SARAN BOYE COMPLETE

Hajjo da duk kejin komai na neman kufce mata tace, “A kaita asibiti, koma minene sai a yisa da ga baya, ciki kuwa harda neman yaron shima. Da yawan mutane wannan suke tsoro ga taimako, shiyyasa bahaushe ke faɗin kasa mutun inuwa ya saka rana. Ko a fuska bazaka taɓa tunain yaron nan zai aikata makamancin hakanba duk da kuwa a farkon shigarsa jikinmu kafiri ne. Ashe ya lulluɓe mune kawai yazo jikinmu ya cutar damu, da alama dama yarinyar nan ya biyo bawai alkairin da muke tsammani daga garesa ba. To kansa yay mawa, ALLAH kuma ya saka mana da gaggawa indai muna da haƙƙi a kansa”.
A tare duk suka amsa mata da amin. Banda baba malam da yay wani ɗan murmushi ya ɗauke kansa kawai. Abdallah ne ya ɗauki Nu'aymah dake a sanƙame ya fita da ita bisa umarnin Hajjon.
An musu ƙarɓar gaggawa saboda halin da Nu'aymah ke a ciki. Musamman ma da suka sami mace ce Doctor ɗin dake dutyn lokacin.
A yanda suka ga likitocin na kai kawo ɗakin da aka saka Nu'aymah hankalinsu ya daɗa tashi sosai. Duk kuma sanda wani ya fito suka tambaya baya basu amsar komai yake wucewa da sauri. Tun suna ɗaukar al'amarin ƙarami har suka fahimci yanada girma sosai, dan Doctors har uku sun ƙaru bayan ta farko. Sai faman yin ƙus-ƙus kuma sukeyi a tsakaninsu.
Cikin ƙarfin hali Abba Musbahu ya dubesu yana faɗin, “Bayin ALLAH inaga idan yarinyar nan ta rasa ranta ne ya kamata ku sanar mana, dan kunata sake ɗaga mana hankali da rashin cewarku komai da kai kawon nan naku”.
Ɗaya da ga cikin likitocin ne ya sadda kansa ƙasa cikin girmamawa yace, “Ai mana afuwa malam, ba muna ɓoye muku komai baneba. Kawai muna akan aikine shiyyasa, amma insha ALLAHU zakuji komai nanda ƴan mintuna kaɗan”.
Shiru wajen yayi babu wanda yace komai, sai dai a zukatansu sam basu gamsu da zancen likitan ba.
★★★
Tunda aka fita da Nu'aymah asibiti baba malam ya koma sashensa. Zaune yake a study room ɗinsa saman wata kujera da ke ɗan lilasa idan yana kanta. Duk da rana ce ɗakin yayi duhu sosai kasancewar bai ɗaga labule ko guda ɗaya ba a ɗakin. Bai kuma kunna fitila ba sai ɗan hasken da ake gani kaɗan kasancewar na hasken rana. Kwance yake a jikin kujerar idanunsa a lumshe ya faɗa duniya mafi nisan zango a tunani.
Tun daga daren jiya har zuwa yanzun zuciyarsa a ruɗani take. Ruɗani irin wanda ƙwaƙwalwa bata iya rarrabe gaskiya da ƙarya, fari da baƙi, haggu da dama........
Motsin da yaji a kusa da shine ya sakashi buɗe idanunsa da ƙyar. Umm ce ya gani cikin ɗan hasken da ɗakin ke da shi. tsaye take a gefensa dafe da kanta alamar tana a cikin matsala. Zumbur ya miƙe ya riƙota ganin tana layi, ga hakki tanayi kamar wadda tayi gudu a cikin sahara.
Kujera doguwa dake a ɗakin ƙwara ɗaya kacal ya nufa da ita, ya kwantar da ita jikinsa sai tsuma ya keyi. “Jannat miya sameki?”.
Duk da halin da take a ciki itama sai da tausayinsa ya kamata jin a yanda yay magana. Tasan ƙarfin hali kawai ya keyi tun jiya akan al'amarin nan, amma shima a ruɗanin yake. Hannunsa ta kamo da ɗayan hannunta, ɗayan kuma na akan ƙirjinta da ke mata azabar zafi tamkar zai buɗe.
