Uncategorized

RAUDHA Page 11 to 20

Ihu kawai RAUDHA take yi tana murna, ɗarewa jikin sa tayi tai ta zuba msa peck a fuska kamar zata cinye sa

Shi kuwa sai dariya yake yi yana jindaɗin yanda take murna da annashuwa

Waya yakira, babu jimawa ɗaya daga cikin bodyguard ɗin sa yashigo yanuna masa computern yace masa yakai ɗakin games ɗin RAUDHA, dayike yasan komi na gidan tunda shine Amintaccen sa, haka yaɗauka yafice su kuma suka dawo Parlour

A ranan tare suka wuni ko fita be sake yi ba

Wajen 02:00pm. Ramcy tazo gidan taya Daddy murnan dawowa, har Part ɗin shi RAUDHA tajanyo ta tunda dama sun saba dashi, kuma shima ya ɗauke ta tamkar ƴar sa ne tunda RAUDHA tana son ta, duk abinda zai iya ma ƴarsa to itama zai mata

Har ƙasa tazuƙuna tagaishe shi, ya’amsa mata cikin fara’a yana ta tambayan ta mutanen gida, daga ƙarshe yace mata tatashi tazauna itama kan kujera, babu musu kuwa tatashi tazauna ɗin kamar yanda yabuƙata, sai suka soma hira gaba ɗaya su ukun cikin nishaɗi

Sai kusan magriba Ramcy tace zata tafi, Trolly ɗaya na tsaraba Daddy yabata, dama yayi ne don ita, itama RAUDHA sai da taƙara mata da wasu abubuwan, Ramcy tayi murna sosai kuma tayi ma Daddy godiya har sai da yace ya isa

Duk da yasaba bata kyauta amma na yau yafi na ko yaushe tunda wannan tafiyan wajen watanni uku yashafe kafin yadawo, kuma be saba yin hakan ba iyakan wata ɗaya ko zuwa kusan biyu yake yi

Drever yamayar da Ramcy har gida tare da tsaraban ta

Su ma sauran ma’aikatan gidan duk sun samu nasu tsaraban, duk wanda yake gidan kuwa ya shaida tunda an ba kowa, sun yi murna sosai tunda tsaraban ba kaɗan bane.

      Da dare suna zaune aka kira Daddy a waya, abokin kasuwancin sa ne yake shaida masa akwai matsala yayi gaggawan zuwa yanzu

Kayansu da sukayi oda a UK sun samu matsala, kuma ana buƙatar su nan da 24hours

Dole hankalin Daddy yatashi, anan yake faɗa ma RAUDHA zai koma China akwai matsala

Ai nan RAUDHA tasa mishi fitina, daƙyar ya rarrashe ta tahaƙura

Wanka yayi yasauya kayan sa zuwa farar tissue yai shigan sa na hausawa, dama Daddy be cika saka kayan turawa ba anan ɗin in ba can yaje ba, amma idan yana nan shigan hausawa yake yi na manyan kaya

Motoci biyar na bodyguard suka raka sa zuwa airport, har da RAUDHA sai da tabi shi sai kukan taɓara take mishi yana rarrashin ta

Sai da Flight ɗin su yaɗaga kafin suka dawo gida.

       Wajen ƙarfe 11:37pm. RAUDHA tana cikin tsaka da barci tatashi a firgice sakamakon harbin Bindiga da taji

Sosai ake harbi kamar za’a tarwatsa gidan

Nan da nan tafirgice tasaki kuka cike da tsananin tsoro, wani irin kifo wa tayi takai tabuga kanta da tyles, but bata damu ba tanufi ƙofar ɗakin tasaka keey jikin ta na wani irin kyarma kamar an saka ta a shock, zame wa ƙasa tayi tana ci gaba da sharɓan kuka, wani harbin da tasake ji kurkusa sai da tasaki fitsari tarufe bakin ta dasauri tana ƙwalalo idanu, tsaban tsoro ƙirjin ta kamar zai faso yafito, daƙyar tararrafa tanufi bakin gadon taɗau wayan ta tasoma kiran Numban Daddyn ta, sai dai baya shiga hakan yasa tasake ɓarke wa da kuka kamar ana tsuma ta, izuwa lokacin majina da hawaye ne suka haɗe sukai dame-dame a fuskar nata, yau dai ta sadakar mutuwa zatayi

Hannun ta na rawa tanemo Numban DPO ta danna masa kira, yana ɗauka tasoma faɗa masa abinda ke faruwa tana yi tana kuka

Ai kuwa nan da nan DPO da yaran sa suka nufo gidan

A can kuwa tsakar gidan sai karan batta ake yi tsakanin ɓarayin da suka shigo su wajen ashirin da bodyguard ɗin gidan, in banda musayar wuta babu abinda suke yi duk an ji ma wasu ciwo

Gaba ɗaya gidan ya hargitse kamar filin dambe, masu aiki duk sun nemi maɓuya, haka ma maƙota duk da basu san takamaiman inda ake harbin ba.

