NAFEESAT 1-END

NAFEESAT Page 1 to 10

    *EPISODE Three*

        A hankali ta sanya hannun ta ta soma jan gemun sa

Hakan yasaka ya buɗe idanuwan sa ya sauke a kan ta, murmushi yayi yana kallon ta yace, “Ni dama nasan babu wanda zai min haka sai ke, When did you come back?”

Murmusawa tayi tana janye hannun ta tace, “yanzu babu daɗewa”.

Tashi zaune yayi yana faɗin “To ya me jikin da fatan ya samu sauƙi?”

Sai da ta dawo kusa dashi kana tace, “Alhmadulillah Kakus suna gaishe ku kowa da kowa”.

“Mun gode muna amsawa”.

“My Kakus miss you so much”.

Murmushi Kaka yayi yana ɗaura hannun sa a kan ta yace, “nima haka Matata, You have left me alone I miss you, kin bar ni da waɗannan yaran mara su kunya masu ido a tsakar ka ko hiran basu taya ni”.

Dariyan ta me kyau ta saki tana jingina kanta jikin Kakan tace, “Kakana kenan! don’t worry, I’ll be back. hira har sai ka gaji daji, akwai labarin ma da na samo maka”.

“Well I hear you tell me”.

Ƙofar da aka turo ne ya sanya Ɗahira rufe bakin ta without saying a word. Big Dady ne tare da Abbu suka shigo da sallama, amsa musu su kayi yayinda Ɗahira ta tashi da sauri ta nufi Mahaifin nata ta rungume shi tana faɗin

“Abbu na”.

Murmushi yayi yana shafo kanta yace, “to ya kin dawo ko zaki fara?”

Dariya tayi tace, “I’m really missing you, Abbu.” 

Sai kuma ta sake shi, Then she hugging Big Daddy and said, “Daddy, I’m the only one.”

Shafo kanta yayi shima yana smiled and said, “my daughter when did you come back?”

“Now Dady”.

“To ya me jikin yaji sauƙi dai ko?”

Gyaɗa masa kai tayi tana faɗin “Alhmadulillah”.

Big Dady yace, “madalla haka ake so”.

Sannan ya juya yana kallon Kaka yace, “Dad, we’re here to talk about new products da za’a shigo dasu.”

Kaka yace, “to shikenan”.

Abbu da ya samu wuri ya zauna yace, “Mamana bamu wuri za muyi magana”.

Big Dady yace, “a’a barta kawai ta zauna”.

Murmushi Ɗahira tayi tana kallon Big Dad tace, “bari dai inje in dawo Dady, because I have some things to do”.

“Well shikenan Daughter”.

Daga nan fita tayi ta rufo musu ƙofa, She did not go back to the General Parlor. Sai tabi ta wani Corridor da zai sada ta da Part ɗin su, tana cikin tafiya ta hangi Baffa ya taho shima ɗin, yayi shigan nan nasa na ɗamewa irin shigan wizaye, kansa babu hula sai kwantaccen gashin kansa da ya sha askin zamani, sosai yayi masa kyau ya sake fito da kyawun sa ainun, hannun sa Sigari ne yake sha, shima yana hango ta ya matse Sigarin a hannun sa ya kashe kana ya tura shi cikin aljihu

Murmushi ya saki lokacin da ya’iso wajen ta yana faɗin “Oyoyo My Lovely sister”. Ya nufe ta da ninyan Hugging ɗin ta

Tayi saurin ja da baya tana murmusawa tace, “Oyoyo My Lovely Brother”.

Sai ya ɓata fuska and looked at her and said, “Why don’t you let me hug you?”

Still tana murmusawa tace, “ka san ba na so fa”.

Ɗage kafaɗa yayi yana cewa, “ok to ya Hanya? kin dawo ko ki neme Ni, kinsan nayi missing ɗin ki sosai”.

Ɗan huro hanci tayi tana kallon sa, sai kuma ta ɓata fuska tace, “Ya Baffa kamar warin Sigari nake ji?”

Waro idanu yayi yace, “Really?”

Sai ta harare sa tana cewa, “Where is our promise?”

He smiled and touched his forehead and said, “Sorry Sis ban saɓa miki ba ai”.

“I don’t agree, ga shi kana bani haƙuri”.

“Da gaske my Sister na Dena sha, sai dai idan hancin ki ya juyo miki wani warin daban”.

Kallon sa kawai take yi, sai kuma tace, “ok I Believe You”.

He smiled and said, “so where are you now?”

“I’ll go back to our Part”.

“Mu je ki taya ni hira mana”.

Girgiza kanta tayi tace, “No grave until tomorrow, now I have something to do.”

Baffa haɗe hannayen sa yayi yana kallon ta yace, “Please Mana my sis”.

Ɗahira ɗan kawar da kanta tayi

ya sake cewa, “Please kinji?”

