NOVELSSARAN BOYE

SARAN BOYE COMPLETE


        *_SAUDIA_*

   Shirin Adawiya ya saka suka wuni cikin daɗin rai yau ita da Abdallah. Dan dakansa ya sakata tai musu girki kamar yanda tai masa alƙawarin yimasa irin girkin da Nu'aymah tafi iyawa kuma tafi so. Shiko ya biye mata harda binta kitchen sukai aikinma tare. 
 Bayan sun gama kuma ya jata ɗakinsa sukai wanka tare, dukda babu abinda yay mata irin na nuna soyayya ga ma'aurata ɗinnan hakan baisa ta damuba. acewarta ai yanzun aka fara wasan. Dan haka ta ƙara ƙaimi wajen saka masa sunan Nu'aymah akan duk abinda zasuyi.

  Zuwa dare bayan tayi barci a ɗakinta shima yana nasa sai ya shiga dogon nazari akan shawarar Adawiyan. A yanda ya ƙiyasta zaiyi amfani da yarinyar wajen dawo da martabarsa ga Nu'aymah kamar yanda ta faɗa masa. Duk da yayi saurin ɗago dabararta nayin hakan game da sakko Nu'aymah a lamarinsu, sai yaga ai shima wata damace a hannunsa da zai dama ya yadda ƙwallon mangwaro kuma ya huta da ƙuda.
Dan haka ya kammala shirinsa tsaf game da yanda zai bida Adawiya akan Nu'aymah har haƙarsa ta cimma ruwa ya mallaki abar sonsa su gina rayuwar da yagama tsara musu tun asalin fara mallakar hankalinsa.
Da wannan ƙwarin gwiwar yay barci ranar. Washe gari kuwa tunkan ya tashi Adawiya harta shirya masa breakfast wai acewarta irin abincin da Nu'aymah tafi ƙauna kenan. Yakoyi farin ciki, a ƙasan ransa kuma yana mai mata kallon ƙuruciya da wauta. Zama yay yaci sosai ya ƙoshi, ya kuma taimaka mata suka gyara gidan sannan suka fita tare ya kaita makaranta kafin shima ya wuce tasa.

    Ba ƙaramin farin ciki Maman Aaida tayi da labarin da Adawiya ta bataba. da kuma abinda ta gani da idonta na kawo Adawiya da Abdallah yayi school, rabonda hakan ta faru tun randa ta fara zuwa da kwanaki ukun da suka biyo baya. Daga haka yace ta cigaba da zuwa ai zata gane hanya. Sai gashi yau ya kawota da kansa cike da farin cikinsa.
  Haka taita walwala a majaranta har lokacin tashi yayi. Abin mamaki kuma sai gashi ya sake dawowa ya ɗauketa. Suna isa gida kuma ya miƙa mata kwalin waya sabuwa fil harda sim card a ciki. Wani uban tsalle ta buga ta ɗaresa tana masa tagwayen kiss a wuyansa da fuska. Daga haka ya biye mata ya kwashi gara sanan ya sake wanka ya fice gidan ya barta da murnar waya.

     Wani irin ji Adawiya tayi kanta na yawo a sama. Ta tsaya gaban mirror tana kallon kanta cike da nishaɗi da yabama tunaninta da shirinta. ‘Yo ashe nice na zauna shashanci akanka Yah Ab, ashe kawai wata ƴar gajeriyar hanyar da zan bi da kai na samu nasarori a kanka bama nasara gudaba, amma na zauna ɓata hawayena da lokacina wajen tunani da baƙin rai. To yanzu kam saika shirya, dan Adawiya tayi alƙawari da alwashin sai kayi nadamar cin kashin dakai mata akan wata shasha Nu'aymah. Kaida Nu'aymah kuwa sai dai gani a hoto, dan lokaci zaizo da ko gaisuwar waya sai kun tsani kanku wajen dinga yinta balle ta zahiri. Ni Adawiya Mustapha Hashim Jibiya, ni kaɗaice matar da zata mallakeka a duniya da komai naka. Kuma Nu'aymah bazata taɓa samun wanda ko ya kama ƙafar matsayin Slippers ɗin wankan kaba Yah Ab. Dan saina sakata kuka da baƙin ciki kwatankwacin wanda ta sakani a baya saboda zazzafar ƙaunarka da begenka inhar niɗin jinin Fauza ce (Addah).

Tofa Adawiya anya baki ɗebo da zafiba kuwa?????????????.


    Nu'aymah da batasanma Adawiya nayiba tana can durƙushe gaban Umm da Baba malam tana mai basu haƙuri akan ɓacin ran data assasa musu a safiyar jiya game da abinda ya faru. Dan jiya gaba ɗaya ƙin kulata Umm tayi. Baba malam kuma basu shigo gidaba sai gab da magriba. Yana zuwa yay alwala ya wuce massalaci ko Hajjo bai leƙaba. Bai kuma shigo gidanba sai goma saura kamar yanda ya saba. Zuwa lokacin kuma Nu'aymahr ta gama jigata da aman da taita kwarawa na ƙa'idar zuwan jininta hartasha magani tai barci. 

   Ƙinyin magana Baba malam yayi har sai da Umn ta gama yima Nu'aymah faɗa sosai akan shegen tsiwarta kamar zata daketa kafin ta koma nasiha kuma. 
    Bata bartaba har sai da taga tana sharar ƙwalla, dan Nu'aymah fa batason faɗa a rayuwarta, sai dai kuma babu yanda ta iya dan iyaye nagari suke saurin tsawatawa yaransu idan sun gansu akan dokin kuskure. Bayan Umm ta gama nata shima bana malam ya murje nasa idanun yay mata tas fiye da wanda Umm ɗin tai matama. Kafin shima daga baya ya koma nasihar da nuna mata illar rashin kunya ga ɗiya mace.
 Tasha kuka da neman gafararsu sosai, dan har saida Muhammad ya sulale sashin hajjo ya sanar mata tazo ta ƙwaci Nu'aymah a hannunsu sannan suka barta. Duk da dai itama Hajjo ba ƙyaleta taiba sai da ta mata nasihar itama.

  Haka Nu'aymah ta wuni ranar cikin halin ciwo da takaicin Yoohan da Guards ɗinsa da duk ta tattara laifin a kansu saboda faɗan da akai mata. Bata da riko sam idan akai mata abu. amma sai gashi yau Yoohan ɗin da tarkacensa sun kasa barin ranta harma washe gari da shima dai haka ta yini babu walwala saboda jinin nata.

