RAUDHA Page 11 to 20

Juyawa yayi yanufi upstairs ɗin don kiran ta
Ita kuma Farida kan dainning tanufa taja kujera tazauna, sannan tabuɗe abincin tana zuba wa a plate iya wanda zata ci
Kamar minti 5 da hawan sa sai ga su sun sauko, tana manne da jikin sa sai mishi shagwaɓa take yi shi kuma yana mata dariya
Idanun Farida na kansu har suka ƙariso, zama suka yi Suhaib ɗin yasoma saving ɗin su shi da ita
Tun da suka soma cin abincin babu wanda yayi magana
RAUDHA tasoma tashi bayan ta ture Plate ɗin
“Aaah Baby har kin gama?” Suhaib yafaɗa idanun sa akanta yana taunan abinci
Gyaɗa masa kai tayi tana langaɓe kai
“Ok Nima na ƙoshi jira Ni muje”.
Tashi yayi yariƙe mata hannu suka nufi cikin parlour’n
Ido kawai Farida tasanya musu ta ma rasa tunanin da zata yi, janye idanun ta tayi taci gaba da cin abincin ta har sanda tagama sannan takoma cikin parlour’n
Hira suke yi don haka itama tadunga saka musu baki.
????????????????????????????
A cikin sati biyu da zuwan RAUDHA gidan har Suhaib ya gama mata komi na school ɗin ta, yau ce ranan da zata fara zuwa don haka tatashi da wuri cike da ɗoki, dama ita akwai ta da son karatu sosai
Ta gama shirin ta cikin farar riga me taushi sosai, rigan dogon hannu yake dashi kuma irin me wuyan nan ne dogo, sai tayi stocking ɗin rigan cikin blue pencil Jeans ɗin ta, tasaka Belt baƙi me ƙyalƙyali, Combat tasaka a ƙafafun ta baƙi sannan ta tsaga gashin kanta tasanya Ribom biyu kalan blue, yau har da saka Wrest watch a hannun ta fari, sosai tayi kyau kamar wata baby doll sai tashin ƙamshi take yi, haka taɗau HangBag ɗin ta tafito tana zuba murmushi
Tunda Suhaib yahango ta yake faman zuba murmushi, abinci yake ci but sai ya’ajiye spoon ɗin yana faɗin
“Wow my dear Baby kinyi kyau”.
“Thanks Yayana”. Tafaɗa tana murmusawa har haƙoran ta suna bayyana
Farida dake zaune gefen Suhaib ɗin akan dainning ita dai kallon RAUDHAN take yi cike da mamaki, sai dai bata iya cewa komi ba tana jiran taji me Suhaib ɗin zai ce game da shigan ta
Zuwa tayi taja kujera tana kallon Farida
Hakan yasa Faridan sakin murmushi tana cewa “baby kinyi kyau”.
Cike da jindaɗi RAUDHA tace mata “tnz Aunty”.
Suhaib yace “Baby gan ɗoki baza ki yafa ko mayafi bane a kan ki?”
Ɓata fuska tayi tana kallon sa tace “Ni bazan saka ba”.
Miƙe wa yayi be sake bi ta maganan ba, sai peck da yayi mata a goshin ta sannan yayi ma Farida yay musu sallama yafice
Farida tana so tayi mata magana amma kuma tana jin tsoro, daga ƙarshe dai tayanke shawaran yin mata maganan, ɗago kai tayi tana kallon RAUDHAN dake sipping coffee tace
“Ƙanwata meyasaka zaki yi wannan shigan bayan fita zaki yi?”
Cakk RAUDHA tatsai da shan Coffee ɗin tana kallon Farida, sannan takuma maida idanun ta jikin ta tana kallon abinda Faridan tagani har ta’iya mata magana, bata ga komi ba hakan yasa taɗago kai tana kallon ta, sai dai bata iya cewa komi ba illa zuba mata shanyayyun idanunta da tayi
Murmushin yaƙe Farida tayi tace “naga baki rufe gashin ki bane kamar yanda Yayanki yafaɗa”.
Taɓe baki RAUDHA tayi tana miƙe wa
“Ban buƙata ne”. Tafaɗa tana yin gaba
Kallon ta kawai take yi har tafice, sai tasaki ajiyan zuciya tana faɗin “Allah ya kyauta to”.
