RAUDHA Page 11 to 20

Bayan malamin ya fita sai takifa kanta saman Deks tana fid da numfashi.
Rash ce taƙariso wajen tare da yin sallama tazauna
Hakan yasa RAUDHAN tatashi zaune tana kallon ta batare da ta amsa mata sallaman ba
Murmushi Rash tayi tace “yau kin yi late baki samu Lecture ɗaya ba”.
Gyaɗa mata kai tayi sai dai bata yi magana ba
Izuwa yanzu Rash ta gane halin RAUDHAN ba wai ta cika son magana bane, don kafin tayi magana sau ɗaya ta baka amsa sau ba adadi da kanta
Jakan ta tabuɗe taciro mata wani leda me ruwan zuma babba, tamiƙa mata tana faɗin
“To ga saƙon ki an siyo”.
Hannu RAUDHA tasaka ta’amsa tana jin farin ciki sosai aranta, ba ƙaramin wahaltuwa tayi ba a kwanakin nan da bata ji ta a sama ba, ta rigada ta saba shiyasa ko kaɗan bata jindaɗi in bata sha ba
“Thank you”. Tafaɗa tana murmushin ta me kyau
Itama Rash murmushin tayi tace “to yanzu ki tashi mu je capteria mu ci abinci yunwa nake ji”.
Bata ce mata komi ba tamiƙe suka fito, duk a cikin su babu wanda yay tunanin zuwa sallah tunda babu me damuwa dashi
Capterian suka wuce suka yi odaring abinci, bayan sun gama RAUDHA tabiya suka fito.
“Kai mutumina ga fa yarinyan can da nake baka labari ita da Rash”. Maan yafaɗa yana kallon su Rash ɗin dake doso wajen su
Kyakykyawar saurayin dake zaune saman mota yakai duban sa inda Maan ke kallo, nan yazuba idanun sa kan RAUDHA ko ƙyafta wa baya yi
“Maan wannan yarinyan kuma fa?” Yatambayi Maan batare da ya ɗauke idanun sa kan ta ba
“Nima dai bansani ba yanda kaganta haka na ganta, ai na faɗa maka ƴar Class ɗin su Rash ne kasan ta da jaye-jaye, itace wacce kakawo mata kaya”.
“Haba dai amma fa ta haɗu, kace irin mu ce?” Yayi maganar yana shafa gemun sa still idanun sa akan ta
Dariya Maan yayi yace “kai dai maye ne Zen..”
Shiru yayi be ƙarisa maganar ba ganin har sun kawo setting su, hakan yasa yasauya maganar da kiran Rash
Sai a lokacin Rash tahange su, don haka takalli RAUDHA tace “ƙawata muje wajen su mana, kinga wancan shine wanda yake kawo mana wannan kayan, muje mu gaisa sai mu wuce Class”.
RAUDHA bata ce mata komi ba illa bin ta da tayi suka isa wajen su
Dasauri Zen yasauko daga kan motan yana faɗin “Rash wannan Babe ɗin fa?”
Kallon sa Rash tayi
Yakashe mata idanu
Sai tayi dariya tace “friend ɗina ce Her name is RAUDHA”.
Sai takalli RAUDHAN kafin tace “Ƙawata wannan shine Zen Abokin Maan ne”.
Idanu RAUDHA tasanya masa kamar yanda shima yazuba mata yana murmushi, ƙare masa kallo kawai take yi da shigan da yayi
Yana sanye da farar riga me yankakken hannu, sai wando jeans blue colour duk an yayyanka shi as kwalliya, yasha askin zamani me tugaggen gashi, wuyan sa kuma sarƙoƙi ne wajen biyar da me Cross a ciki, hakan yatabbatar mata shi ɗin Christian ne
Bata ce komi ba illa ɗauke kanta da tayi
“Hi”. Yafaɗa yana miƙa mata hannu alamun su gaisa
Idanun ta tamaida kansa kafin tabi hannun da kallo, sai kuma tace “Hi”. Batare da ta bashi hannun ba
Murmushi yayi yakalli Rash yace “ƙawar ki fa tayi min tana da kyau sosai, zan zo tazama friend ɗina”.
Dariya Rash tayi tace “kaga ga ita nan sai kafaɗa mata”.
Kallon ta yayi yace “ko zamu iya zama friend RAUDHA? I Like you”.
Fuska ta yamutsa kafin takalli Rash sai kuma tajuya tawuce batare da tabashi amsa ba
Hakan yasa Rash tayi saurin ce musu “byee na tafi sai mun haɗu anjima”. Tay gaba itama
Zen be ɗauke kai akanta ba har sanda suka ɓace ma ganin sa, sai yasauke ajiyan zuciya yana kallon Maan dake mishi magana amma be ji ba
“Guy wlh yarinyan tayi sai ta zama nawa, dole ne duk yanda za’a yi nahaɗa alaƙa da ita”.