  Da haka kwanaki suka cigaba da  ƙara shurawa, baba malam yana cigaba da ƙoƙari neman hanyar haɗuwar Doctor da Nu'aymah batare da kowa ya saniba. Sai dai kuma har yanzu dai ba'a dace ba kam. Har gasu Yusrah sunyi nisa a zana jarabawarsu, wadda a dalilinta baba malm ya dakata da nemawa Nu'aymah makaranta. A cewarsu idan sun kammala sai a nema mata ita da Amal, tunda ita Yusrah zatabi Abdallah ne taje itama tayi nata karatun kamar adawiya.
    Cikin wannan tsukun takardun da bawan ALLAH nan da har yanzu basusan ko wanene ba suka gama kammala. Daga na neman aiki harna karatun yaran daya buƙata. Haka suka tattarasu aka aika masa ta hanyar daya faɗa.
Kamar wasa kuwa sai ga saƙon ɗaukar aikin nata zuwa ɗaya bayan ɗaya. Hakama na masu shiga makaranta ba'a ƙulla sati uku ba ya turo da kammaluwar komai da makarantun da duk zasuje ɗin.
 Wannan al'amari yayi masifar yima baba malam da duk ahalinsa daɗi. har takai ya shirya family meeting na musamman ya roƙa duk yaran da iyayensu akan su ware dare guda wajen mikama UBANGIJI addu'aoinsu na alkairi akan wannan bawan ALLAH da basusan wanene ba ɗan kuma wane yankine. Kowa ya aminta da wannan tukuyci, sunkuma ɗauki alwashi da ɗamnarar gudanarwa insha ALLAH.
   Yanda Nu'aymah taga mahaifinta yana farin ciki da al'amarin ita bayanma ƙiyamullaili da tayi harda azumi ta tashi washe gari, dan a duniya babu abinda ke sakata nutsuwa da maɗaukakin farin ciki irin ganin iyayenta a farin ciki.

 Kamar yanda Baba malam ya roƙama wannan bawan ALLAH addu'a ga iyalansa haka ya roƙama masa a massallaci, ya kuma roƙa masa a gidan marayun da alkairin yazam duk a kansune. Dan bayan wancan aiken duk ƙarshen wata sai an kawo mota guda ta kayan abinci gidan daga wannan mutumi da basusan ko waneneba. Wani abin mamakima harda yankakkun kaji lafiyayyu ake hado musu yanzun ko ɗanyen kifi ko jan nama.

SAUDIA

    Tunda Adawiya ta samu waya shikenanfa harka ta buɗe mata. Kullum cikin kiran ƴan uwanta takeyi suna shargallensu. duk da Nu'aymah bata da waya a hannu yanzu haka Adawiya ke addabama Umm kira akan ta bata. Kokuma wayar Amal ko Yusrah, kai harta hajjo kira take a haɗasu.
    Duk hakan tanayinsane danta birge Yah Abdallah ya yarda da gaske tanason cika masa alƙawarinsa na maido Nu'aymah rayuwarsa. Shi kuma duk da yasan dalilin yin hakan bai taɓa nuna mata ya fahimta ɗinba. Haka ya cigaba da biye mata akan ƙuruciyarta da wauta. Sai dai yanajin farin cikin yanda yakejin muryar sahibarsa kullum sama da sau biyar a rana. Duk da har yanzu bai taɓa amsar wayar sunyi maganaba koda kuwa a gabansa ne Adawiya zatai fira da Nu'aymah.

     A gefe kuma abinda Abdallah bai taɓa fahimtaba shine Adawiya ta daina shan maganin da yake bata. Duk sanda zai batan bata musawa wajen amsa, sai dai fa cikin dabara da wayon da ALLAH yay mata zata zirar dashi cikin riga tayi kamar tasha. Sai ta faki idanunsa ta watsa cikin wani abun da tasan idonsa bazai kaiba. A haka suka cigaba da shurawa ƴar shaƙuwar dake tsakaninsu kafin aure tana dawowa a dalilin saka Nu'aymah da sukayi a tsakkiyar lamarinsu.

★★★★★

    A ranar da Adawiya ta fara kiransu a waya suka gaisa Nu'aymah tasha kuka a ɓoye, dan har Umm sai da ta gane tayi kuka. Dan haka ta jata a jikinta sosai cikin hikima taita lallashinta harta ware. Daga nan kullum Adawiya ta kirata bayan sun gama hirar da ƙyar take iya danne zuciyarta. Dan tunkan ai nisa ta fara fahimtar kamar da biyu Adawiya ke kiranta tana gasa mata magana a fakaice kan Abdallah.
 Duk da ƙuruciya da yarinta dake tattare da ita hakan bai hanata zama ta harhaɗa wasu abubuwan cikin rantaba gameda abinda ya shuɗe na rayuwarta da Abdallah harma lalacewar aurensu da har yanzu an gaza gano musabbabin sa a gidan. Kuma har yanzu wasu basubar kallonta da tabon guduwaba a ranar auren nata. Yayinda sukeji a ransu rashin dawowar Ameer gareta butulcine da alhakin Abdallah.

    A wayar da Adawiya takeyi da ita kowa yana kallonta a matsayin shakuwar da sukayice da ɗunbin soyayyar dake a tsakaninsu. Amma kuma a baɗini Nu'aymah ita kaɗai tasan mike faruwa tsakaninta da Adawiyar. Ta kuma shanye a ranta duk da yana damunta bata taɓa nunama kowa a fuskaba koda kuwa su Yusrah ne balle Umm.

★★★★

  Rayuwa ta cigaba da shurawa, inda alkairin wannan bawan ALLAH keta sake faɗaɗa ga gidan marayunnan. Ga azumi nata gabatowa gamai yawancin kwana kuma. Kowa nata shirye-shirye da abinda ALLAH ya hore masa dan farantama iyalansa da bayin ALLAHn da basu da shi.
         A gefe kuma babban gida irin na malamai su baba malam sunata shirye-shiryen tafsir da hidimar da suka shiryama marasa ƙarfi wanda suke jiran sakamakonsu a gurin UBANGIJI al'arshi.
 Duk shekara su duka huɗun suna gudanar da wa'azi a mabanbanta garuruwan da suke rayuwa. Abba Mustapha dake tare da baba malam anan kano shine keyi anan masallacin ƙofar gidansu. Yayinda shi kuma baba malam keyi a massallacin gidan sarki duk shekarar duniya.
  To a wannan shekararma sun kammala shirinsu tsaf daga gidajensu har gidan marayunsu. Ta wani ɓangaren kuma taimakone keta ɓullowa ta hanyoyi daban-daban zuwa gidan marayunsu. Amma duk da haka baba malam bai gazaba wajen tsayuwar daka akan tantance daga ina komai ya fito da ingancinsa ga lafiyar yaran da mutuncinsu.

