NAFEESAT Page 1 to 10

Ita kuwa Hajja Fatu ganin haka ya saka ta sakin wani shu’umin murmushi tana cewa, “Ai sai haƙuri amma dai na san yarinyan nan yanzu hure mata kunne ake yi, ada ai ba ta yin haka duk kuwa da cewa yana dukan ta, amma yanzu tunda ana son haɗa sa da ubansa ai an koya mata yanda zata riƙa kawo ƙarar sa, kin ga hakan zai sa Mahaifin sa ya riƙa fushi dashi”.
Hajiya kallon Hajja Fatu tayi don da alamun kalaman nata sun gama ratsa ta sosai tace, “nima naga alamun haka Hajja, sai dai ko ma wa ya koya mata da duk abinda suke nufi da ɗana sai dai ya koma kan su, babu wanda ya’isa ya shiga tsakanin ɗana da mahaifin sa, dole ne ma in ja masa kunne babu ruwan sa da ita tun wuri ya fita harkan ta, ba na son abinda zai saka mu sami saɓani, domin akan ɗana babu abinda bazan iyaba, kowa ya san da cewa ina matuƙar ƙaunar sa; don zan iya yin komi akan sa”.
Ajiyan zuciya Hajja Fatu ta saki tana kallon Hajiyan da alamun nuna damuwa a fuskarta tace, “gaskiya ne Hajiya, gwara dai ayi wa tufkan hanci tun kafin magana tasha banban, Allah ya kyauta gaba to, Ni bari in tashi na tafi”.
“To shikenan Nagode sai nima na leƙo”. Cewar Hajiya da murmushi a fuskarta
Tashi Hajja tayi ta nufi ƙofa ta fice tare da barin Hajiya cikin tunani. Tana fita ta saki wani shu’umin murmushi fuskarta cike da farin ciki, dama abinda take so kenan kuma tana ganin da alamu tarkon ta ya fara kamawa, taku ɗaya zuwa biyu tayi ta tsaya tana juyowa ta kalli ƙofar parlour’n Hajiya, a fili ta furta
“Now the game has started. If I am Hajja Fatu, I will open the heart of everyone in the house. I will make everyone hate you, A’ishah. tare da ƴarkin da kika ƙwallafa rai a kan ta, zan maye gurbin zuciyar kowa da ƙauna ta a ran shi, zaki san kin shigo cikin Familyn da ba na ki ba, mu zuba dani dake..”
“Hajja ke da wace ce zaku zuba? Me tayi miki?”
Da sauri Hajja ta juyo tana kallon ta, wani irin bugawa zuciyar ta tayi, nan da nan tsoro da fargaba ya ɗarsu a cikin zuciyarta har bata san sanda ta fiddo idanu waje ba suna kallon kallo..
_Hhhh to Fans shin wa kuke tunanin wacce Hajja ta gani haka har ta sorata ainun?_
_karku manta da Comments, domin comments ɗin ku shi ke saka na ƙara yawan post._
[5/21, 10:02 PM] Oummu Ɗahirah: ????????????????????????????????????????
*FAMILY DOCTORS*
????
????????????????????????????????????????
????????????????????????????
*NAFEESAT RETURN*
????????????????????????????
*MALLAKAR:*
_NAFISAT ISMA’IL LAWAL_
*SARAUNIYAR TSOKANAR PERFECT* ????????
*بسم الله الرحمن الرحيم*
*PERFECT WRITER’S ASSOCIATION*????
“`( WE AIN’T PERFECT BUT WE’RE ALWAYS, TRYING OUR BEST TO MOTIVATE AND ENTERTAIN OUR READERS ????)“`
/https://www.facebook.com/Perfect-writers-association-100452275039839/
*P.W.A✍️*
*JIKAR LAWALI CE*✍️
*Wattpad: UmmuDahirah*????
*SADAUKARWA*
_Na sadaukar ga Family na gaba ɗaya. *GOMA’S FAMILY*_
*TUNATARWA*
“`Manzon Allah mai tsira da aminci, ya yi mana bayani a kan sallah da abin da Bawa yake iya samu. Cewa ya yi, “Yana yiwuwa mutum ya kawo sallah ga baki ɗayan ta amma a ba shi lada wadda ba ta wuce sudusin ta ko ushurin ta ba.” Abin da yasa haka kuwa shi ne rashin nutsuwa cikin sallah.
Allah yasa mu dace.“`
*EPISODE Six*
Murmushi Hajja Fatu ta ƙirƙiro cikin tsananin ruɗewa da son ɓoye halin da take ciki tace, “am..uhmm babu, auhm Ni da wata ƙawata ce da taci amana ta”. Taƙarishe maganar tana sake sakin murmushi
Ɗahira kuwa kallon ta kawai take yi, domin kuwa duk abinda ta faɗa ta riga taji, sai dai tayi tsananin mamaki da al’ajabin abinda Hajja Fatu take faɗa akan Mahaifiyar ta da ita kanta. ita ma ɗin nuna mata tayi kamar bata ji maganar nata ba illa sakin murmushi da tayi tace, “But Hajja, why don’t you forgive her? I don’t see the point in keeping a person in mind.”
