan ko wacce ta wuce

ƙarisowa Yusra tayi kusa da Shakira dake zaune bakin gado; itama ta zauna gefen ta tana cewa, “wai ya maganar mu na zuwa shopping yaushe za mu je?”

Shakira tace, “ki bari a kawo mana Mota mana, kin ga sai muje aciki ko ya kika ce? Don Ni wlh bazan fita a tsohuwar mota ba, gwara muje muna tsole idanun Gayu”

Dariya Yusra tayi tana cewa, “shegiya inda ba’a ce za’a ba mu ba fa? ya za kiyi dole ki fita a ciki”.

“Uhm baza ki gane bane amma dai gwara mu bari sai ranan Sunday ɗin muje, kin san har gidan su Marcy za muje ranan wlh”.

Hannu Yusra ta bata suka kashe tana cewa, “gaskiya ne Tawan ai wlh yanzu ma kika tuna min da ita, ahh ai dole ne ma muje, kai wlh har kin sani na ƙosa ranan tazo, uhmm Allah ya kai mu har na hango irin wulaƙancin da zanyi”.

Sai suka kwashe da dariya suna sake tafawa

Shakira tace, “kin san yanzu muka gama hiran ki da mutumiyar taki?”

“Wace kenan?” Yusra ta tambaye ta cike da rashin fahimta

“Wace kika sani ban da Ɗahira, Ni na rasa meyasaka ba ta ƙaunar ki duk sanda zamu zauna sai tayi maganar ki, abun mamakin ma yanda tayi ta zagin Ya Usman anan wajen, uhmm duk wai akan waya”.

Ɗaure fuska Yusra tayi tace, “wlh yarinyan nan akwai ranan da zan cire mutunci mu goge raini, ni fa na gaji da kawo miñ ƙarar ta da kike yi a kaina tana zagi na, wlh zan je inji dalilin da ya saka take zagi na”. Tana ƙarike maganar ta miƙe da ninyar tafiya

Shakira tayi saurin riƙe ta tana cewa, “ke kuma meye haka? Yau ta soma zagin ki da zaki damu? Wlh idan baki iya kama ɓarawo ba sai ya kama ki, yanzu idan kika je sai kice mata mene? ki bari duk ranan da kika kama ta tana maganar naki sai ki ɗau mataki amma ba yanzu ba, kuma menene na damuwa tunda gani ina faɗa miki komi?”.

Yusra dake tsaye har yanzu kallon Shakira take yi har ta dire aya kana ta ɗaura da nata, “But wlh today I have to tell Hajiya everything, dama ina ɓoye mata ne ban son hankalin ta ya tashi”. Daga haka ta juya ta fice fuuu kamar ana tura ta

Tana fita Shakira ta saki murmushi tana cewa, “Dama haka nake so gwara kije ki faɗa ma Hajiyar ki don ta ƙara ƙullatan ta, shegiya Ni wlh ba ƙaunar Ɗahiran nan nake yi ba, da wani idanu sai kace na fataken dare, kai ko a turawan ma bana tunanin akwai masu irin wannan idanun..”

Ƙaran buɗe ƙofarta shi ya katse mata maganar ta, tayi saurin juyawa tana kallon me shigowa, ganin Mahaifiyar ta ne ya saka ta sauke ajiyan zuciya har da dafe ƙirji

ƙarisowa wajen ta Hajja Fatu tayi tana kallon ta tace, “What happened to Yusra leaving here in a rage?”

Dariya Shakira ta kwashe dashi tana cewa, “me kuwa zai faru in ba zugo ta da nayi ita da Ɗahira ba, ai yau sosai na fusata ta don har maganar Ya Usman nayi mata, yanzun ma Mahaifiyar ta za taje ta sanar ma wa”.

Sai kuma ta kuma kwashe wa da dariya tana cewa, “wlh da ma maganar ya koma kunnen Ya Usman inga yanda zai yi ƙulun kubura da ita”.

Hajja Fatu itama dariyan tayi tace, “yauwa ɗiyar albarka ai gwara da kika zugo ta ɗin, idan ta sanar wa mahaifiyar ta na san yanzu gaba ta soma ita da A’isha, hmmm mu zuba yanzu ma aka soma”.

Wannan shine halayyan Shakira da Mahaifiyar ta, ko ince ƙudurun su akan Ɗahira da Maman ta

Yusra da Ɗahira basu shiri tun farko; sakamakon zigin da Shakira take yi a tsakanin su batare da sun sani ba, ita Yusra akwai zafin kai da saurin fushi, tun farko dama ba wani shiri suke yi da Ɗahira ba, hakan yasaka Shakira ta samu dama take ƙara wa abun wuta, duk idan suka zauna tare da Yusra sai ta ce mata, “Ɗahira ta zage ta, ko tayi gulmanta”, hakan yasaka Yusra ko magana ta dena ma Ɗahira kullum kallon ta da abun take yi, ita kuma Ɗahira dama ba me son shiga harkan da babu ruwan ta bane bare kuma idan ana mata wulaƙanci, don haka itama ɗin sai ta fita harkan ta a cewar ta “duk ranan da ta sauko ta dena ɗaga mata kai sai su ci gaba da mutunci” kuma dama Ɗahira tana ganin itace Babba babu yanda za’a yi ta zauna tana bin ƙanwar ta don kawai tana son su shirya tunda ta san bata yi mata komi ba, duk da su huɗun ba wani tazara ne a tsakanin su ba duk sa’annin juna ne, sai dai Ɗahira aka fara haifa yanzu haka shekarun ta 25years and Two Month, sai Shakira me shekaru 25years cif-cif, sai kuma Yusra me 24years and 8month, maraban su da Fadila kwana goma ne

Gaba ɗaya ahalin gidan halayyan su ɗaya ne na jijji da kai da nuna taƙama, sai dai na wasu ya fi na wasu ne musamman ma Usman da ya fi kowa a gidan, kuma hakan a jinin su yake.

_Hmm now the game has started because there is a lot cakwakiya  in this family, just go ahead and follow me and suburbuɗo me a comment to get more Post.

[5/22, 10:47 AM] Oummu Ɗahirah: ????????????????????????????????????????

                   *FAMILY DOCTORS*

                              ????

????????????????????????????????????????

????????????????????????????

  *NAFEESAT RETURN*

????????????????????????????

*MALLAKAR:*

_NAFISAT ISMA’IL LAWAL_

*SARAUNIYAR TSOKANAR PERFECT*????????‍

*بسم الله الرحمن الرحيم*

*PERFECT WRITER’S ASSOCIATION*????

“`( WE AIN’T PERFECT BUT WE’RE ALWAYS, TRYING OUR BEST TO MOTIVATE AND ENTERTAIN OUR READERS ????)“`

/https://www.facebook.com/Perfect-writers-association-100452275039839/

               *P.W.A✍️*

*JIKAR LAWALI CE*✍️

*Wattpad: UmmuDahirah*????

*SADAUKARWA*

_Na sadaukar ga Family na gaba ɗaya. *GOMA’S FAMILY*_

    *EPISODE Seven*

          Sallama tayi ta turo ƙofar ta shigo, Aunty Amarya dake zaune gefen gado ta’amsa mata tana kallon ta

ƙarisowa tayi ta zauna kusa da ita tare da miƙa mata ledan tana cewa, “Ga shi Mama”.

Bata amsa ba tace da ita, “Where have you been waiting for me?”

Ɗahira tace, “na je wajen Shakira amsan Littafaina ne”.

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9Next page

Related Articles

Leave a Reply

Back to top button