         Alhmdllh an shiga watan azumin ramadan cikin rahamar UBANGIJI da yardarsa. Kowanne musulmi na ƙwarai yana cike da murnar shigar wannan wata mai tarin falala dake zuwa mana a cikin watanni goma sha biyu na shekara sau ɗaya kacal ya wuce.
Randa aka kai azumi na goma Baba malam ya gama shirya maganar Umrah da Hajjo kanje a duk shekarar duniya idan wata ya raba. A ƙa'ida kuma takanje da yara biyune cikin ƴaƴan gidan. Namiji babba sai mace budurwa guda ɗaya. Sau ɗaya a wata shekara dasu Nu'aymah suka tada billi ita da Adawiya aka tafi dasu su biyu. Aiko Hajjo ta shawo wahala da su, tun daga lokacin ta rantse bazasu sake bintaba sai sunyi hankali. Sai dai idan wani zaije cikin iyayensu mata su bishi.
     To a wannan karon koda Baba malam yay mata magana a mamakin kowa sai tace da Nu'aymah zataje. Babu wanda hakan bai bashi mamaki ba. Amma sai babu wanda yace wani abu tunda dama itake zaɓar abokin tafiyartata.
    Amsar passport ɗinsu baba malam yay ya bama Ahmad yay musu komai su biyun, sai shi Ahmad ɗin da zaije a wannan karon tare da hajjon.
 Haka kawai sai Nu'aymah ta tsinta kanta da rashin jin ɗokin zuwan, duk da kuwa tana matuƙar son rayuwa a ƙasar saudia saboda dalilan data ginu dasu a cikin rai game da ƙasar.
 Ta samu hajjo a ɓoye ta roƙeta akan ta canja ta da ko Amal ko Yusrah, ita batason zuwa batajin daɗin jikinta. Harara Hajjo ta watsa mata tana taɓe baki. Batare da tace mata cikankiba a zancen ta ɗauke kanta ta maida ga lissafin atamfofin salla da ƴaƴanta kan siya mata danta rabama ƴan uwa da abokan arziki. To da yake bata dawowa sai a daren salla  sai yazam take rabasu kafin ta wuce.
   “Hajjo dan ALLAH mana”. Nu'aymah ta faɗa cike da shagwaɓar data saba yima hajjon tana kwanciya mata a gefen kafaɗa.
  Ture mata kai hajjo tayi tana faɗin, “K da ALLAH jacan shashasha, yo ko shi uban naki wama yake da suna (ba faɗafa zatai ba burgace sabida ɗan farine????) bai isa sakani ko hanani abinda nai niyyaba bareke haihuwar jiya jiya Zainabu. Dukfa take-takenku ina sane dasu. Yanzu bautar UBANGIJI ce ma baƙyason zuwa saboda Abdullahi nacan ko yaya? Ke koma ɗokin ganin ƴar uwarki da duk ta addabi kanta da ƙulafucinki a watannin nan baƙyayi? Ni na tausaya mukune dan kuga juna ke da ita shiyyasama na zaɓi tafiya dake. duk da nasan wahalarku da rashin arziƙi zaku jazamin acan kamar yanda kuka saba”.
 Baki Nu'aymah ta sake kumburawa tana faɗin, “Ada kenan, sai akace miki kullum zama zamuyitayi jiya iyau Hajjo, yanzu fa munsan kanmu”.
Baki Hajjon ta riƙe tana ƙyaɓewa, “Oho to lallai sannu uwata Ɗaharatu, keni dalla tashimin a falo koma kizo na aikeki gidan marigayi malam Aminu kikai waɗannan zannuwan na marayun ƴaƴansu”.
   “Ni wlhy hajjo bani da lafiya, ki aiki Amal kosu Muhammad ai basa azumi”.
   “To wlhy ko zakiyi mushe a gidannan kece zaki aikarnan, kuma Umrah babu fashi sai kinjeta. Dan ALLAH idan kunga juna ke da Abdullahin ku babbaka juna saboda takaicin kanku da kukeji. Tunda shima ya zama babban hotiho ya ɗauki fushi da mutane shi mai zuciya. Toni namaga kuturu ƙarewa zuciyar banzarku da kuka gada wajen malam”.
     Nu'aymah bata sake tankawaba, dan ita ɗaya tasan damuwar da take ciki da matsin da take fuskanta daga Adawiya akan Yah Abdallah ta waya. A ganinta suna a nesa da juna kenan inaga sun haɗu, tunda ta tabbata babu fashi a gidan zasu sauka. Tayi imani da ALLAH harta mutu son Yah Abdallah bazai bartaba, ƙilama shine zai zama ajalinta. Kafin ta san matsayin Yusrah da Adawiya a garesa tana fatan ko bayan shekara nawane idan ya gama fushin ya dawo gareta. Amma kuma zuwa yanzun ta haƙura koda sonsa zai halakata. Badan bazata iya zama dasu bane, sai dai kawai tanason tayi sadaukarwa a garesu dukda tasan ta fisu buƙatarsa. 
     Tanaji a jikinta inhar ta matsama kanta saita mallaki Yah Ab kamar yanda ta rayu da wannan burin a ranta to lallai zumincin gidansu da aka gina tunkan samuwarsu yana gab da tsinkewa ya tarwatse ta dalilinsu. Dan kuwa Adawiya da gaske take nuna mata zata iya yaƙi da kowa akan Yah Abdallah a yanzun har ita kanta Nu'aymah. Tana ƙaunar Adawiya har yanzu a ranta, duk da SARAN ƁOYEN da take mata batare da kowa ya saniba daga ita sai ALLAH. Wannan dalilan guda biyu kawai zaisa ta sakama ranta salama da haƙuri. Sai dai kuma haƙura da Abdallah yana nufin harta koma ga ALLAH bazatayi aureba. Shiyyasa ta duƙufa addu'ar ALLAH ma yasa kar a samu likitan da ake fatan ta silarsa ciwonta zai barta. Dan a yanzu bata buƙatar kowacce irin lafiya kuma, tafi buƙatar ta rayu a haka harmai kasancewa ta kasance a gareta. Idan da rabo zasu hadu da yah Ab ɗinta a gida mafi tsada shine Aljannah.
 Da wannna tunani ta ɗauki aikan Hajjo ta fice bayan ta shiga bedroom ɗinta ta ɗakko hijjab dan akwai kayanta anan sashen hajjon.

ABUJA

      “Wai nikam Khadijah mike damunkine haka kwanakin nan? Ina lura dake kullum walwalarki da farincikinki ƙara nisantar rayuwarki da mu'amularki sukeyi. Ko baki da lafiya ne?”.
  Idanun Momyn Ab cike da ƙwalla take kallon mijin nata. Ta matso hawayen nata suka gangaro saman kumatunta tana girgiza masa kai.
Tausayintane ya sake kamashi, dan tsaf ya fahimci damuwar tata akan Abdallah ne da a yanzu ko kiranta a waya baya sonyi sai idan shine ya kirashi ya balbalesa da faɗa. “Khadijah!” ya sake kiran sunanta cike da taushin murya.
Kanta ta sake ɗagawa ta dubesa. Sai kuma ta duƙar tana fadin, “Na'am”.
     “Mike damunki? Ki faɗamin dan ALLAH?”. Jin ya ambaci ALLAH ya sakata sake fashewa da kuka, cikin rawar harshe irin na mai kuka tace, “Abdallah ne, gaba ɗaya Abdallah yaƙi sauka daga fushin rashin Nu'aymah. Kuma nama lura yanzu fushin nasa duk a kaina ya tattarashi bansan miya saka ba?. Bayason kirana sam yanzun, sannan ƙiri-ƙiri yaki yazo ko sau ɗaya mu gansa. Idan wancan karon yana ganin baida iyali rashin zuwansa bai damemuba ai yanzu yana dasu, ita kanta tana buƙatar ganin nata iyayen ai Adawiyan. Kuma wancan karan a rana sai muyi waya sau uku hardama video call. Yanzu kam kaga inma bakai ka kirasa ka baniba sam ya manta dani?”. ta ƙare maganar da rushewa da kuka mai ban tausayi.
 Jawota jikinsa yayi kasancewar darene sosai ansha aruwa. Dan sunama zaune ne sun kammala ƙiyamullaili suna jiran lokacin sahur ya ƙarasa su tashi yaran suma.
  Bayanta ya rinƙa shafawa a hankali shima yana jin ɗacin hakan a maƙoshinsa. dan bama ita kaɗai Abdallah kema hakanba, kowama yana masa. Sai dai su da sauƙi saboda harkar business na shiga tsakaninsu akai-akai. Amma ko ranar sai da baba malam da kansa yay wannan ƙorafin na banza da kowa da Abdallah yayi tun tafiyarsa.
Baki ya buɗe a hankali yace...........✍

SAHFAT PREORDER!