“Ok Muje”.

Murmushi ya sakar mata yace, “yauwa ko ke fa”.

Itama murmushin tayi tabi bayan sa suka jera suka nufi cikin gidan.

Suna shiga cikin ɗakin sa tabi ɗakin da kallo tana yamutsa fuska, sai kuma ta kalle sa tace, “Wai Ya Baffa kwana nawa ɗakin nan be ga shara ba?”

Shafo kansa yayi yana kallon ta shima yace, “wlh kin san ban da lokaci kuma ga shi ke kinje anguwa, and na saka Shakira ita kuma kin san halin ta ba wani iyawa tayi ba” 

Gyaɗa kanta tayi kana tace, “ok bari in gyara maka yanzu ko”.

“Ok my sis let me help you”.

Zuwa tayi ta soma kakkaɓe gadon yana tayata suna hira, bayan sun gama suka share ɗakin tare da wanke Toilet ɗin ɗakin, ita tayi Moping shi kuma ya koma kan sofa ya zauna yana latsa wayan sa

Bayan ta gama ta dawo kan hannun kujeran ta zauna tana kallon sa tace, “Yaya na gama maka bari in wuce sashin mu kar Mama taji ni shiru”.

Ok my sister, Thank you so much, that’s why I love you so much coz you are so kind”.

She smiled and said, “Yayana kenan! I love you more than anyone else in this house. Kaima kana da kirki.”

Tashi tayi tana nufan saman drower ta ɗau wayan ta tadawo tana kallon sa da shima ya kafe ta da nashi idanun, murmushi tayi masa tace, “Na tafi Yaya”.

Miƙewa yayi ya rako ta har bakin ƙofa kana ya koma ciki yana zama saman kujera tare da aza kansa ya kwantar kan hannun yana lumshe idanun sa, murmushi kawai yake saki yana tuna ɗan kyakykyawar fuskarta, sosai yake matuƙar son ƙanwar tasa, kuma so na aure, burin sa kawai a rayuwa yaga ranan da zai mallaki Ɗahira a matsayin matar sa domin tayi masa tako ina, sai dai har yanzu ya kasa samun ƙwarin gwiwar tunkaran ta yace mata yana son ta

Ɗahira tana da wani irin kwarjini da zai yi wuya namiji ya tunkare ta da zancen so, shiyasaka tun tasowan ta bata taɓa yin saurayi ba duk da tana da farin jini sosai na mutane, a lokacin da suka je ABU Zaria karatun su na Degree yawancin Friends ɗin ta maza ne, kuma duk acikin su babu wanda ba so yake kawo sa wajenta ba but basu iya gaya mata.

Shima haka Baffa ya daɗe yana ƙaunar ta yana dakon son ta Amma har yanzu be iya sanar da ita ba, kuma duk abinda tace “yayi ko ya bari” yana bari, shi ɗin ma’abocin shan Sigari ne don wani lokacin har Alcohol yake korawa, amma babu wanda ya sani a gidan sai ita kaɗai kasancewar tana yawan zuwa ɗakin sa koda ba ya nan, wani lokacin sai tazo ta kwanta tayi barcin ta, yawan kusancin su dashi ne ya saka tasan wannan sirrin nasa, kuma tun sanda tace ya dena sha ya dena, sai dai har yanzu Sigari ne be dena gaba ɗaya ba, amma idan har zata gani zai yi ƙoƙarin ɓoyewa.

        *WASHE GARI*

         Ranan ne ya kasance ranan Walima, kowa idan ka gani agidan cikin farin ciki yake, sosai gidan ya sake cika sai hada-hada ake yi, har mutanen Maiduguri tushen su kenan duk sun hallaro, duk girman gidan nan sai da aka cika sa da mutane

Ƙarfe 02:00pm. Aka soma tafiya *AL’AMEEN FAMILY HOSPITAL* kasancewar acan ne za’ayi taron, haka motoci manya-manya suke ta jidan mutane suna kai su.

_Kar ku manta da_

*Share*

*Comments*

*Vote*

*Like.*

[5/21, 9:54 PM] Oummu Ɗahirah: ????????????????????????????????????????

            *FAMILY DOCTORS*

                       ????

????????????????????????????????????????

????????????????????????????

 *NAFEESAT RETURN*

????????????????????????????

*MALLAKAR:*

_NAFISAT ISMA’IL LAWAL_

*SARAUNIYAR TSOKANAR PERFECT*????????‍

*بسم الله الرحمن الرحيم*

*PERFECT WRITER’S ASSOCIATION*????

“`( WE AIN’T PERFECT BUT WE’RE ALWAYS, TRYING OUR BEST TO MOTIVATE AND ENTERTAIN OUR READERS ????)“`

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9Next page

Related Articles

Leave a Reply

Back to top button