RAUDHA Page 11 to 20

Babu kowa cikin tanƙamemen parlour’n sai ita kaɗai, girman parlour’n sai da yaɗauke set uku na kujeru daban-daban
Bata jima da zama ba tajiyo horn ɗin motoci, da gudu tatashi tafita, tun daga nesa tahango motoci kusan goma suna tahowa amma haka tanufi wajen da gudun ta tana farin ciki
Kafin ta’iso har motocin sunyi parcking mutane sun soma fitowa
Motoci biyar na bodyguard ɗin Daddy ne, sauran kuma na mutanen sa ne tare da abokan sa da sukai mishi rakiya
Farin dattijon mutum ne yafito a motan tsakiyan wanda shi kaɗai ne fari tar kuma babba sosai, mutumin yana da tsananin kwarjini da cikan haiba, kallo ɗaya idan kayi masa zakaga tsantsan kamar da suke yi da RAUDHA, sai dai kuma bashi da maraba da Suhaib don shi yafi ɗauko sa sak kamar kaki yayi ya’ajiye
Da wani irin gudu tanufo mahaifin nata, duk yawan mutanen wajen tunda taƙilla idanu kansa bata ƙara waiwayan su ba
Tana isowa yamiƙa hannu yacafe ta a jikin sa, juyata kawai yake yi yana dariya cike da tsantsan ƙaunar ta, itama ɗin dariya take yi tana kiran
“Daddy.. Daddy..”
Duk wanda yagansu yasan akwai soyayya me ƙarfi a tsakanin su
Duk mutanen wajen kallon su kawai suke yi suna murmushi cike da sha’awan su
Sosai Daddy yaga Babyn nasa ta sauya masa, tayi rama sosai duk da yasan ita ɗin ba ma’abociyar cin abinci bane
Inda RAUDHA me tarbiyya ce be kamata tafito da wannan kayan agaban mutane ba, shima kuma Daddy ko kaɗan be damu da ganin ta ahaka ba bare har yaga tayi laifi
Tana jikin sa be sauke ta ba yakalli mutanen da murmushi a face ɗin sa yace
“Mu shiga ciki”.
Babu musu suka nufi cikin gidan gaba ɗayan su
A Parlour suka yada zango gaba ɗayan su
Daddy ajikin sa yaɗaura RAUDHA ko kunyan mutane baya ji, dayake yana rayuwan sa irin na turawa ne shiyasa be ji kunya ba, kuma ko kaɗan baya jin shakkar nuna tsantsan soyayyar da yake mata ako ina, bare kuma ya ɗauke ta ne tamkar yarinya ƴar shekara biyar, sosai yake tsananin tausayin ta kasancewar ta tashi cikin maraicin uwa, shiyasa duk wani abun da yakamata uwa tayi ma ƴarta shi ke yi ma RAUDHA
RAUDHA lafewa tayi ajikin sa tana kallon mutanen dake zaune ana gaggaisa wa, wasu daga cikin abokan shi sai tonan ta suke yi tana murmusawa amma batace komi ba
Ahaka dai sukai ta yin ma Daddy barka tare da nuna murnan su na samun nasara da yayi a kasuwancin sa
Masu aiki duk sun jibge musu Drinks a gaban su
Sun ɗan ɗauki kusan mintuna 20 kafin suyi masa sallama su tafi
Anan RAUDHA tasake matse shi tana faɗin “I miss You Daddyyyy?”
Har da ƙwallan ta
Shima sake Hugging ɗin ta yayi yana murmushi me bayyana haƙora yace “I miss You more than you Babyna”.
Ɗago kanta tayi tana kallon sa da dariya a fuskarta, sosai za’a gane farin ciki tsantsa da take ciki
“Daddy na..” Tafaɗa tana sake yin dariya bayan ta sake shigewa jikin sa
Daddy dariya yayi yace “Baby murna yayi miki yawa kin kasa magana ko”.
Still ɗago kanta tayi tana kallon sa, baki awashe tagyaɗa masa kai
A lokacin ne sauran ma’aikatan gidan suka soma shigowa suna kawo mishi gaisuwa har dasu Saude aciki
Amsa musu yake yi cikin fara’a wanda zaka gane ɗab’ian sa ne hakan
Sai da kowa yafita kafin yasake kallon RAUDHA, wannan karon ma da murmushi a face ɗin sa yace “to ya kike Babyna na same ki lafiya?”
“Eh Daddyna”.
Shafa kanta yayi yace “duk kin rame Sweetheart, kin yi ciwo ne baki faɗa min ba?”
Girgiza kanta tayi tana sake cusa hannun ta cikin nashi tace “Daddy ban yi ciwo ba kewar ka ne ya ramar dani”.
Dariya yayi sabida yanda tayi maganar
Itama sai tatayashi tana yi tana cino baki alamun zatayi fushi
Cikin dariyan yace “sorry Baby Kar ki ɓata rai, tashi muje ɗakina sai inyi wanka mu sake gaisawa ko?”.