“Sooraj inaji a jikina mutuwa zanyi, a wannan karon zuciyata bazata iya ɗaukar wannan al'amarinba. Abban Nu'aymah akwai ruɗani a cikin zancen nan, amma ni kaina na kasa banbance mai gaskiya tsakanin ƴarmu da likitocin nan. Idan da ace likita ɗaya ne ya faɗa sai muce ko haɗa baki akayi da shine, amma kaga harsu uku, ɗayan ma bamu santa ba tunda asibiti suka sameta. Sannan Sooraj a kwanakin cikin nan da aka ambata ya kasance jikin Nu'aymah ban taɓa ganin wani alama na mai ciki tattare da yarinyarta ba, babban tashin hankalina kuma shine tabbas watan da ya shige na azumi banga Nu'aymah tayi jini ba har suka wuce saudia, wancan watan kuma a farkon wata tayisa. Kasan dai ita jininta baya ɓoyuwa a gidan nan saboda lalurar da yake zuwa mata da shi. Sooraj na shiga ruɗani wlhy”.
Ta ƙare maganar da fashewa da kuka.
Shima sai ya ji hawaye na ziraro masa batare da ya shirya yin hakan ba. Dan zuciyarsa ta karye gaba ɗaya. Ya rungumeta a jikinsa sukayi mai isarsu kafin ya ɗagota yana kallon yanda take faman dafe ƙirjin nata har yanzun.
“Jannat bazaki mutuba, bana fata ki tafi ki barni cikin wannan tarnaƙin, nima zuciyar tawa ba iya ɗauka zatai ba. Ki daure dan ALLAH muyi imani da ƙaddara. Amma kamar yanda kike cikin ruɗani a wannan al'amarin wlhy nima haka nake a ciki. Na ƙiyasta duka zuwan Yoohan cikin gidan nan gaba ɗaya ban iya tunano ta yanda har ya samu keɓancewa da Nu'aymah ba. Wlhy zuciyata ta kasa yarda Nu'aymah da Yoohan zasu aikata wannan ɓarnar. Idan kuma nace ban amince sun aikata ɗinba yaya xanyi da waɗan nan hujjojin bayyanannu kuma Jannat? Ya ALLAH ka bayyanar da gaskiyar al'amarin nan koda a cikin Zukatanmu ne ya Rabbi”.
Haka sukaita hawaye har sai da baba malam ya fahimci Umm na neman rasa numfashin ta. Sake ruɗewa yayi ya shiga girgiza ta jikinsa na rawa. Yama rasa miya kamata yay mata, kiran sunanta kawai yake iya yi da iya ƙarfinsa.
Hakanne ya jawo hankalin su Hajjo da ke zaune jigum-jigum suna jiran jin halin da Nu'aymah dake a a sibiti take a ciki. Har rige-rigen shiga sashen sukeyi, gashi duk mazan gidan sun wuce asibiti tare da Nu'aymah, dama baba malam ɗinne kawai ya rage.
A hankali inuwar mutum dake a jikin windown tana kallon su baba malam ta kafar labule ta janye daga wajen. Hakan yay dai-dai da fara shigowar matan gidan. Babu wanda hajijiya bata kusan kwasa ba ganin da gaske Umm bata numfashi, ga baba malam yau duk jarumtarsa da kawaici yana zirar da hawaye............
_★★★
A asibiti bayan sallar la'asar Doctors ɗin suka buƙaci ganin wasu a cikin su Abba. Su duka ukun suka shiga office ɗin, aka bar su Abdallah kawai a waje.
Sai da aka nuna musu wajen zama kafin likitar mace tai ɗan gyaran murya tana kallon sauran ƴan uwanta uku likitocin. Kawuna suka ɗaga mata alamar bata damar magana. Ta amsa musu da kai itama tana sake gyara zamanta.
