NAFEESAT 1-END

NAFEESAT Page 1 to 10

Ita kuwa Ɗahira sauke idanun ta kan ƙafan sa tayi tana kallon wayan yayinda taji hawaye sun ciko mata idanu sabida tsananin baƙin ciki da yazo mata iya wuya, still ɗago kanta tayi tana kallon sa cike da zallan tsana da ya nuna a cikin ƙwayan idanun nata

shi kuma hawayen da ya gani a idanun nata shi ya saka shi jin wani farin ciki tare da sanyi a ransa, magana ce a bakin sa yake son faɗa mata amma girman kai da Izza sun hana sa buɗe bakin, illa juyawa da yayi ya nufi ƙofa ya buɗe ya shige..

      Ƙaran rufe ƙofan ne ya saka ta ƙyafta idanun ta wanda hakan ne yasa hawayen ta daman zubowa suka sauka kan kuncin ta, ahankali ta sake mayar da idanun ta kan wayanta da ya gama murƙushe ta duk screan ɗin ya farfashe babu kyan gani, wasu zafafan hawayen ne suka soma sintiri a face ɗin ta, tayi saurin saka hannu ta soma sharewa domin baza ta bama kanta daman nuna raunin ta kan shi ba, dole ne ta nuna masa yanzu ba irin da bane, dole ta nuna masa ba ta tsoron sa, kuma duk abinda yayi mata BASHI ne ya ɗauka dole sai ya biya, don haka ɗaukan wayan tayi ta nufi ciki itama da sauri.

_To fa nan ake yinta, bari muga me zai faru?_

_kar ku manta ku suburbuɗo min Comments ta hakan ne zai bani daman ƙara muku yawan Page._

Plz

*Share and Vote.*

[5/21, 9:54 PM] Oummu Ɗahirah: ????????????????????????????????????????

             *FAMILY DOCTORS*

                         ????

????????????????????????????????????????

????????????????????????????

   *NAFEESAT RETURN*

????????????????????????????

*MALLAKAR:*

                 _NAFISAT ISMA’IL LAWAL_

*SARAUNIYAR TSOKANAR PERFECT* ????????‍

*بسم الله الرحمن الرحيم*

*PERFECT WRITER’S ASSOCIATION*????

“`( WE AIN’T PERFECT BUT WE’RE ALWAYS, TRYING OUR BEST TO MOTIVATE AND ENTERTAIN OUR READERS ????)“`

/https://www.facebook.com/Perfect-writers-association-100452275039839/

               *P.W.A✍️*

*JIKAR LAWALI CE*✍️

*Wattpad: UmmuDahirah*????

*SADAUKARWA*

_Na sadaukar ga Family na gaba ɗaya. *GOMA’S FAMILY*_

       . *EPISODE Five*

          Da shigan ta darect wajen Kaka ta nufa, ta sami waje kan hannun kujeran dake kusa da Wheel chair ɗin sa ta zauna tana sauke kai ƙasa

“Matata lafiya wa ya taɓa min ke?”

Abinda ya saka yayi mata tambayar ya santa idan har tazo wuri dole sai ta tsokane shi, ƙa’ida ne sai taja masa gemu kafin ta nemi wurin zama

Ɗago kanta tayi tana kallon sa sai kuma ta soma wurwurga idanun ta tana kallon mutanen wurin da duk suka nutsu suna kallon ta, a kan Usman dake zaune kusa da Abbun ta ta sauke idanu, yayin da shi kuwa wayan sa yake latsawa ko sanin Allah yayi ruwanta be yi ba

“Tell me my wife. I can’t calm down idan ban san abin da ke damun ki ba?”

Dawo da idanun ta kan Kaka tayi cike da marairaice fuska tace, “Kaka Ya Usman ne ya fasa min waya, kuma ya saka ƙafa ya tattaka shi da gangar”.

Kaka salati yayi yana kallon wayan dake hannun ta kana ya mayar da idanun sa kan Usman da har yanzu yaƙi ya ɗago kansa duk da yana jin abinda ake yi, shi har a lakocin mamakin yarinyan yake yi ainun, “yaushe har ta samu ƙwarin gwiwar da har zata kawo ƙarar sa? Lallai yarinyan nan dole ya koya mata hankali”.

“Fodio, why did you break my wife’s phone?”

Shiru yayi batare da ya ɗago kan sa ba, kuma be dena latsa wayan ba

“Kai ba magana ake maka ba? Are you crazy? Uban meyasa ka fasa mata waya? Ka dawo kenan zaka soma takura mata ko?” Big Dady yayi maganar a zafafe yana kallon sa

Sai a lokacin ne Usman ya ɗago kai fuskar nan a ɗaure yana kallon su, sai dai be iya cewa komi ba

Abba yace, “miƙo wayan mu gani uwata”.

