Uncategorized

RAUDHA Page 11 to 20

“Sannun ku da zuwa, maraba da ƙanwata”.

Suhaib ne kaɗai ya’amsa gaisuwar matar tasa yayinda RAUDHA kuma in banda kallon ta babu abinda take yi, har yanzu tana cike da tsoro sosai duk da kuwa sun bar garin

Zama Suhaib yayi yazaunar da ita kusa dashi

Ita kuma Farida sai tanufi Fridge taɗauko musu drinks tahaɗo da Cups ta’ajiye musu a gaban su kana tazauna tana cewa “My Husband kayi sauri da yawa”.

Suhaib dake kallon ta yace “to me zan zauna yi tunda na ɗauko ta? An gama gyara mata ɗakin saman?”

“Eh an gama, Allah yakyauta gaba to, mun gode Allah da babu abinda yafaru”.

Sai kuma tamayar da idanun ta kan RAUDHA tace “Baby babu magana?”

Sai lokacin RAUDHA tabuɗi baki tace “Sannu to”.

Gaba ɗaya sai da suka dara ganin yanda tayi maganar tana turo baki

Suhaib yace “tashi Baby in Kai ki ɗakin ki sai ki huta ko kafin akawo miki kayan ki?”.

Babu musu tamiƙe yariƙe mata hannu suka haura sama

Farida tabi su da kallon aranta tana mamakin irin ƙaunar da Mijin nata yake nuna ma ƙanwar sa

Ko kaɗan bata kishi da RAUDHA, hasali ma itama tana ƙaunar ta sosai tunda ta silan ta ne tasamu Suhaib ɗin, da fari ita take mahaukacin ƙaunar sa tun lokacin da yasoma aiki a Companin Daddyn sa, itama a lokacin tasamu aiki a Companin, sai tasoma shige masa suna mutunci batare dashi yasan son sa take yi ba

Duk wanda yake mu’amala da Suhaib dole ne yasan ƙaunar da yake ma ƙanwar sa, koda kuwa baka taɓa ganin ta bane labarin ta sai ya ishe ka, be da wani magana sai ta RAUDHA, hakan ne yasaka itama Farida tasoma nuna ƙaunar ta gare ta, duk da batasan RAUDHA ba amma sai tasoma tayasa ƙaunar ta, wannan dalilin ne Suhaib yasake sakin jiki da ita, domin sosai yake jin daɗin yanda take nuna ƙaunar ta ga ƙanwar sa, komi tasamu tace yakai ma RAUDHA, komi maganar ta RAUDHA, hakan yasaka soyayyar Farida tashiga ransa ainun tunda tana son ƙanwar sa, ita kanta Faridan tasan sabida RAUDHA yake son ta

Har Allah yasa daga ƙarshe suka yi aure, wajen shekara ɗaya da rabi kenan yanzu

RAUDHA sau biyu tataɓa zuwa gidan, sai dai har yanzu ta kasa sake jikin ta da Faridan duk da kuwa tana nuna mata kulawa da soyayya, sai dai ita akwai ta da rashin sabo idan har bada Daddy ko Suhaib ba bata son wani yashiga jikin ta, that’s why bata cika zuwa ba tunda shi Suhaib ɗin yana zuwa can.

      A halin yanzu Farida ta ajiye aikin ta, tun sanda tasamu ciki Suhaib yace mata sai dai ta’ajiye aikin ta rainan masa Yaron sa, dama can shi baya son Matar sa tariƙa aiki tunda suna da kuɗin da komi zai iya wadata ta dashi

Itama kuma bata yi musu ba ta’ajiye kamar yanda yake so ɗin, but duk wata yana bata albashi hakan yaƙara faranta mata sosai, kuma taji daɗin abun da yayi mata shiyasa bata damu yanzu tayi aiki ko kar tayi ba, tunda mijin ta na mata duk abinda take so..

Dafa kafaɗan ta yayi hakan yasa tadawo duniyar tunanin da talula tabi sa da ido

Murmushi yasakar mata yace “tunanin me kike yi haka har na dawo baki ji ni ba?”

Numfashi taja tace “babu komi Husband”.

“Ok to ki kula min da ƙanwata don Allah, idan tatashi kiyi mata duk abinda take so ki kula da ita plz sweetheart?”

Murmushi tayi tace kar ka damu insha Allahu bazan baka kunya ba Mijina”.

Kyakykyawar murmushin sa yayi mata yana shafa gefen kumatun ta yace “Thanks Sweetheart, yanzu ta kwanta ne kayan ta na kan hanya idan sun iso sai ki saka a shigar mata dashi ɗakin ta, Ni zan tafi office insha Allahu Nima bazan daɗe ba zan dawo”.

“To amma bakayi breakfast ba katafi yanzu kuma haka zaka tafi kenan baka yi ba?” Tayi maganar idanun ta cikin nasa

Suhaib yace “nayi late yanzu Sweetheart idan na je office zan yi kinji?”

