NAFEESAT Page 1 to 10

Gyaɗa kai kawai tayi tana ɗaukan ɗan kitt ɗin dake gaban ta ta miƙa mata tace, “ga shi Abbun ki ya ce in baki kyautar sa ne”.
Saurin miƙa hannu Ɗahira tayi ta’amsa tana buɗe wa, murmushi ta saki ganin danƙareriyar sarƙan gwal kana ta kalli Maman nata tace, “ina Abbu ɗin?”
“Ya fita, Ni kuma ki riƙe wannan ledan da kika amso sai ki ɗinka”.
Dariyan farin ciki Ɗahira ta saki kana tayi mata godiya tare da nuna murnan ta a fili, buɗe ledan tayi ta soma duba wa, atamfofi ne guda biyu masu kyan gaske sai kuma Material guda ɗaya
“Mama Nagode sosai Allah ya saka da alheri”.
Murmushi Aunty Amarya tayi tana kallon tilon ƴartan cike da so da ƙauna tace, “ki dena godiya tunda ya zama dole ne mu yi miki”.
Daga nan miƙe wa Ɗahira tayi zata fita, Aunty Amarya ta kira ta ta dawo, sake zama tayi inda ta tashi tana kallon Mamar nata
Ita kuwa cikin sauya fuska tace, “Meyasaka kika kai ƙarar Usman don ya fasa miki waya?”
Shiru Ɗahira tayi tana sunkuyar da kai ƙasa
“I don’t want to hear it again, do I?”
Gyaɗa kanta tayi
“Tashi ki je Allah miki albarka”.
Sai da ta’amsa da “ameen”. Before leaving
Tana fita ɗakin su ta shiga
Fadila na kan gadon ta tana latsa waya sai faman doka murmushi take yi, idan za’a rantse ma bata san da shigowan ta ba
ita kuwa Direct wajen gadon ta ta nufa ta’ajiye kayan hannun ta, fiddo kayan tayi tana gani, har ta gama dubawan ta’adana sannan ta dawo ta zauna ta ciro Books ɗin ta zube su saman gadon
dai-dai lokacin ne Fadila ta ɗago kai ta kalle ta, nan idanunta suka faɗa kan NOVELS ɗin dake zube kan gado, da sauri ta’ajiye wayan ta tataso ta nufo wajen ta tana zama kan gadon;, ta saka hannu ta ɗauki ɗaya daga cikin litattafan, cikin farin ciki ta ɗago tana kallon Ɗahira tace, “Hey Sis Where did you get this book?”
Ɗahira da take riƙe da ɗaya daga cikin litattafan me suna *BARRISTER IBRAHIM KHALIL* tana dubawa ta bata amsa, “It’s mine”.
“Wayyo Allah wlh na daɗe ina neman Littafin *RAUDHAN* nan amma ban samu ba, Please ki ara min in karan ta, sosai nake son Littafan *JIKAR LAWAL GOMA* amma na rasa inda zan samu, ko da naje kasuwa nayi yawo but Allah be sa na samu ba”.
Ajiye Littafin hannun ta tayi tana kallon ta tace, “Ni kam samun littafan ta ba ya min wuya, idan kina so sai ki bari adawo min da wayata in saka ki group ɗinta”.
Murmushi Fadila tayi tace, “Thanks Sis, kai wlh har naji daɗi! na ƙosa naga ƙarshen abinda zai faru tsakanin *RAUDHA* da Captain Rayyan”.
Miƙe wa Ɗahira tayi ta shige Toilet ta bar Fadila nan zaune har ta soma karanta NOVELS ɗin.
_If you need my Book so contact me on this Number 07065334256._
⚫⚫⚫⚫⚫⚫⚫⚫⚫⚫
Tun sanda ya fito General parlour ya nufi part ɗin su, cikin ɗakin sa ya shiga ya rufo ƙofan, Direct gaban Royal Bed ɗin sa ya nufa ya zauna a bakin gadon, har a lokacin be saki fuskar sa ba sai dai baza ka iya gane a halin da yake ciki ba, ya jima ahaka yayi shiru yana tunani sannan daga baya ya miƙe ya soma haɗa kayan sa cikin trolly, bayan ya gama Toilet ya shiga be jima ba ya fito ya bar ɗakin, yana fito wa parlour ya tarda Hajiya zaune tana kallo, a hankali ya taka ya’iso wajen ta ya sami waje kan sofa ya zauna
Hajiya kallon sa tayi tace, “Dama kana ciki?”