    Wani kaya sai amale ka ɗauka????.

SAHFAT PREORDER maida tsohuwa yarinya.

Kaji masu kawo kayan adon gida dana jiki ƴan gaske.

Ina mata masu ƴan bana bakwai? ko uwargidar da ake shirin kawoma ƴar bana bakwai?. Kai hardama matan gayu ƴan ƙwalisa masu son sabunta gida da kayan ado ƴan waje masu sauƙin farashi da nagarta!.

To ku garzayo dama ta samu, dan SAHFAT PREORDER sune na ɗaya a wannan fanin. Idan kayan kitchen kikeso masu ƙyau da nagarta a farashi mai sauƙi kuma zaki samu a Sahfat preorder. Idan kayan sakawa kikeso na manyan mata ƴan gayu suma akwaisu babu ƙayarya. Jaka ko takalma na nunawa tsara suma ba’a barsu a baya ba harma da mayafai. Hakama kayan ɗaki basu da tsara.

Ni shaidace domin dukkan kayana ta hannunsu nake samu nima. Ku garzayo kuma a dama daku dan nasan zakuyi alfahari da hakan insha ALLAHU.

Kiyi magana ta wannan Number 08142957548 insha ALLAH zaki samu ƙarin bayani ƴar uwa.

Siyen nagari????, maida kuɗi gida???? sai SAHFAT PREORDER????????????????????


ZAFAFA BIYAR 2021


Hafsat miss xoxo????
KIBIYAR AJALI……!
(Sulke baya tareta saita gitta).????????

      Mamu gee????

MIN ƘALB!!????????

    Hafsat rano????

ABINDA KE CIKIN ZUCIYA…!!????????

    Safiyya huguma???? SIRAƊIN RAYUWA????????

     Bilyn Abdull????

SARAN ƁOYE????????

Duka akan farashi mai rahusar gaske.

Kamar haka????????????????

Ɗaya___300
Biyu____400
Uku_____450
Huɗu____500
Biyar_____700

Zaku biya kudinku acikin wannan asusun namu na banki????????

ACCOUNT NO 0812652655
ACCOUNT NAME- HAFSAT LAWAN GAMBO
BANK NAME: ACCESS BANK.

saiku turawa wannnan numban shedan biyanku(evidence of payment)????????

0903 234 5899

IDAN KUMA KATIN WAYANE KO VTU/TRANSFER ZAKU TURA TA WANNAN NUMBER TAREDA SHEDARKU????????

09033181070

????????????????????????????????????????
TEAM—-ZAFAFA BIYAR????????????????

ALLAH ka gafartama iyayenmu????????????.
[5/28, 3:14 PM] Queen Meenali????: INA MASU NEMAN INDA ZASU SAMU INGANTATTUN:
HERBALS APHRODISIAC NA GARGAJIYA BANA HADIN BATURE BA MAI SIDE EFFECT..?

TO KU SAURARA KUJI, DOMIN NESA TAZO KUSA..

ZEE HERBALS APHRODISIAC!
ZEE HERBALS APHRODISIAC!!
ZEE HERBALS APHRODISIAC!!!

MUNZO MUKU DA INGATTTUN KAYAYYAKI WANDA ZASU GYARA CIKI DA WAJE
MUNADA SUPPLEMENT MASU GYARAN JIKI DANA FATA, WANDA ZASA SAKI KIYI SHEKI FATAR KI TAYI LAUSHI. TAYI LUWAI! LUWAI! TAMKAR TA JARIRAI
AKWAI SUPPLEMENT NA KAYAN MATA WANDA ZASU GYARA KI, KIJI KI TAMKAR BUDURWA, SUPPLEMENTS DINMU BASU DA SIDE EFFECT, DOMIN AN HADO SU NE DAGA INGATTATTUN ITATUWA, WATO NATURAL PRODUCTS NE ACIKI.
KAI BA ANAN KADAI MUKA TSAYA BA, MUNA DA INGATTUN KAYAYYAKIN MATA WANDA KESA KISHIYA KWAFA, WANDA DUK INDA SARAUNIYA TAKAI KIN WUCE, WANDA ZASU TSATSO MIKI MARTABAR KI DA KIMAR KI.

AKWAI INGATTATTUN MAGUNGUNA, NA CUTUTTUKAN DA SUKA SHAFI DAN ADAM DAMA JINNU.. KAI DAMA WANDA BAMU AMBATA BA.. ZEE HERBALS APHRODISIAC (MASARAUTAR INGATTATTUN MAGUNGUNA KENAN)
KYAU, ARHA, INGANCI, RAHUSA… SAI ZEE HERBALS APHRODISIAC
MANHAJOJIN MU NA SOCIAL MEDIA: KAMAR INSTAGRAM DA WHATSAPP DAMA NAMBAR TARHON MU: DOMIN SHIIGA KUGA IRIN KAYAYYAKIN MU TUNTUBE MU TA

INSTAGRAM LINK DIN MU:
www.instagram.com/zeeherbalsaphrodisiac

WHATSAPP LINK DIN MU:
https://Zeeherbalsaphrodisiac.whats.bz

NAMBAR TARHON MU
08169380189

KARKA BARI A BAKA LABARI GWARA KA BAYAR.. KIZO A DAMA DAKE YAR UWA, KI ZAMO DAYA DAGA CIKIN KASAITATTUN MATA MASU AJI.. MUNA GARIN KATSINA, SANNAN KAYAN MU MUNA BADA SU AKAN FARASHIN SAYA ‘DAI DAI KO SARI.. MUNA TURA KAYANMU A KO’INA A FADIN NAJERIYA.


No. 19

…………..“Khadijah tabbas kin cancanci ki damu, amma karki manta nima fa ina cikin damuwarne har kashi biyu. Ta shi da taki kema, dan farin cikinki shine nawa dana sauran yarana. Akasin haka duk a wani hali zaki sakamu. Ko yau ke baki lura da yanda Omar ya yini sukuku ba saboda yanda yake ganinki?. Kofa makaranta bai fitaba sai da nai masa magana”.
Zaune ta tashi sosai tana share hawayenta. “Kayi haƙuri to na daina, amma kodan Adawiya ka sakashi ya biyo Hajjo idan zata dawo suzo suyi salla a gidan dan ALLAH itama iyayensu su ganta, sannan musan yaya zaman nasu yake tafiya”.
Ɗan murmushi yay mata da shafa kumatunta. Yace, “Karki damu zanyi ƙoƙarin hakan insha ALLAH, nima gobe idan ALLAH ya kaimu zanje kanon, inaga Omar ne zaiyi tafsir ma gobe idan ALLAH ya kaimun insha ALLAH”.
Kanta ta jinjina masa da addu’ar fatan ganin wayewar garin lafiya.