Cike da girmamawa a garesu tace, “Dama munason muku bayani ne akan abinda ke faruwa idan bazaku damu ba”. Babu wanda ya iya ce mata komai a cikinsu. Dan haka ta cigaba da faɗin, “Maganar gaskiya yarinyar nan tana cikin mawuyacin hali, duk yanda mukaso ceto rayuwarta ma mun gagara, dan aikin yafi ƙarfinmu. Amma a yanzu dai abinda muka iya kawai shine jawo numfashin ta da wasu na'urori kafin a samu mafita. Muna da likitan da zai iya duba matsalarta, sai dai kuma ganinsa shine tashin hankalin musamman da ya kasance yau kwanakinsa goma sha ɗaya kacal da barin nan, sannan aikinsa yana da ƙa'ida bana waje ɗaya bane balle muce muku kai tsaye ga inda zaku iya samunsa. Amma yanzu dai in taƙaice zance matsayinku na iyaye a garemu masu daraja da kima bazamu iya ganin matsala a gareku ba mu kauda idanunmu, dan haka munyi ƙoƙarin nemansa dan muji ko zai iya mana alfarmar ganinsa amma bai ɗaga wayar ba, sai dai mun kira amintaccen sa da ke a garin Lagos a yanzu haka ya tabbatar mana zai bincika mana shi, idan har ya amince zaizo zamu iya ganinsa a koda yaushe. idan bai aminceba yana da wani uzurin kuma shi zaizo ya ga yarinyar ko zai iya bada wata mafita akan matsalar tata dan shima babban likita ne”.
Cike da gamsuwa da bayaninta duk suka karɓa mata da “ALLAH yasa a dace” tare da musu godiya sosai akan wannan taimako da sukai musu. Daga haka suka tashi suka fito kowa yana addu'ar dacewa a cikin ransa da jin tausayin ɗiyar ɗan uwan nasu dama ɗan uwan nasu shi kansa fiye da ko yaushe a yau.
Kamar da wasa sai ga su Abbah sun shafe fin awanni bakwai amma babu labarin likitan da ake tsumayen jira. Su kuma likitocin basuce musu komaiba. Haka suka cigaba da zama jugum-jugum suna addu'oi a zukatansu har tsahon wani lokaci. Shigar lokacin sallar la'asar ne ya sake tadasu suka nufi massallaci, bayan an idar da salla suka sake fitowa suka sake zaman jiran tsammani.
Wata cikkakkiyar awa biyu suka sake sharewa gangariya, Abban Abdallah na ƙoƙarin miƙewa zuwa office ɗin Doctor ɗin nan mace mai suna Doctor Ai'sha yaji yaya ake ciki? sai ya hangota tana fitowa da ga office ɗin nata fuskarta washe da murmushi.
Kafin ya samu damar mata magana yaga ta nufi ƙofar fita da hanzarinta. Kamar zai bita sai kuma ya fasa, ya cigaba da tsaiwa a wajen yana jiran ganin ko zata dawo.
Tsayuwar tasa tayi dai-dai da shigowarsa cike da takunsa na ƙarfi da lafiya, wanda idan baka saniba zaka iya ɗauka tsabar isa ce da izza ke ɗawainiya da shi. Amma sam ba haka baneba, halittar tasa ce kawai haka.
Kansa duƙe yake sakamakon file ɗin Nu'aymah da ke a hannunsa yana dubawa. Ya ɗan rame, hakan ya saka sake fiddo hasken fatarsa da ƙyawun da ALLAH yay masa. Ga wani annuri na hasken ibadar ALLAH tattare da shi, wanda ya sake ɗaukaka ƙwarjininsa da cikar haiba kai kace farin watane ɗan daren sha biyar. Kamar kullum sanye yake cikin suit, na yau ɗin sun kasance Coffee color, sai farar shirt da ke a ciki babu necktie, dan maɓallan Shirt ɗinma kusan uku a buɗe suke.
Doctor Aysha na daga gefen damarsa duk da yaɗan zartata kaɗan a tafiyar kasancewar ya fita tsayi, da alama bayani take masa akan matsalar. Sai Solomon dake ɗauke da jikkarsa a hannu, da Doctor Sa'ad da wasu likitoci biyu da Nurse kusan huɗu na biye da bayansa. Har suka zo suka gitta Abban Abdallah bai ga fuskarsa da ƙyau ba, dan har lokacin kan nasa a sunkuye yake ga file ɗin. A dai-dai ƙofar ɗakin da Nu'aymah ke ciki suka ja birki, su Abdallah da duk suka zuba nusu ido duk suka miƙe, sai dai kafin wani cikinsu yace wani abu. Ya tura ƙofar ɗakin ya shige har lokacin hankalinsa nakan file ɗin.
Iya shi da Doctors ɗin suka shiga, yayinda Solomon da Nurses ɗin suka ja birki a bakin ƙofar.