Maan yay dariya yace “cabb wlh kana da aiki Zen, Nima Tunda naganta taburge Ni but bana tunanin fa ƴar hannu ce that’s why ban ƙwallafa raina ba”.
Kallon sa Zen yayi yace “kai kasan halina duk yarinyan da tayi min dole ne sai ta shiga hannu na, bare kuma wannan Babe ɗin da tahaɗu sosai, wlh dole ne sai ta shiga cikin mu, kai dai kabari zamu san abun yi”.
“Allah ko mutumina?”
Jinjina masa kai Zen yayi alamun tabbaci kafin yace “kazuba idanu kagani”.
Ihu Maan yasaki yana bashi hannu suka kashe
“Yanzu mu je gida, anjima idan mun haɗu da Rash sai mu tattauna”. Zen yay maganan yana nufan ƙofan me zaman banza yabuɗe yashige
Shima Maan motan yashiga yaja suka bar wajen.
Kasancewar Lecture ɗaya yarage musu biyu zuwa uku, suna gama wa RAUDHA tayi gida.
????????????????????????
Rash asalin sunan ta Rashida ne, a Kano suke ita da Mahaifiyar ta da ƙannin ta biyu, kasancewar mahaifin su ya daɗe da rasuwa sai yazamana Maman su ke ci dasu tunda basu da me taimaka musu ƴan uwa duk sun guje su
Tun tasowar Rash idanuwan ta suka buɗe da son kuɗi, kasancewar ta yarinya me son ƙarya shiyasa take bin gidajen yaran masu kuɗi tana ƙulla alaƙa dasu, a haka har tasoma haɗuwa da maza ɓata gari tana ba da kanta gare su suna biyan ta
Wannan abun duk da take yi Maman ta bata taɓa hana ta ba, a ganin ta yarinyan ta tayi farin jinin da tun kafin tagama girma samari na mata rubibi, hakan baya damun ta tunda tana kawo mata kuɗi duk abinda tasamu tare suke ci
Abu yayi gaba har takai ta kawo ma Rash ita ke ci da ƴan gidan su, ta zama tantiriyar karuwa wanda duk wani namiji me ji da kansa ya san Rash saboda shaharan ta
Maman ta da tagano ainihin abinda take yi take samun kuɗi hakan be wani ɗaga mata hankali ba, tunda dai tasan wannan shine zamanin, babu me baka sai idan ka ba shi wani abun da zai ƙaru da kai, sai dai ko kaɗan bata yarda ƙannin Rash sun faɗa wannan mummunan rayuwan ba, a ganin ta Rash ita kaɗai ta isa tawanke musu matsalan rayuwan su, ta yarda ta sadaukar da rayuwan Rash don su samu kuɗin da zasu ci gaba da rayuwa gaba ɗayan su, a cewar ta idan sun gama samun abinda suke so sai taja ƴar ta ajiki ta tuba takoma ga Allah sannan tayi mata aure shikenan komi ya wuce hmmm.
Rash babu inda bata bin namiji in dai zai biya ta kuɗi, ana haka suka haɗu da Sulaiman wanda a yanzu suke kiran sa da Maan, a salin haɗuwar su a social media suka haɗu wanda har yakai ga sun haɗu a fili
Maan ɗan Jigawa ne, babu laifi iyayen sa suna da kuɗi sosai, duk abinda yake so suna masa sabida shi kaɗai ne suka haifa
Tun fara abotan su soyayya tashiga tsakanin su, Rash tunda taga hoton Maan takamu da tsananin ƙaunar sa sabida babu ƙarya Maan yana da matuƙar kyau, irin kyakykyawar bafulatanin nan ne tamkar su sukai kansu
Dayake shima ɗan hannu ne shiyasa tunda suka haɗu Rash take bashi kanta suke rayuwan ƙasƙanci, shaƙuwar da suka yi da soyayyan da suke ma juna ko yaushe suna tare tamkar Chwingum
A lokacin da Maan zai tafi karatun sa a Abuja inda anan ne yazaɓan ma kansa don ci gaba da karatun sa, sai Rash itama tace zata bi sa, hakan ya saka sa farin ciki sosai don haka yace tahaɗo kayan ta su tafi
Batare da sanin Mahaifiyar ta ba Rash tahaɗa kayan ta tabi Maan Abuja, ya kama musu hayan gida Plet anan suke zaune, sun ci gaba da zama tamkar mata da miji
Kasancewar Rash tayi karatun ta zuwa matakin primary sai Maan yanema mata school taci gaba, sai dai tana yi tana tsallake sabida tafi son rayuwan jami’a ne, ita babu abinda take ƙauna in banda taganta cikin jami’a tana rayuwan wayewa irin ta ƴan mata masu ji da kansu
Wannan yasa koda tagama Scondary school sai tashiga school ɗin su Maan inda a lokacin yana Degree ɗin sa ne