      Washe gari Abban su Abdallah ya nufi kano domin yin sallama da hajjo da suke shirin wucewa nan da kwanaki biyu. Yako isa da wuri, dan sanda ya shigo gidan ma duk ƴan uwansa na nan, baba malam yanama barci bai tashiba tun ɗazun daya ɗan kwanta. Yaran sun baibayesa da oyoyo kamar yanda suka saba a sashen hajjo, kowa na tambayar ɗan uwansa da suke sa'anni. Yayinda shi kuma yake tambayarsu azuminsu nawa-nawa.
 Ya jima yana biyema shirmensu kafin ya nufi ɓangarensu da babu kowa a ciki, sai dai zuwan nasa Hajjo ta saka Amal da Nu'aymah zuwa su gyara duk da yace ba kwana zaiyi ba. Wanka yaɗanyi ya kwanta kafin azhar ya samu ganawa dasu baba malam, dan yama iske Abba Musbahu yana wajen tafsir danshi na safe ya keyi.

     Bayan gama gaisuwa da Abban su Abdallah Nu'aymah ta nufi sashensu ranta duk a cinkushe, ko kaɗan bata sha'awar wannan zuwa Umrah duk da tana buƙatar hakan fiye da komai a ƙasan ranta. To amma fitinar da take hangoma kanta a tafiyar ta fahimci sai tafi daɗin yawa.
  “Lafiyarki kuwa Nu'aymah? Kina tafiya kamar hankalinki baya jikinki?”. Umm dake zaune a falo tana duba littafin KITABUT TAUHID ta faɗa tana kallonta.
   Zama Nu'aymah tai kusa da ita, tare da ɗora kanta gefen kafaɗar Umm ɗin. “Umm azuminne fa yau nikan tun yanzu na fara jinsa ALLAH, ni koma wajen tafsir bazanjeba yau barci zanje nayi”. Shiru Umm tai kawai tana kallon Nu'aymah, dan gaba ɗaya a watannin nan tana kula da ita kamar akwai abinda ke damunta. Ta zaunar da ita yafi a ƙirga tana tambayarta amma sai tace mata babu komai. Da yake ta san akwai damuwar Abdallah tattare da ita har yanzu sai take danganta yanayin Nu'aymahn da hakan. Shiyyasa ta duƙufa gayama ALLAH akan lamarin. Idan da rabon aure a tsakaninsu ALLAH ya kawo mafita ayi, idan babu kuma ALLAH ya saka musu salama su duka itama ya bata miji nagari.
Jin Umm batace komaiba itama sai bata sakeyin magana ba, tama lumshe idonu kamar mai barci. 
       Sun jima a haka, kafin Umm da taji Nu'aymah ta mata nauyi a kafaɗa taɗan ɗago ta kalleta, numfashi take saukewa a hankali na barci. ta girgiza kai kawai da ɗagota a hankali ta gyara mata kwanciya a kujerar tare da ɗaura kanta saman cinyarta. Aiko kamar jira take saita sake gyara kwanciya da ƙyau a cinyar Umm ɗin.
    “Ita wannan lafiya take kuwa?” Baba malam da Umm bataji fitowarsa da isowarsa wajenba ya faɗa yana ɗaura hannunsa saman goshin Nu'aymahn. Ɗago ido Umm tai ta kallesa dai-dai ya janye hannun ya sake maidawa a gefen wuyan Nu'aymah.
   “Lafiya lau take, barcine kawai”. Janye hannun yay yana sauke ajiyar zuciya da faɗin, “To Alhmdllh, bara na leƙa massallaci Mustapha yasanar min da zuwan baƙi”.
Kanta ta jinjina masa cike da girmamawa, tare da masa addu'ar dawowa lafiya. Da amin ya amsa yay gaba. Harya kusa ficewa a falon sai kuma ya tsaya tare da juyowa. “Banji motsin Muhammad ba, shi yana inane?”.
    “Inaga yana ɓangaren Hajjo, dan tun isowar Abbansu na Abuha ya fice”. Umm ta bashi amsa. “Oh Rizwan ɗin yazo ne?”. Yay maganar yana ficewa batare daya saurari amsa daga Umm ɗinba. Itama ganin ya fice ɗin sai batace komaiba ta maida hankalinta ga kallon tafsir ɗin da takeyi yanzun a WISAL HAUSA.

        Kasancewar baba malam da anyi magriba yasha ruwa yake barin gidan sai suka yanke shawarar ganawa bayan sallar zuhur shi da sauran ƴan uwansa biyu dan Abba Musbahu yana Lagos.
Bayan ya kammala da baƙin da sukazo ganinsa bai shigo gidanba dan lokacin salla yayi. Sai da suka idar da salar zuhur ɗin sannan suka shigo gidan a tare ta ƙaramar ƙofa abin sha'awa. Kansu tsaye sashen mahaifiyarsu suka nufa. Inda suka isketa ita kaɗai sai Kubrah dake fashin salla tana barci a kujera. Sallamarsu kuma ta sakata farkawa. Sai ta koma bedroom ɗin hajjo ta kwanta bayan ta gaishesu.
   Duk a ƙasa suka zauna suka zagaye mahaifiyarsu, dan wannan al'adarsu ce inhar suna wajenta basa zaman kujera sai dai ƙasa. Sun gaisheta ta amsa cike da farin cikin ganunsu kamar yanda ta saba. Harda ɗan barkwancinta akan autanta. “Kunzo duk kun zagayeni babu autana”. Dukansu murmushi sukayi, Abbansu Abdallah yace, “Inna ai tunda kin gammu kin gansa”. Dariya taɗanyi irin tasu ta manya. Tace, “Gara dai shima na gansa ɗin dai yaji ɗumina”.
   Dariya suke mata cike da ƙaunarta. Kafin su tsagaita su fara tattauna abinda ya tarasu game da abinda suke tsarawa na hidima bayan tafiyarta. Sun shafe kusan awa ɗaya suna ƙulla abubuwa masu muhimmanci da amfani. A cikin maganganun nasu ne Abbansu Adawiya ke kawo shawarar ya kamata su gayyato bawan ALLAH nan daketa hidima a garesu shan ruwa idan a cikin kano yake inhar yanada halin zuwan.
     Baba malam da shawarar taima daɗi sosai yace, “Mustapha kaga kuma fa kazo da shawara mai ƙyau gaskiya. Dan wlhy bazan ɓoye mukuba inajin matuƙar son ƙwaɗaituwa da ganin wannan bawan ALLAH. Akwanakin nan kodan na saka lamarinsa cikin raina sai nakanta mafarki da shi duk da ban taɓa ganinsaba. Sai dai yanda mafarkin nasa ke zuwamin sai abin yakan zauna cikin raina sosai. Shiyyasa nakeson mu ƙara ƙaimi wajen masa addu'ar fatan alkairi, idanma wani al'amarine ke damunsa ALLAH ke nunamin ta hakan ALLAH ya warware masa”.
   Duk da sun fahimci mafarkin akwai abu mara ƙyau a ciki sai basu takura kansu nason saniba, suka shiga addu'a a garesa da alƙawarin sakashi a duk ibadunsu insha ALLAH. Sunja kusan awa biyu da rabi a wajenta sannan suka fito dan la'asarma tayi. Basu koma ciki ba sai suka nufi massallaci kawai.