Sai da ya ƙarasa gab da gadon da Nu'aymah ke kwance sannan ya ajiye file ɗin ya kai dubansa gareta, bai ganeta ba sam, saboda na'urar da aka saka mata mai taimakama numfashinta fita. Ya ɗan ranƙwafo kanta kaɗan ya kai hannu ya zare na'urar mai haɗe da oxygen. Ba ƙaramin tsirgawa zuciyarsa tayi ba, amma saboda son sake gaskta abinda yake tunanin sai ya zare Glasses ɗin idonsa da ya ƙara ƙawata fuskar tashi. ‘Kamar dai itace’ ya ayyana a zuciyarsa cike da kokwanto.
A fili kam sai yay saurin maida mata na'urar saboda ganin yanda ƙirjinta ke sama da ƙasa da sauri-sauri ga jikinta na vibration har gadon kansa na motsawa. Luuu ya ɗanyi da idanunsa ya lumshesu ya sake buɗewa a kanta. murya a cinkushe ya dubi Doctor Aysha a ɗan faɗace ya ke faɗin, “Anyi matuƙar sakaci da lafiyar yarinyar nan da har take neman shiga matakin ƙarshe, ina mamakin yanda mutane suke abu tamkar basu san muhimmacin lafiya ba. Mtsoww!!. Su Iyayenta fa?”.
Dr Sa'ad ne ya bashi amsa da “Haka suke wlhy Doctor, sai kuma an mutu suce likitoci ne da sakaci bayan tun farko sune da matsalar su.........”
Cikin sauri Dr Aysha ta katse Dr Sa'ad ɗin dan bata son ya sake tunzura Dr Yoohan, “Ayi haƙuri sir, duk family nata suna waje, duk da kasancewarsu manyan mutane suna tare da ita tun ɗazun fiye da awa tara wlhy”.
Baice komaiba, ya dai sake kai dubansa ga Nu'aymahn, sai kuma yay azamar ɗauke kansa batare da nasan dalilin yin hakan ba. Juyawa yay zai fita. Doctor Aysha tai saurin ɗaukar file ɗin da ya ajiye su ka sake bin bayansa ita da su Doctor Sa'ad da ke ta faman cika yana batsewa saboda haushin kare dangin Nu'aymah da tayi.
Yanzun ma bai duba kowa ba a cikin su Abdallah yay wucewarsa. Duk da kallo suka sake binsa suma, yayinda Abban Adawiya yaso gane sa, sai dai baiyi magana ba jin suma su Abban Abdallah basu ce komai ba.
Da ga shi sai Solomon suka shiga office ɗinsa, komai ƙal yake, dan tunda Dr Aysha ta tabbatar da zuwan nasa ta saka aka sake tsaftace office ɗin duk da dama ƙa'ida kullum sai an share an goge. Ƙaramin ɗakin hutun dake cikin office ɗin Solo ya ƙarasa. Ganin nanma komai dai-dai yake yanda yasan Yoohan ɗin na buƙata sai ya ajiye jikkar ya fito.
Tsaye ya iske sa yana ƙoƙarin zame rigar suit ɗinsa, har Solomon ɗin ya kai ƙofar fita ya tsinkayi muryarsa ya na faɗin, “Kiramin Dr Aysha”.
“Okay sir”.
Solo ya faɗa da sauri yana ficewa. Hanging ɗin rigar yayi bayan kujerarsa ta zama, sannan ya fara ƙoƙarin kunna Computer ɗin da ke a saman desk ɗin na sa. Yanda yay matuƙar zuba idanunsa ga Computer ɗin zai tabbatar maka abunda yake yi a ciki yana da matuƙar muhimmanci. A haka Dr Aysha ta turo ƙofar bayan tayi knocking ta shigo, dan tasan ba lallai ta samu amsa ba musamman a irin wannan lokacin da ta tabbatar hankalinsa gabaki ɗayansa nakan patient ɗin da ke jiran taimakonsa.
Batare da ya ɗago ya kalleta ba yace, “Matsalar yarinyarnan babba ne, sai dai zan mata wani ƙaramin theatre yanzun, dan haka ku shiryata zuwa theatre room”. Ya miƙa mata file ɗin gabansa yana cigaba da faɗin, “Wannan mahaifinta zai saka hannu anan, ko mahaifiyarta ko mijinta. Kuma dole ɗaya da ga cikinsu ake buƙata kawai”.