          RAUDHA tana gama waya da DPO Yayan ta takira tana kuka tana faɗin “Yaya don Allah kazo kaɗauke Ni zasu kashe Ni, wayyo Allah yaya na shiga uku shikenan zasu kashe Ni mutuwa zan yi…”

Sai tasaki kuka tana sharɓan majina

Hankalin Suhaib a matuƙar tashin hankali yake tambayan ta su wanene? Amma ina ta kasa ma magana sabida tsaban kuka

Sai da yayi ta faman rarrashin ta kafin daƙyar ta’iya mishi bayani

“Don Allah kiyi shiru kinji? Kiyi shiru my dear please, I promise you babu abunda zai same ki baza su kashe ki ba kinji… Sorry.. sorry My dear zuwa gobe insha Allahu zan zo..”

“A’a yaya kazo yau katafi dani don Allah zasu kashe ni”.

Suhaib kamar zai yi kuka yace “Dear baza su kashe ki ba yanzu bari in Kira Asp. Aryan yanzu zai zo kin ji ki kwantar da hankalin ki, ina zuwa zan sake kiran ki”.

Ɗif yakashe wayan

Sake maƙurewa tayi ajikin bango tana ci gaba da kukan ta cike da tsananin tsoro.

A waje kuwa har ƴan sanda ???? sun zo kuma anyi nasaran kama wasu, wasu kuma sun gudu, a cikin bodyguard ɗin wasu duk sun samu harbi sannan an kashe mutane uku har lahira.

RAUDHA bata buɗe ƙofar ɗakin ta ba sai da taji muryan DPO, nan tasake haukace musu akan sai sun kira mata Daddyn ta, shi da kanshi DPO ɗin yakira sa amma wayan sa akashe, shaf sun manta a yanzu ɗin yana jirgi wayan sa baza ta shiga ba

A taƙaice dai aranan daƙyar suka rarrashe ta suka haɗa ta da ƴan sandan da zasu yi gadin ɗakin ta, kuma bata yarda ta kwana ita kaɗai ba sai da aka kira mata su Saude da sauran masu aiki, a waje kuma duk aka ƙara matakan tsaro

RAUDHA ƙiri-ƙiri ta kasa barci in banda firgita babu abinda take yi duk da kuwa ba ita kaɗai bace a ɗakin, kuma ta hana kowa barci dole su zauna gadin ta, aranan dai haka suka kwana gaba ɗayan su ido buɗe har Suhaib da ba ma agidan yake ba, koda yakira ta saka mishi rigima yayi kar yafara yakashe wayan, a haka takwana da waya a kunne tana jin motsin sa, shi kuma sai faman kwantar mata da hankali yake yi tunda tuni barci ya ƙaurace ma idanun sa, ko kaɗan bazai iya barci ƙanwar sa na can cikin firgici ba.

Ta tsorata sosai ita duk a ganin ta ɗauke ta suka zo yi tunda tasha jin ana ɗauke mutane akashe su, sosai take matuƙar tsoron ƴan kidnappers, bata so ko kaɗan taje hannun su.

[11/26/2020, 11:51 AM] نفيسة أم طاهرة: ????????????????????????????????????????

????????????????????

????????????????????

  *RAUDHA*

????????????????????

????????????????????

????????????????????????????????????????

*MALLAKAR*✍️

              _Nafisat Isma’il Lawal Goma_

*بسم الله الرحمن الرحيم*

 

*FEENAH WRITER’S ASSO????*

“`®Ɗaya tamkar da Dubu????✓“`

*JIKAR LAWALI CE*✍️

*Wattpad: UmmuDahirah*????

         *F.W.A????/*

.

  *NOT EDITED* ___________________________????

        *SEASON FIFTEEN*

_______????Ƙarfe 07:30am. Yayi ma Suhaib a garin Zaria, lokacin da yashiga gidan RAUDHA maƙalƙale shi tayi tana ta kuka, daƙyar yararrashe ta tayi shiru sannan yace “taje tahaɗo kayan ta su tafi” babu musu kuwa tasaka Masu aiki suka haɗa mata kayan ta

Duk ka gaba ɗaya duk wani abun buƙatun ta sai da Suhaib yasaka aka kwashe mata aka zuba a mota, mota biyu aka cika drevers sukai gaba dashi, su kuma sai suka biyo Flight suka nufi Abuja

Drevern sa yazo yaɗauke su a airport suka nufi gidan Suhaib ɗin dake Asokoro, babban gida ne me hawa biyu, sosai gidan yahaɗu matuƙa gashi an kashe kuɗi kamar baza’a mutu ba

Drever na yin parcking suka fito, Suhaib yariƙe mata hannu suka nufi cikin gidan, suna shiga parlour’n gidan

Matar sa Farida tafito daga ɗaki tana kallon su da murmushi a face ɗin ta, tana da tsohon ciki haihuwa ko yau ko gobe

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11Next page

Related Articles

Leave a Reply

Back to top button