____

    Shirye-shiryen tafiyar hajjo da Nu'aymah da Yah Ahmad Umrah ya gama kammala tsaf, insha ALLAH gobe idan ALLAH ya kaimu zasu wuce. Ta kama dai-dai da cikar azumi kwana goma sha biyar kenan.
   Duk hanyoyin da Nu'aymah zatabi nason ganin tafiyar bata yuwu da itaba tabi amma bata samu mafita ba. Hakan yasa taci kukanta ta haƙura ta barma UBANGIJI ikonsa, dan ta miƙa kukanta wajen ALLAH akan wannan tafiya har batasan iyakaba. Ganin al'amarin ya kasa gagara saita ɗaurasa a mizanin hakan shine mafi alkairi a gareta shiyyasa.

  Zaunar da ita Umm tayi tai mata doguwar nasiha akan wannan tafiya, tare da tunatar da ita manyan ibadu da idan taje zata maida hankali a kansu ba shashanci ba. Tsaf Nu'aymah ta riƙe komai a ranta, tareda ƙarfafa ranta akan insha ALLAH zata zama mai himma. Saboda ma ta gujema abinda take gudun ganin daga Adawiya da Yah Abdallah saita ƙudiri niyyar shiga ittiqafin idan sun isa.

    Washe gari ƙarfe biyu na rana jirginsu ya ɗaga zuwa ƙasa mai tsarki ita da Yah Ahmad da Hajjo. Ta tafi cike da kewar Umm da Muhammad harma da baba malam da sauran jama'ar gidan. Musamman ma su Amal da badan basu ƙarasa jarabawarsu guda biyu data rageba da tare zasu tafi.

To Nu’aymah a sauka lafiya. Duk da muna tare dake dan muji yaya wasan zai kaya ke da Adawiya da Yah Abdallah????????????????.


        *_DOCTOR YOOHAN_*

 Kwance yake acan cikin garden ɗin gidan nasu daya ƙawatu da korayen ciyayi da furanni kala-kala, tare da ƴaƴan itatuwa da ALLAH yayma bayinsa ni'ima da su. Kwanakinsa biyu kenan a Abuja ya ɗauki hutu na kwanaki goma ne saboda jikinsa daya ɗan motsa masa. 
    Fuskarsa a cinkushe take matuƙa, dan rashin walwalarsa ta yau ta ɗara ta kullum ma. Sosai zuciyarsa ke a matuƙar ƙuntace, shiyyasa ma ya waro kansa daga cikin gidan ya dawo nan cikin garden ɗin a gaban swimming pool dake gefe ya kwanta. Haka yake, a duk lokacin da abin nasa ya motsa yakan tsinci kansa cikin wani irin ƙunci da takuruwa. Komai na rayuwa yakan koma masa baƙiƙƙirin. Yaji ya tsani komai da kowa har aikinsa na taimakon al'umma da yake matuƙar so fiye da komai. Idan yana a wannan halin ko magana baya sonyi da kowa ciki harda iyayensa kuwa. Shiyyasa da ya motsa sai yay wuf ya ɗauki hutu domin samun damar zuwa ya keɓance kansa batare da ya shiga haƙƙin wani ba.
 Duk yanda iskar garden ɗin dana ruwan pool ɗin ke kaɗawa da ƙamshin furanni masu daɗi sam bayajin wani nishaɗi tattare da shi. Hasalima yazo wajen ya zaunane badan yay farin cikiba ko yaji daɗi. Hannayensa da yay filo dasu ya sake gyarawa yana yamutsa fuska kaɗan. Sai kuma yaja tsaƙi tamkar wanda akaima wani abu.  
   A haka Solomon ya shigo cikin garden ɗin a ɗarare, dan yafi kowa sanin idan ogan nasu na irin wannan yanayin babu mai raɓarsa a gidan har iyayensa, suko wani lokacinma sallamarsu yake daga gidan gaba ɗaya ma.......
   Duk da Yoohan yaji motsin mutum a wajen baiko motsaba, har sai da Solomon yay magana cike da rawar baki, “O...Oga good everning, dama saƙone aka kawo maka daga hannun manager ɗin com.......” kasa ƙarasawa yay saboda yanda Yoohan ɗin ya buɗe fararen idanun nan nasa da suka rine suka koma jajaye a kwanakin nan uku da ciwon nasa ya motsa.
   Yanda yake jifansa da kallon ba ƙaramin tayar masa da hankali yayiba, ya ɗanja baya kaɗan dan yana shawarar juyawane kafin abinda baiyi zatoba ya afku yanzun nan. 
  Yoohan da duk yake kallonsa ta ƙasan ido ya maida idanunsa ya lumshe batare da ya nuna alamar yama san da zaman Solomon ɗin a wajen ba. Juyawa Solo yayi da sauri yabar garden ɗin, dan zuciyarsa ta bashi shawarar gwara ya juya yaje ya ajiye masa saƙon a ɗaki idan ya gadama ƙila ya duba daga baya.

     Shigowar Solomon falon ya saka madam Chioma dake cike da tsantsar damuwar halin da Yoohan ɗin ke a ciki ta ɗago tana kallonsa. Risinawa Solomon yay ya gaidata yana nuna mata abinda ke hannunsa da faɗin, “Ma'am zan ajiyema oga wannan a ɗakinsa”.
    Muryar Madam Chioma a cinkushe tace, “Yana ina?”. “Yana garden kwance Ma'am” ya bata amsa cike da girmamawa. Batace komaiba sai miƙewa da tai ta nufi ƙofa, shi kuma Solomon ya nufi sama dan ajiyewa.

   A yanda Solomon ya tafi ya barsa haka Madam Chioma ta shigo garden ɗin ta iskesa itama. Duk da tana tsoron abinda zai iya biyo baya haka ta ƙarasa garesa cikin sanɗa. A gaban kujerar da yake kwance irin wadda ake ajiyewa a gaban swimming pool ɗin nan ta tsugunna saitin kansa. Duk da a yanzunma yanajin motsin sarai bai buɗe idanunsa ba harta kai hannunta kan sumarsa dake a hargitse yau tamkar ba itace ke masifar ɗaukar gyara ba. ta ranƙwafa kanta saman fuskarsa tamkar zatai masa kiss. yanda takai bakinta gab da nashi ya sakashi saurin saka hannunsa ya ɗaura saman bakinsa yay musu katanga. Sannan ya sake saka ɗayan hannunsa da sauri ya riƙe nata data tura cikin gashin kansa, ya buɗe jajayen idanunsa sosai a kanta. A take taga wani fushi na tattaruwa saman fuskarsa mai saka bantsoro ga duk mai kallonsa. Saurin girgiza masa kai ta shigayi cike da kame-kame tana faɗin, “Relax my baby”. Tai maganar jikinta har ɗan rawa yake na tsorata da yanayinsa dan tayi zaton barci yakeyi da farko.
       Batare da yace mata komaiba ya miƙe zaune tare da sakin hannunta daya damƙe, sai kuma ya miƙe ya saka Slippers ɗinsa yabar garden ɗin gaba ɗaya batare da ko waiwayarta yayiba.
 Binsa tai da kallo idanunta na cika da ƙwalla, babu abinda zaka iya hanga a gareta sai tsantsar damuwa da tashin hankali. Kasa tashi tai a wajen har tsahon wani lokaci. Sai da tai kuka sosai kafin ta iya miƙewa tabi bayansa.