Ɗan jimm Dr Aysha tayi. sai kuma komi ta tuna oho, ta gyaɗa masa kai da faɗin “Okay sir”. Daga haka ta fice shi kuma ya miƙe ya nufi ɗakin da ke a cikin office ɗin.........✍
ZAFAFA BIYAR 2021
Hafsat miss xoxo????
KIBIYAR AJALI……!
(Sulke baya tareta saita gitta).????????
Mamu gee????
MIN ƘALB!!????????
Hafsat rano????
ABINDA KE CIKIN ZUCIYA…!!????????
Safiyya huguma???? SIRAƊIN RAYUWA????????
Bilyn Abdull????
SARAN ƁOYE????????
Duka akan farashi mai rahusar gaske.
Kamar haka????????????????
Ɗaya___300
Biyu____400
Uku_____450
Huɗu____500
Biyar_____700
Zaku biya kudinku acikin wannan asusun namu na banki????????
ACCOUNT NO 0812652655
ACCOUNT NAME- HAFSAT LAWAN GAMBO
BANK NAME: ACCESS BANK.
saiku turawa wannnan numban shedan biyanku(evidence of payment)????????
0903 234 5899
IDAN KUMA KATIN WAYANE KO VTU/TRANSFER ZAKU TURA TA WANNAN NUMBER TAREDA SHEDARKU????????
09033181070
????????????????????????????????????????
TEAM—-ZAFAFA BIYAR????????????????
ALLAH ka gafartama iyayenmu????????????.
[5/26, 3:26 PM] +234 806 269 3623: LITTAFIN nan na kuɗi ne. Dan girman ALLAH ki daure ki biya kafin ki karanta, idan kuma bazaki iya biya ba ki haƙura domin ALLAH karki karanta. Idan kuma kin saya dan girman ALLAH karki yaɗa mana????????.
No. 37
…………A tsaitsaye ta iske su Abba gaba ɗaya yanzun kam. Cikin girmamawa ta ƙarasa garesu. Fuskarta ɗauke da murmushi tace, “Congratulations, mun samu nasara babban likitan da ganinsa ke da matuƙar wahala ya amshi gayyatarmu”.
Cike da jin daɗi suka shiga faɗin Alhmdllh.
Da ga haka ta buƙaci magana da su Abbah. Babu musu suka bita office. Bayani tai musu akan ƙa’idar saka hannu da Dr Yoohan ya sanar mata, Abba Musbahu ne ya nuna ai suma iyayen Nu’aymah ne idan sun saka hannun babu damuwa, tunda yayansu baya a kusa, gashi kuma tace za’a shiga aikin ne da gaggawa……..
Ita dai kasa ce musu komai tayi dan suna da girma da kima a idonta, sannan kuma ta tabbatar tunda Dr Yoohan yace a cikin ukun ɗaya ake buƙata dolene hakan za’ayi. Ganin shirun da tayi ne ya saka Abban Adawiya fahimtar akwai matsala, dan haka sai ya kalli ƴan uwansa, “Inaga kawai mu kira Yayan kamar zaifi fa’ida, dan sun fimu sanin muhimmancin sharɗanta hakan”.
Duk sun gamsu da bayaninsa. Abban Abdallah ya ciro waya yay kiran Baba malam. Kirannasa ya shiga wayar baba malam ɗinne dai-dai lokacin da Umm da Hajjo ta shafama ruwa a fuska ta kawo nannauyan numfashi alamar dama suma tayi. Kusan a tare duk suma suka sauke numfashin, musamman ma baba malam da ke jin kamar an tsundumasa a aljanna.
Ba ƙaramin faɗuwa kuma gabansa yayiba ganin kiran ɗan uwansa, amma sai yay ƙarfin halin ɗagawa ya saka a kunne. “Rudwan ta rasu ko?”.
Da dauri Abban Abdallah yace, “A’a Yaya tana da ranta”. Da ga haka yayma baba malam bayanin halin da ake ciki. Kamar baba malam bazaice komaiba. sai kuma ya nisa kaɗan da faɗin, “Shike nan ina zuwa”.
★★★★
Bayan saka hannun baba malam Yoohan da wasu likitocin biyu sai Dr Aysha ta uku suka shiga theatre room da Nu'aymah da ko maƙiyinta ya ganta a wannan lokacin sai ya tausaya mata.