Miƙa masa wayan tayi, ya’amsa yana juyawa sai ya ɗago yana kallon ta yace, “Agarin ya yafasa miki wayan?”

“Mun yi karo ne shine ya faɗi, da nayi masa magana shi ne ya dawo ya tattaka min da takalmin sa”.

“It’s your fault, why did you talk to him then? Stop following her shit please”. Abbu yayi maganar yana amsan wayan daga hannun Abba and put it aside

Big Dady said, “why doesn’t she talk and break her phone?”

Sai kuma ya mayar da kallon sa ga Usman ɗin yace, “Make sure you buy her her phone and pay for it, idan ba haka ba zan mummunan saɓa maka kana jina ko?”

Gyaɗa kan sa kawai Usman yayi yana kallon Ɗahira da kanta ke ƙasa, kawai tunani yake yi a ransa abinda zai yi mata idan har ta shigo hannun sa

Kaka ne yace, “ya isa haka Lawal (Noor), karka ɗau abinda zafi haka mana, yanzu mu mayar da hankali kan abinda ya tara mu. Alhmadulillah and Allah show us this time to see my grandchildren finish their studies and become doctors now, don haka na tara ku in sanar muku da Albishir da na tanadar muku”.

Murmushi yayi yana kallon su ɗaya bayan ɗaya kana yaci gaba da cewa, “Zuwa nan da Sunday motocin ku da na siya muku za su iso sai kowa ya zaɓi wanda yake so, wannan shi ne kyauta na a gare ku, sannan ina jan hankalin ku ku mayar da hankali wajen aikin ku, abinda ya kai ku shi za kuyi ba na son wasa, 

May God help you all. May God bless you.”

Duk ka parlour’n suka amsa da ameen ban da Usman da har yanzu latsa wayan sa yake yi, nan ɗaya bayan ɗaya suka yi ta mishi godiya kana ya kalli Usman yace

“Kai kuma Fodio, the opportunity I have given you is enough. dole ne ka dawo Nigeria kaci gaba da aiki a asibitin mu, domin baza mu zira idanu ace kana can kana ma Nasara aiki suna ƙaruwa mu nan ka bar mu haka ba”.

Usman da ya ɗago kansa yana kallon Kaka, a karo na farko yace, “wai Kaka meyasaka kake son takura min ne? I don’t want to work here. I want to..”

Be dire maganar ba Big Dady ya daka masa tsawa, hakan yasaka shi yin shiru yana kawar da kai still fuskan sa ba walwala

“Umarni ake baka ba shawara ba ka ajiye aiki ka dawo nan kaci gaba, karka sake mu ƙara ja’inja da kai”. Big Dady ya faɗi maganar da kakkausar murya

Murmushi Kaka yayi yace, “ka bar shi nace Lawal; ba na son kana nuna masa zafi, ai ba cewa yayi bazai dawo ba, abi shi a sannu, kowa zai iya tafiya. idan kuma da me magana ko ƙorafi akan wani abu sai yayi magana”.

Kafin Kaka ya rufe baki Usman yayi saurin tashi ya fice, haka sauran ma su kayi ta tatashi suna ficewa ya rage daga Kaka sai su Big Dady

               *****

      Hajja Fatu ce ta shigo parlour’n Hajiya da sallama

Hajiya wacce ke zaune a parlour ta’amsa mata sallaman sannan tayi mata maraba

Zama Hajja Fatu tayi tana kallon Hajiya da murmushi a face ɗin ta tace, “Oh ashe haka abu ya faru? Na zo miki jajen abinda Ɗahira tayi wa Usman ne, gaskiya bata kyauta ba”.

Hajiya tace, “Haka ne. amma shima da laifin sa ai, da be taka mata wayan ba baza ta kawo ƙarar sa ba”.

Ɗan taɓe baki Hajja Fatu tayi tace, “eh Haka ne kamar yanda ki kace, amma abinda tayi ai be kamata ba, wannan ai kamar tana so ta haɗa Ɗa da uba ne, ko ba kya ganin yanda Mahaifin sa ya nuna fushi dashi? Kuma da ba haka yake nuna masa ba, don Ni kai na shaida ce wajen ƙaunar da yake masa, amma a kan ta ya rufe idanu ya suburbuɗa masa faɗa a gaban ƙannin sa, wannan abun ba yi bane, idan ma uwarta take zugo ta ai zamu gani”.

Shiru Hajiya tayi tana sauraron maganganun Hajja Fatu, kuma da alamun sosai zancen yake shigan ta duba da yanda fuskarta ta sauya, domin abinda aka yi wa ɗan nata dama be mata daɗi ba, amma kuma maganganun Hajja ya sake saka ta taji haushi matuƙa

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9Next page

Related Articles

Leave a Reply

Back to top button