  Yoohan da tuni ya shige ciki yana shiga sashensa ya maida ƙofar ya kulle tare da barin key ɗin a ciki dan karma Mom ɗin tace zata biyosa. Kai tsaye ɗakin motsa jikinsa ya shige ya farayi da wani irin yanayi maiban tsoro. Dan komai yana aiwatar da shine fiye da yanda yakeyi idan yana cikin nutsuwarsa. 
  Tsahon lokaci ya kwashe a ɗakin, duk da yanda yay bala'in fita hayyacinsa saboda wahala ya kasa bari ya huta. Sai da yay wujiga-wujiga da shi, daga ƙarshema ya yanke jiki ya faɗi. 
         A take wasu hawaye masu zafi suka shiga gangaro masa a fuska, ya shiga taunar lip ɗinsa ƙirjinsa na sake zafafa, abinda ke kusa da shi ya rarimo yay wurgi da shi, ya sake ɗaukar wani ya ƙara wurgawa. A haka yayta jefe-jefe da kayan ɗakin yana hawaye cike da jin ɗacin da fushi mara dalili.

       Hankalin madam Chioma yay masifar sake tashi fiye da farko. Tunda Yoohan ya fara jefe-jefen nan akan kunnenta ne, taje ta kira su Solomon amma kowa na tsoron shiga ɗakin. Waya ta ɗauka ta kira papa shima. Bugu biyu kuwa ya ɗaga. Da kukanta shaɓe-shaɓe ta sanar masa da duk abinda ke faruwa.
 Duk da papa yasan da yanayin na Yoohan sai hankalinsa ya sake ƙololuwar tashi fiye da da can. Wannan al'amari na Yoohan na bashi tsoro. Sunyi addu'oin a church, sunyi maganin, sunyi na aaibitin amma abu yaƙi barinsa. Tunda suke basu taɓa gamo da mai kalar matsalar Yoohan ba. Shi ciwon nasa bawai wani waje ne ke masa ciwo a jikinsa ba, likitocima kansu sun sanar musu su basa ganin kowacce irin matsala tattare da Yoohan ɗin, ƙwaƙwalwarsa lafiyarta lau. 
      UBANGIJI shine yasan gaibu game da matsalar Yoohan. Dan haka kawai yake tsintar kansa da kasa yin barci. Sai ya jera kwanaki sama da biyar bai rintsaba koda kuwa yanajin son yin barci, ada sanda abin ya fara masa sai ake yimasa allurar barci mai shegen ƙarfi, a kuma haɗa masa da magani. Idan har akai haka yakan samu barci kona awa ɗaya zuwa biyune ya farka. A hankali kuma yana ƙara girma matsalar na hauhawa, sai yazama kobabu ciwon ma baya iya barcin sai yasha maganin ko anyi allura, kuma baya wuce awa biyu zai tashi. Al'amarin sosai ya fara neman taɓa masa rayuwa da karatu, amma da yake yanada ƙwazo sai akaita lallaɓawa.
 A lokacin da karatunsa na likitanci ya fara zurfi sai ya fahimci shan maganin barci da yin allurar barci illace a lafiyarsa da hankalinsa da kuma aikinsa dake cikin manyan burikansa na rayuwa. Ballema da ALLAH ya taimakesa shaye-shaye baya cikin abin sha'awarsa, dan ya jima da fahimtar inhar zaiyi shaye-shaye koda na giyane to bafa zai kai labariba akan burin zamansa likita, sai kuma Asthma da yake da ita, itama ta taka rawar gani wajen sakashi ƙyamatar bushe-bushen hayaƙin samarin zamani. A ɗan tsakanin da ya daina yarda amasa allura, ya kuma daina shan maganin barci yasha matuƙar wahala, komawa yay tamkar wani ƙaramin mahaukaci, (kunsan rashin barci matsalane). Ya koma babu abinda ya keyi sai baƙin rai, abu kaɗan zai hau fushi, baya walwala sam, baison hayaniya, magana ma sai yaso ya keyinta. Karatunsa ma sai ya fara neman yin tangal-tangal. 
 Baya son zuwa aji, akoda yaushe yafi buƙatar zamansa a hostel shi kaɗai, idan kuma ya fito sai ya koma can gefe guda ya zauna inda mutanema basa gilmawa. Duk da wannan tashin hankali da Yoohan yake a ciki yana nan akan bakansa na daina yarda ayi masa allurar barci ko yasha magani, ya yarda zai jure duk wani matsi da rayuwa zatazo masa da shi dan ya samu ya sai-saita rayuwarsa kodan samun cikar burinsa. Aikam ya jigatu, dan a tsakanin badan Rich ba da ƙwaƙwalwarsa ma zata iya taɓuwa.
  A cikin wannan yanayin da ya tsinta kanshi a wata ƙasa suka sami hutun sati biyu. A wannan karon sai ya haɗa kaya yace shi zaije gida 9ja hutu. Rich yayi mamaki matuƙa, dan yasan burinsu shine bazasu taɓa zuwa gidaba sai sun kammala karatu. Duk yanda yaso tunama Yoohan wannan alƙawarin yaƙi saurarensa sam, haka dole ya barsa ya shirya ya taho Najeriya. Da yazo Najeriyar ma bata canja zaniba. Dan sai addu'in coci da kullum papa yake kan kaisa ai masa bayan nashi, sai kuma masu magani da basu maraba da a kirasu da matsafa kowa na gwada tasa fasahar.
    Ahaka ya kusan cinye hutun babu wani ci gaba, saima gaba al'amarin yakeyi dan yanata ƙara nisanta kansa da zama cikin mutane, ya kuma daina fara'a sam balle walwala. Cikin amincin ALLAH ana saura kwana biyu zai koma makaranta ALLAH ya haɗa shi da wani bawan ALLAH da wani yammaci, ya ɗauka mota ya ɗan fita daga gida suka kusayin taho mu gama da motar mutumin. Hankali a tashe waɗanda suke a waccan motar suka fito, amma shi Yoohan sai yaƙi fita yay zamansa a mota yana cika yana batsewa. Su duk zatonsu wani abun ya samesa, sai da suka buɗe motarsa dansu duba sai suka samesa lafiya lau. Sai dai kuma mutumin kallo guda yayma Yoohan ɗin ya fahimci yana tare da damuwa sosai, duk da wani kallon banza dana takaici da Yoohan ke musu sai yay murmushinsa daya ƙarama kamilar fuskarsa kwarjini, cikin kwantar da murya ya kama hannun Yoohan ya fiddosa a motar, ya saka drivernsa ya ja motar gefe dan a tsakkiyar titi suke. Danma titine na anguwa babu yawan shiga da fitar motoci.
 Da farko Yoohan yaso bijirewa, sai dai kwarjinin mutumin ya cika masa idanu har yaji bazai taɓa iya masa musu ba. Can gefe bawan ALLAH nan yasa suka zauna, ya amshi ruwan da yasa drivern sa ya ɗakko masa a mota ya bama Yoohan yace ya sha. Nanma sai bai musaba ya amsa yasha kusan rabin robar yana sauke ajiyar zuciya a jajjere. Sai da ya huta na wasu mintuna sannan mutum nan ya shiga masa tambayoyi cike da nutsuwa da kulawa. Wasu Yoohan ɗin na bashi amsarsu, wasu kam sai yay masa shiru.
         Duk da bawan ALLAH nan ya fahimci Yoohan ɗin ba musulmi bane sai ya dubesa cike da kulawa yace, “Idan na baka wani magani ka gwada zaka amsa kasha?”. Kallonsa Yoohan ɗin yayi na wasu mintuna yana nazari, kamar bazai amsaba sai kuma can ya ɗaga masa kai alamar “eh”. Murmushi wancan mutumin yayi a wancan lokacin, ya ɗauka goran ruwan da Yoohan ɗin yasha ya rage yay addu'oi a ciki ya bashi. Yoohan ya jima yana kallon ruwan kamar bazai sha ba, sai da yaja lokaci mai tsayi sannan ya kafa baki ya shanye. Murmushi mutumin ya sakeyi, ya kama kan Yoohan yay masa addu'oi ya tofa masa. Daga haka yace masa ya koma gida ya kwanta, insha ALLAH yau sai an gaji da dogon barcinsa a gidansu an tadashi. Da izinin ALLAH kuma indai matsalar barcice ya daina fuskantarta sai dai idan hakan yana cikin doguwar ƙaddararsa.
  A lokacin Yoohan ya tashine kawai ya bar wajen amma ko godiya baima mutuminba dan bawai ya yarda da zancensa bane, tunda shi yasan faɗi tashin da iyayensa keta famanyi akan matsalar. Shi kuma mutumin bai damuba sai kallo kawai ya bisa da shi a ransa yana fata da sakankancewa UBANGIJI zai amsa masa addu'arsa tai tasiri akan Yoohan ɗin.............✍