Tun suna irga mintuna har suka koma awanni, dan anyi sallar magrib har isha'i su Yoohan basu fitoba. Duk jikinsu ya kumayin sanyi. amma saboda ƙarfin hali irin na baba malan haka ya bama matan da samarin ƴaƴan nasu umarnin suje gida su huta haka nan. Basu da ikon masa musu akan hakan, amma a kallo ɗaya zaka fahimci ba haka suka so ba, dan Abdallah kasa daurewa yay kansa a ƙasa yace, “Abba da ku kuje kawai, ni zan zauna har su fito insha ALLAHU”.
Da sauri Naser shima yace, “Abba nima ina nan harsu fito dan ALLAH”. Ta ƙasan ido Abdallah ya ballama Naser harara, amma dai baice komai ba.
Shiru kawai baba malam yay yana dubansu, dan shi harga ALLAH tausayi suke bashi. Kafin baba malam yace wani abu Hajjo tace, “Ai mu duka ma tafiyar tamu bamai yuwuwa bace ba, dan ya kamata muga fitowarsu ko ma tafi da ɗan ƙwarin gwiwa. ALLAH dai ya bata lafiya”.
Duk da Amin suka amsa mata. Daga haka kuma babu wanda ya sake cewa komai, suka sake cigaba da zaman jiran tsammani.
Sai kusan ƙarfe tara na dare dai-dai su Yoohan suka fito, duk su baba malam suka miƙe tsaye don son jin yaya ake ciki? Su Doctor Aysha ne kawai suka tsaya musu bayani, dan Yoohan yana ɗakin bai fito ba tukunna.
A tare suka shiga faɗin Alhmdllhi, Koba komai sunɗan sami kwanciyar hankali duk da ba cewa akai Nu'aymahn ta tashi garas bane ba.
Su Dr Aysha da suma fuskokinsu ke nuna alamar nutsuwar jin daɗin yanda aikin ya kasance suka sanar da su zasu iya tafiya gida. Dan Doctor yace babu wanda zai iya ganin Nu'aymah a yanzu, hasalima ba'a buƙatar kowa a gareta.
Duk da ba haka suka so ba sun gamsu da bayanin Doctor Mubarak ɗin, dan haka baba malam yace su wuce ɗin kawai, dama gashi sun baro Umm ita kaɗai a gida sai su Hajarah da ke a tare da ita.
★★★★‡★★★★
Kamar jiya yau ma baba malam ba shine yaja salla a massallaci ba, hakama bayan an idar bai zauna wajen karatu ba ya shiga gida.
Tun a daren jiya ya gama yanke shawarar da ta dace akan wannan al'amarin, dan haka koda ya shigo gidan waya ya ɗauka, ya rubuta gajeren text massege ya tura. Umm na zaune na azkar tana kallonsa. Yanda baice mata komaiba itama batace ɗinba har sai da ya kammala ya ɗago yana kallonta.
Ɗan Murmushin ƙarfin hali tai masa ta duƙar da kanta. Shima sai ya ɗan murmusa cike da jarumta ya kirayi sunanta a hankali. ɗagowa tai ta sake kallonsa. Muryarsa a sanyaye yace, “Ki ƙara haƙuri Jannat kinji, nasan kina cutuwa matuƙa, amma inason ki ɗauki komai matsayin jarabawa, kinsan ita duniya dama UBANGIJI bai yita dan ta kasance abin jin daɗin ɗan adam ba a kullum”.
Ƙwallar da suka cika mata idanu ta haɗiye da ƙyar, ta maida kanta ƙasa dan karya gani tana faɗin, “Insha ALLAHU, ALLAH ya bamu ikon cinyewa”.
“Amen ya rabbi” ya amsa mata shima.
Shiru ɗakin yayi kowa na nazari a zuciyarsa, a haka har gari ya ƙarasa wayewa tangaran. Duk da Umm bazata iya aiki ba haka ta fita cikin dauriya ta lissafama Rabi abinda zatayi. Ita kuma ta koma ɗakin baba malam inda ta tarar zai shiga wanka.
★★★
A ɓangaren Abdallah kam tun a daren jiya ya karɓa Number Yoohan a wajen Ahmad. Babu irin tambayar da Ahmad ɗin bai masa ba akan mizaiyi da Number amma yaƙi faɗa masa. Dan haka ya ƙyalesa kawai yay kwanciyarsa.