Fitan RAUDHA parcking lot tanufa tashiga motan ta da Daddy yasake mata, tunda har dashi duk aka ɗauko mata, jan motan tayi tay bakin Gate tana buga horn
Jiki na rawa Gate man yabuɗe mata tafice da gudun gangancin ta
Bata zarce ko ina ba sai makarantan su, bayan tayi parcking sai da taɗau lokaci kafin tafito cikin motan sannan tarufe, tasoma tafiya cikin tafiyan ta me nutsuwa tamkar baza ta taka ƙasa ba
Dayike school ɗin haɗuwan mutane daban-daban ne kuma ƙabila iri-iri don haka shigan RAUDHA be zama baƙo agare su ba, sai dai hakan be hana idanun mutane sauka kanta ba sabida haɗuwan ta, duk inda tabi ana kallon ta
Ta rigada tasan department ɗin su tunda ranan ƙarshe da Suhaib zai zo ya kammala mata duk registration ɗin ta da ita suka taho, kuma duk ya nuna mata wajaje da dama a school ɗin
English double major zata karanta don haka can department ɗin tanufa.
.
_to ga fa RAUDHA a school bari mu ga me zai faru?_
[12/26/2020, 3:28 PM] نفيسة أم طاهرة: ????????????????????????????????????????
????????????????????
????????????????????
*RAUDHA*
????????????????????
????????????????????
????????????????????????????????????????
*MALLAKAR*✍️
_Nafisat Isma’il Lawal Goma_
*بسم الله الرحمن الرحيم*
⚖
*FEENAH WRITER’S ASSO????*
“`®Ɗaya tamkar da Dubu????✓“`
*JIKAR LAWALI CE*✍️
*Wattpad: UmmuDahirah*????
*F.W.A????/*
.
*NOT EDITED* ___________________________????
*SEASON SEVENTEEN*
_______????Holl ɗin da zasu yi karatu ta dosa tashige
Babu wasu ɗalibai sosai aciki kasancewar safiya ne kuma sabbin zuwa ne, gashi time be yi ba
Can ƙarshen kujeru tanufa tazauna batare da ta kalli kowa cikin holl ɗin ba, tana nan zaune tana latsa wayan ta ta ɗaura ƙafa ɗaya kan ɗaya, mutane sukai tashigo wa da ɗai-ɗai har suka yi rabin ajin wanda ga duk kan alamu yawan nasu bazai fi hakan ba
Can kuma Malamin da zai ɗauke su lecture yashigo, suka gaishe shi ya’amsa da fara’a
Da fari Barka da zuwa yasoma yin musu a matsayin su na sabbin ɗalibai, sannan yaɗaura da ɗan guntun nasihan sa kafin yasoma gabatar musu da sunansa da kuma lecturen da zai musu
RAUDHA na zaune har a lokacin kamar yanda take, sai dai yanzu ta ɗauko Tap ɗin ta wanda Suhaib yasiya mata tana yin jotting a ciki, bata kallon malamin amma duk abinda yake faɗa tana ji kuma tana rubuta abinda zata ƙaru aciki.
Bayan ya gama sai yatambaye su idan da me tambaya yayi masa, kun san sabbin ɗalibai akwai su da tsoro sai idan sun saba, don haka kowa yanoƙe yaƙi ɗaga hannu duk da kuwa wasun su suna da tambaya
RAUDHA da sai yanzu taɗago kanta takalli Malamin da mutanen ciki taɗaga hannun ta batare da ta furta komi ba
Malamin da idanun sa yasauka kanta yabata daman tambayan
Don haka kowa yajuyo yazuba mata idanu ana kallon ta, wasu ma sai lokacin suka ganta, wasu kuma basu yi zaton ƴar ajin bane duba da yanda taje can baya nesa dasu ta keɓe kanta
Tambaya tasoma jero masa yana bata amsa
Abun har sai da yaba ɗalibai mamaki, ganin yanda take ta zubo tambayoyi cikin daddaɗan muryan ta me sanyi
Shi kuwa Malamin sai amsa mata yake yi, don har shi ta burge shi, shi a rayuwa yana son ɗalibi me yawan tambaya akan karatu, hakan na saka wa ɗalibi yay saurin fahimta tunda bashi da tsoron tambayan Malami
Ita kuma RAUDHA dama halin ta ne tambaya a aji, ka mun kaga ta ɗaga hannu da sunan ba ma malami amsa to sai dai shi yatashe ta, amma duk tambayan da malami zai yi a aji koda ta sani baza ta tashi ta faɗa ba, but da zaran ya ba da daman tambayar sa to anan ne zatai ta jero mishi tambayoyi kaf abinda take so tasani, kuma baza ta taɓa ko jin kunya ko tayi tunanin shi malamin zai yi tunanin tana son ƙure sa ne ba, ko ya kai ashirin ne tambayoyin ta sai tayi maka, sai dai kai kace ya isa haka nan
Shiyasa sanda tayi secondary school babu malamin da be san ta ba har CE mata suke yi sarkin tambaya.
Questions biyar tatambaye sa kuma duk ya amsa mata
Shirun da tayi yatabbatar ma Malamin ta gama don haka sai yatambaye ta sunan ta
Taba shi amsa da *”RAUDHA ElMUSTAPHA MAKAMASHI”.*