Gyaɗa masa kai tayi

Shi kuma yayi mata kiss a lips ɗin ta sannan yasake shafa kumatun ta yace “sai na dawo Byeee ki kula da kanki”.

Murmushi tayi masa tare da addu’ar dawowa lafiya.

Sai da yabar parlour’n kafin tamiƙe daƙyar takoma ɗakin ta dake ƙasa.

         ????????????

Kwana biyu da zuwan RAUDHA gidan sannan Suhaib yasamu Numban Daddy ya shiga, lokacin suna zaune a parlour sai yatashi tsam yafice, sai da suka tattauna da Daddy ɗin kafin yadawo yamiƙa wa RAUDHA wayan

“My sweetheart ga Daddy zai yi magana dake?”

Wani irin tsalle tayi tararumi wayan tana ihu tasaka a kunne

“Daddyyyy”. Tafaɗa da ƙarfin da yasa Suhaib da Farida suka rufe kunnen su suna dariya

Dama koda yafita yin wayan batasan da Daddy yake yi ba

Daga can Daddy murmushi yayi cike da farin ciki yace “my Baby Kar ki fasa min dodon kunne mana”.

Kawai sai tasaki kukan shagwaɓa tana faɗin “Daddy nayi missing ɗin ka.. yaushe zaka zo kaɗauke Ni?”

“Sorry My Baby.. bazan dawo nan kusa ba coz akwai matsala da kayana suka samu dole zan zauna zuwa ɗan wani lokaci”.

Kuka tasoma mishi sosai tana bubbuga ƙafa tace “Daddy Allah Ni bazan koma can ba sai dai kazo kaɗauke Ni bazan iya zama Ni kaɗai ba”.

Daddy yace “my dear ai dama bance ki koma can ɗin ba, tunda kina gidan yayan ki zaki zauna har nadawo sai in zo in ɗauke ki ko?”

Ɗaga kai tayi takalli Suhaib dake kusa da ita, fuskarta sharkaf da hawaye tace “Daddy bana son nan..”

Riƙo hannun ta Suhaib yayi kafin yace “baki son wajena ko my sister? Kin fi son ki zauna acan kidnappers su kama ki su kashe ki..”

Tun kafin ma yaƙarisa maganar tasoma girgiza mishi kai

Daddy yace “my dear ki zauna a wajen yayanki zaki fi samun kulawa, kinga waɗannan mutanen da suka shiga gida na anyi bincike an gane ke suka zo ɗauka sabida suyi garkuwa dake, idan kika koma yanzu akwai matsala”.

Cikin zubar hawaye tace “to Daddy zan zauna bana so su kama Ni”.

“Yauwa my dear, kinga sai ki soma karatun ki anan tunda Yayan ki yace min an soma siyar da Admission uhmm?”

Shiru kawai tayi bata ce komi ba

Suhaib da har yanzu yana riƙe da hannun ta yasoma murza mata yatsu yana faɗin

“Daddy zata zauna anan ɗin insha Allahu zanna kula da ita babu abinda zai faru da ita”.

“Yauwa Suhaib ka kula min da ita sosai duk abinda take so kayi mata, idan nadawo zan zo har nan in ganki, and mutanen da suke neman ki acan ma baza su ƙara ganin ki ba bare su kama ki ko my dear?”.

“Eh Daddy”. Tafaɗa tana turo baki

Farida ita dai nata ido ne, kallon su kawai take yi cike da burgewa, tabbas duk wanda yazauna dasu zai san suna matuƙar ƙaunar ta, tana jinjina irin girman soyayyar da suke nuna mata, tana ta kallon su har sanda suka gama wayan ita kuma RAUDHA tamiƙe dasauri tanufi upstairs inda ɗakin ta yake

Tana shiga tafaɗa kan gado tana rufe idanunta, ko kaɗan bata jin daɗin zaman gidan, ta saba da can ta saba da rayuwanta ita kaɗai, a kwana biyun nan sosai take jin kewar can, ga matsanancin kewar Ramcy da take ji, ko babu komi baza ta so tarabu da ƙawarta ba shiyasa duk bata jindaɗi a zamanta na nan

Tashi zaune tayi taɗau wayan ta dake ajiye a bed side drower, tun sanda tazo takashe ta’ajiye bata sake ɗauka ba sai yanzu, kunnawa tayi tay dialling Numban Ramcy, sai da taɗauka sannan takoma takwanta

“My Besty Ina kika shiga nayi neman ki har na gaji?” Cewar Ramcy kamar zata yi kuka

Lumshe idanu RAUDHA tayi kafin tabuɗe tace “I miss You my Besty.. Ina Abuja?”

“Shine baki kira ni kin sanar min ba? Sannan kika kashe wayan ki, naje gidan ku but ba’a buɗe min ƙofa ba, kullum sai naje ko yau ma sai da naje amma banga kowa ba, meke faruwa ne?”

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11Next page

Related Articles

Leave a Reply

Back to top button