Ɗaga ta yayi tana jikin sa wannan karon ma be sauke ta ba yanufi lifter yabuɗe yashiga.
[11/23/2020, 10:01 AM] نفيسة أم طاهرة: ????????????????????????????????????????
????????????????????
????????????????????
*RAUDHA*
????????????????????
????????????????????
????????????????????????????????????????
*MALLAKAR*✍️
_Nafisat Isma’il Lawal Goma_
*بسم الله الرحمن الرحيم*
⚖
*FEENAH WRITER’S ASSO????*
“`®Ɗaya tamkar da Dubu????✓“`
*JIKAR LAWALI CE*✍️
*Wattpad: UmmuDahirah*????
*F.W.A????/*
.
*NOT EDITED* ___________________________????
*SEASON FOURTEEN*
_______????Bayan Daddy yayi wanka parlour’n sa suka zauna, anan an rigada an jera masa abinci a dainning, don haka tare suka soma ci da RAUDHA, suna yi suna hira yana tambayan ta matsalolin ta
Sai da aka kira sallan Asar kafin yamiƙe yafita bayan yayi alwala
Itama RAUDHA dasauri tashiga ɗakin ta na Part ɗin Daddy ɗin taɗauro alwala
Ko wani upstairs akwai ɗakin ta aciki, Dad ɗin ta yana hawa na biyu ne
Bayan an idar da Sallah koda yadawo mutanen anguwa yagani sun yi masa dafifi a ƙofar gida, a zummar sun zo tayasa murna but a baɗini maula suka zo yi, sun san Alhaji me kyauta ne bazai taɓa barin su haka ba
Ai kuwa bayan ya gaisa dasu faram-faram sai yashiga cikin gidan yakira bodyguard ɗin sa ɗaya yace ” yabiyo sa ya’amso musu saƙo”.
Kuɗi yabashi yace yaraba musu sai wasu daga cikin kayayyaki na masarufi da yasa a ɗibo daga store duk a rabar musu kar yalalace
Zama yayi a parlour’n sa RAUDHA na jikin sa sai zuba masa surutu take yi
Sosai RAUDHA take da miskilanci amma idan tazauna gaban mahaifin ta zakai tunanin ta haɗiye rediyo ne saboda yanda take zuba kamar ana ƙara mata sabbin batir
Koda aka kira wayan Daddy dake can cikin bedroom ɗin sa da gudu taje taɗauko masa, zama tayi gefen sa tana faɗin
“Daddy Yaya ne yakira ka”.
Amsan wayan yayi yana murmushi yakara a kunne da sallama a bakin sa
Daga can Suhaib amsawa yayi cikin jindaɗi sannan yagaishe shi
Ga duk kan alamu yanda suke wayan zaka san akwai shaƙuwa da junan su, anan Suhaib yake faɗa masa bazai samu zuwa ba sai jibi sabida aiki da sukai masa yawa
Daddy be wani damu ba yace masa yakula da kansa sosai Allah yakawo sa lafiya
RAUDHA ce ta’amsa wayan tana ta zuba masa shagwaɓa akan ita dai sai yazo, daƙyar ya rarrashe ta tahaƙura
Haka suka kasance a ranan cikin farin ciki, duk inda Daddy yake tana maƙale dashi, ƙarshe ma a part ɗin sa takwana.
Washe gari da wuri tatashi tayi wanka tashirya cikin biri da wando me hannun vest, sai dai bata saka wani riga aciki ba kamar yanda ake saka wa, blue colour ne na jeans, sai ta tufke gashin ta a tsakiyar kai da jelan
Tana fitowa ta tarar da Daddy zaune yana amsa call, shi lokacin ya daɗe da tashi ma har ya fita waje ya gaisa da baƙi, shigowan sa kenan yasoma waya da wani abokin kasuwancin sa
Zama tayi gefen sa har yagama sannan yakalle ta cikin so da ƙauna yace “My Baby kin tashi?”.
Gyaɗa masa kai tayi tana turo baki gaba
Murmushi yayi yashafa mata kai kana yace “oya tashi muje muyi breakfast tukuna sai ki faɗa min meke damun ki”.
Dasauri tatashi tariƙo hannun sa suka nufi kan dainning inda aka jera musu breakfast kala-kala
Akan cinyan sa ya’ajiye ta yahaɗa musu duk abinda suke buƙata, shi yadunga ciyar da ita har suka kammala sannan suka dawo parlour
Jan hannun ta yayi suka koma bedroom ɗin sa inda yanuna mata wasu manyan Trollys guda uku yace mata duk tsaraban ta ne, sannan yaƙara mata da sabuwar waya iPhone 11pro har da Lapton tare da keey ɗin mota, sai yanuna mata wani ƙaton computer me kamar t.v yace mata sai ta’ajiye a ɗakin games ɗin ta