SAHFAT PREORDER!


    Wani kaya sai amale ka ɗauka????.

SAHFAT PREORDER maida tsohuwa yarinya.

Kaji masu kawo kayan adon gida dana jiki ƴan gaske.

Ina mata masu ƴan bana bakwai? ko uwargidar da ake shirin kawoma ƴar bana bakwai?. Kai hardama matan gayu ƴan ƙwalisa masu son sabunta gida da kayan ado ƴan waje masu sauƙin farashi da nagarta!.

To ku garzayo dama ta samu, dan SAHFAT PREORDER sune na ɗaya a wannan fanin. Idan kayan kitchen kikeso masu ƙyau da nagarta a farashi mai sauƙi kuma zaki samu a Sahfat preorder. Idan kayan sakawa kikeso na manyan mata ƴan gayu suma akwaisu babu ƙayarya. Jaka ko takalma na nunawa tsara suma ba’a barsu a baya ba harma da mayafai. Hakama kayan ɗaki basu da tsara.

Ni shaidace domin dukkan kayana ta hannunsu nake samu nima. Ku garzayo kuma a dama daku dan nasan zakuyi alfahari da hakan insha ALLAHU.

Kiyi magana ta wannan Number 08142957548 insha ALLAH zaki samu ƙarin bayani ƴar uwa.

Siyen nagari????, maida kuɗi gida???? sai SAHFAT PREORDER????????????????????


ZAFAFA BIYAR 2021


Hafsat miss xoxo????
KIBIYAR AJALI……!
(Sulke baya tareta saita gitta).????????

      Mamu gee????

MIN ƘALB!!????????

    Hafsat rano????

ABINDA KE CIKIN ZUCIYA…!!????????

    Safiyya huguma???? SIRAƊIN RAYUWA????????

     Bilyn Abdull????

SARAN ƁOYE????????

Duka akan farashi mai rahusar gaske.

Kamar haka????????????????

Ɗaya___300
Biyu____400
Uku_____450
Huɗu____500
Biyar_____700

Zaku biya kudinku acikin wannan asusun namu na banki????????

ACCOUNT NO 0812652655
ACCOUNT NAME- HAFSAT LAWAN GAMBO
BANK NAME: ACCESS BANK.

saiku turawa wannnan numban shedan biyanku(evidence of payment)????????

0903 234 5899

IDAN KUMA KATIN WAYANE KO VTU/TRANSFER ZAKU TURA TA WANNAN NUMBER TAREDA SHEDARKU????????

09033181070

????????????????????????????????????????
TEAM—-ZAFAFA BIYAR????????????????

ALLAH ka gafartama iyayenmu????????????.

INA MASU NEMAN INDA ZASU SAMU INGANTATTUN:
HERBALS APHRODISIAC NA GARGAJIYA BANA HADIN BATURE BA MAI SIDE EFFECT..?

TO KU SAURARA KUJI, DOMIN NESA TAZO KUSA..

ZEE HERBALS APHRODISIAC!
ZEE HERBALS APHRODISIAC!!
ZEE HERBALS APHRODISIAC!!!

MUNZO MUKU DA INGATTTUN KAYAYYAKI WANDA ZASU GYARA CIKI DA WAJE
MUNADA SUPPLEMENT MASU GYARAN JIKI DANA FATA, WANDA ZASA SAKI KIYI SHEKI FATAR KI TAYI LAUSHI. TAYI LUWAI! LUWAI! TAMKAR TA JARIRAI
AKWAI SUPPLEMENT NA KAYAN MATA WANDA ZASU GYARA KI, KIJI KI TAMKAR BUDURWA, SUPPLEMENTS DINMU BASU DA SIDE EFFECT, DOMIN AN HADO SU NE DAGA INGATTATTUN ITATUWA, WATO NATURAL PRODUCTS NE ACIKI.
KAI BA ANAN KADAI MUKA TSAYA BA, MUNA DA INGATTUN KAYAYYAKIN MATA WANDA KESA KISHIYA KWAFA, WANDA DUK INDA SARAUNIYA TAKAI KIN WUCE, WANDA ZASU TSATSO MIKI MARTABAR KI DA KIMAR KI.

AKWAI INGATTATTUN MAGUNGUNA, NA CUTUTTUKAN DA SUKA SHAFI DAN ADAM DAMA JINNU.. KAI DAMA WANDA BAMU AMBATA BA.. ZEE HERBALS APHRODISIAC (MASARAUTAR INGATTATTUN MAGUNGUNA KENAN)
KYAU, ARHA, INGANCI, RAHUSA… SAI ZEE HERBALS APHRODISIAC
MANHAJOJIN MU NA SOCIAL MEDIA: KAMAR INSTAGRAM DA WHATSAPP DAMA NAMBAR TARHON MU: DOMIN SHIIGA KUGA IRIN KAYAYYAKIN MU TUNTUBE MU TA

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21 22 23 24 25 26 27 28 29 30 31 32 33 34 35 36 37 38 39 40 41 42 43 44 45 46 47 48 49 50 51 52 53 54 55 56 57 58 59 60 61 62 63 64 65 66 67 68Next page

Related Articles

Leave a Reply

Back to top button