Gyaɗa mata kai kawai yayi yana mayar da idanun sa kan t.v
kallon sa Hajiya take yi tana karantan yanayin sa, duk da ta san halin ɗan nata ba kasafai kake gane alƙibilan sa ba, kiran sunan sa tayi
hakan ya saka ya juyo yana kallon ta sai dai be amsa mata ba
“Ina son ka fita harkan yarinyan nan ba na son ko kaɗan wani abu ya sake haɗa ku, yanzu ba kamar Da bane”.
Usman kallon ta yake yi a rashin fahimta, don be fahimci abinda take magana akai ba, sai dai kuma bazai iya buɗe baki ya tambaye ta ba
itama Hajiya ganin yayi shiru be ce komi ba; sai taci gaba da kallon ta don ta san ba amsa mata zai yi ba
sai da yaja lokaci a zaune a wajen be yi abinda ya kawo sa ba kafin daga bisani daƙyar ya buɗe baki yace,”I’m leaving”.
Kallon sa tayi batare da ta gane me yake nufi ba
hakan ya saka ya kawar da kai yana ɗan motsa bakin sa
“Ina zaka je?” Ta tambaye sa don ita bata gane inda za shi ba
In a calm and proud voice he said, “Turkey”.
Hajiya tace, “kamar ya zaka koma kai da kace sai kayi kwana biyu?”
Shiru yayi
“Are you talking quietly?”
“I have a job there.”
Shiru tayi tana kallon sa, shi kuwa ya kau da kai don be san ma su haɗa idanu
“Shikenan amma ka bari sai gobe sai ka tafi, yau dai ka haƙura”.
Be ce komi ba ya miƙe ya nufi ɗakin sa, yayinda ita kuma taraka sa da kallo tana mamakin irin halin sa
Shi kuwa yana shiga keey ɗin mota ya ɗauka ya fito ya zo ya wuce Hajiya still tana bin sa da kallo
parcking space ya nufa ya ɗau motar sa ya bar gidan.
⚫⚫⚫⚫⚫⚫⚫⚫⚫⚫
*WASHE GARI*
Wajen ƙarfe 05:30pm. Na yamma Ɗahira na zaune saman gadon ta tana karatun Novel *(JARUMAI na Jikar Lawal Goma).*
Fadil ne ya shigo ɗakin kamar an hankaɗo shi ko sallama, wajen ta ya nufa yana dariya yace, “Aunty, are you still here?”
Kallon sa kawai take yi batare da ta furta komi ba
sai ya sake sakin dariya yana cewa, “Yaya Usman ne ya bani saƙo in baki shi ne naje ɗakin Kaka neman ki ashe kina nan kina faman karatun Novel, Wai me kuke karantawa aciki ne?” Yaƙarike maganar yana kai hannun sa kan littafin
Buge hannun sa tayi tana hararan sa tace, “kai ba na son iskanci; Yi abun da ya kawo ka ka ware”.
Miƙa mata Leda yayi tare da wayan ta da aka farfasa yace, “ga kwaraɓaɓɓiyan wayan ki inji Kaka”.
Bata ce komi ba ta’amsa tana ajiye wa taci gaba da karatun ta
shi kuma Fadil tsayawa yayi yaƙi tafiya yana kallon ta
Ɗago kyawawan idanuwan ta tayi ta maida kansa, “What’s stopping me?”
“Aunty Ɗahira ki bani wannan wayan mana tunda kin ga kin samu wata”.
“What are you talking about now?” Ɗahira ta tambaye sa still tana kallon sa
Ɗan turo baki yayi yace, “ai gaskiya na faɗa ba kwaraɓaɓɓiyan ba ce?”
Hannu tasa da ninyan riƙo sa yayi saurin matsawa ya nufi ƙofa yana mata dariya
“Idan na kama ka Fadil..” Sai tayi shiru tana ƙwafa sannan taci gaba da karatun ta
Fadil yace, “to inzo in amsa Aunty?”
Bata kula sa ba Amma kuma sosai ya’ishe ta; don ita ba ta son hayaniya da yawan surutu, shi kuma Fadil ya san ba ta so shiyasaka yaƙi tafiya sai magana yake mata yana son ya ƙule ta, ko kuma taji haushi ta ba shi wayan ya tafi, sai da ya gaji don kan shi sannan ya fice batare da ta sake kula sa ba
Yana fita ta’ajiye Littafin don tunda ya fara surutun sa ta dena fahimtar Book ɗin, ledan ta buɗe ta ciro wayan dake cikin kwali, sai da ta gama jujjuya ta ahaka kafin ta taɓe baki tana buɗe wayan, the same irin wayan ta ne, Simcard ɗin ta ta cire ta saka a ciki sannan ta kunna tare da gyara zaman ta tana murmushi ta soma latsa wayan.
Share this
[ad_2]