Wani irin ajiyan zuciya Hajja Fatu ta saki jin cewa ta yarda da abinda ta faɗa mata, hakan na nufin bata ji maganar da tayi ba kenan, murmushi ta sake ƙirƙirowa tace, “ƴata baza ki gane zafin cin amana ba, amma tunda kin ce in yafe ai Ni me iya yafe mata ne, nima sai yanzu na gane hakan be da wani amfani muyi ta sa’insa akan abinda be kai ya kawo ba”.
Sai kuma ta sauya akalan maganar da tambayarta “ina zaki je kika yo nan?”
Ɗahira said, “I will reply to Mamana’s message,”
Gyaɗa kanta Hajja Fatu tayi tace, “ok”.
Sannan ta juya ta tafi batare da ta sake furta komi ba
Ɗahira kuwa bin bayan ta tayi da kallo har sanda ta ƙule wa ganin ta, maganganun Hajjan ne suka dawo mata
“What does that mean?” Tafaɗa aranta tana sake zurfafa a tunani
Tabbas ta san akwai abinda Hajja ke shiryawa akan Mahaifiyar ta, sai dai kuma duk yanda za’a yi baza ta taɓa bari taci nasara ba, tun farko dama tasan Hajja Fatu ba ta ƙaunar Mahaifiyar ta, Kasancewar ita A’isha wato Aunty Amarya Asalin ta ƴar Soba ce a ƙaramar hukuman Zaria, karatu ya kawo ta Kaduna tana zaune wajen auntyn ta, to anan ne Mijinta Al’ameen ya ganta har ya’aure ta, tun sanda aka kawo ta gidan Hajja Fatu ta nuna ba ta ƙaunarta kuma take son nuna ita ɗin bare ce acikin su, sabida alokacin ƙanwarta dama ta daɗe tana ƙaunar Al’ameen wato Abbu, to hakan ya saka ta ɗau alwashin sai ta fid da Aunty Amarya a cikin gidan ko ta halin ƙaƙa, don a cewarta tunda ƙanwarta bata same shi ba duk a dalilinta, to, itama sai ta rasa shi
Numfashi Ɗahira ta sauke tana ɗauke kanta daga kallon Hanyan da Hajja Fatu tabi, ko kaɗan baza ta so ta faɗa wa Mahaifiyarta wannan maganar ba, domin ta san hankalin ta zai tashi matuƙa, sai dai zata dage da taya ta da addu’a duk wani wanda ke binta da sharri ya koma masa
takawa tayi ta shige Parlour’n Hajiya da sallama
Hajiya da har yanzu take zaune tana tunanin maganar Hajja Fatu, ta ɗago kanta tana bin Ɗahira da kallo, fuska babu walwala ta’amsa mata sallaman
Ita kuwa Ɗahira ƙarisowa tayi ta zauna a kujera tana kallon Hajiya tace, “Hajiya sannu da hutawa”.
“Yauwa”. Hajiya ta’amsa ataƙaice tana sake tamke fuska
Sosai Ɗahira tayi mamakin halin da Hajiya ta nuna mata, domin ta san ta mace ce me fara’a, kuma suna ɗasawa da ita ainun, tayi mamaki da ganin sauyawar fuskarta amma kuma sai ta dangana hakan da ko wani abun ne ke damunta, don ko kaɗan bata yi tunanin abinda ya faru ɗazu ba
“Hajiya dama Mama ce tace inzo in amsar mata saƙo”.
Miƙe wa Hajiya tayi batare da ta tanka mata ba ta shige ɗaki, sai gata ta fito da leda ta miƙa mata
Amsa Ɗahira tayi cike da girmamawa ta tashi ta fice
Ita kuwa Hajiya rakata tayi da harara tana jan tsaki
Ɗahira da har ta fice sai da tajiyo sautin tsakin, hakan yasaka taja ta tsaya tana kallon ƙofar, nan take kuwa abinda ya faru ɗazu ya dawo mata kwanya “kenan Hajiya tana fushi da ita ne saboda abinda ya faru ɗazu?” Ta tambayi zuciyarta cike da mamaki, taɓe bakin ta kawai tayi tajuya tayi tafiyar ta, Part ɗin Hajja Fatu ta shige, babu kowa a parlour sai ta nufi ɗakin Shakira kanta tsaye, tana isa ta tura ƙofar ta shiga da sallama a bakin ta
Shakira dake zaune gaban mirror tana gyara kayan kwalliyan ta ta ɗago da kanta tana kallon ta, sai kuma ta saki murmushi tana cewa, “ƴan mata adon gari me aka kawo min ne?”
Ƙarisawa kusa da ita Ɗahira tayi tana jingina da bango tace, “a’a Ni babu abinda na kawo miki, amsa dai nazo yi, kin san yanzu wayata ta samu matsala shiyasa zaki haɗo min kan Littafaina in tafi dasu”.