Tun a daren ya fito harabar gidansu ya kira wani abokinsa SSS, bayani ya kora masa akan taimakon da yake son yay masa, babu musu kuwa ya amsa zaiyi. ya buƙaci Number Yoohan a take ya tura masa ita da ƙara jaddada masa dan ALLAH zuwa gobe yake buƙatar result.
A safiyar yau kam kusan ƙarfe bakwai da kwata sai ga kiran abokin nasa. Bayan sun gaisa da ɗan tsokanar juna kamar yanda suka saba ya sanar masa aikinsa ya kammala, yaya yakeso ayi?.
“Wow gaskiya na gode matuƙa Mahmood, amma nayi mamakin jin mai Number wai yana a kano, kasan a yanda naji Abuja yake da zama”.
“Eh to, zata iya yuwuwa kanon yazo, dan a yanzu hakama sai da na sake tabbatar da yana a inda muka gansa jiya sannan na kiraka, dama wannan shine amfanin tracing ɗin ai”.
“Gaskiya kam, aiko nagode sosai. Abu nagaba shine zanzo mu haɗu yanzun, dan ina buƙatar a kama min shi ne”.
Dariya sosai Mahmood ya keyi, yace, “Shegen sama mi yayi maka ne? Halan wata harƙallar kuka ƙulla ya doje?”.
“Ai harƙallar dake tsakanina da wannan shegen ta wuce duk yanda zakai tunani wlhy Mahmood, kai dai faɗamin inda kake nazo na sameka kawai”.........
★∆∆★
Sai ƙarfe shida da wasu mintuna ya farka na safiya. ya tashi a ɗan firgice bakinsa ɗauke da addu'ar barci da ALLAH ya bashi ikon riƙewa a lokaci ƙanƙani kamar yanda baba malam ya koyar da shi. Tunda ALLAH yasa ya musulinta yau ne karan farko da zaiyi sallar asubahi a makare. Dan alarm yake sakawa gudun karya makara. Sannan kuma baba malam duk asubahi sai ya kirasa ya tadashi. Hakan na masa daɗi, yana kuma ƙara masa ƙwarin gwiwa. Dalilin makarar tasa ta yau ma dan bai kwanta da wuri bane, dan tun bayan fitowarsu theatre ya duƙufa ne akan binciken matsalar Nu'aymah. Dalilin binciken nema ya sakashi kwana a asibitin, Solomon ne kawai yaje Hotel ya kwana.
Bayi ya shiga ya ɗauro alwala ya fito, ya buɗe jakka ya ciri sallaya da yanzu bai rabo da ita a kayansa duk inda zaije, shimfiɗawa yayi sannan ya zura jallabiya ya tada salla. Yana idarwa saƙo na shigowa wayarsa, sai dai baibi takai ba ya miƙe ya fita dan yana son duba patient ɗinsa.
Kusan mintuna ashirin ya ɗauka a ɗakin da Nu'aymah take sannan ya fito ya koma office. Yanzunma baibi takan wayarba dai ya shiga wanka. Bayan ya fitone ya ɗauka wayar saboda ganin screen ɗin yana haske. Missed calls ne har uku yaci karo da su duk na Mumynsa. Bai kirata ba sai ƙoƙarin duba saƙon da ya gani yay cike da mamakin ganin baba malam ne.
Yana gama duba saƙon yay ƙoƙarin kiran baba malam ɗin. Cikin sa'a kuwa ya ɗaga. Tamkar yana a gabansa haka ya rissina da girmamawa ya gaida shi, shima kuma da ga can baba malam ya amsa masa da kulawa tamkar yanda ya saba.
“Uncle dama naga massege ɗinka ne, ina fatan dai lafiya?”.
“To Alhmdllh Yahya, kawai dai inason ganinka ɗinne, ina fatan bazan shiga aikinka ba?”.
“A'a Uncle babu damuwa, dan yanzu hakama ina cikin kano, insha ALLAHU zuwa anjima zan shigo”.
“Masha ALLAH, ALLAH ya nuna mana”.
Daga haka sukai sallama Yoohan na cigaba da mamakin ganin nasa da baba malam ke buƙatar yi, dan ya ƙara fahimtar kiran nasa nada muhimmanci sosai. Bai kira Momy ba sai da ya shirya cikin ƙanun kaya. Daga wandon har riga duk baƙaƙe ne, sai suka sake fito masa da ainahin farar fatarsa daketa ƙyalli da ɗaukar idanu. Yaɗan saka turare tare da gyara gashinsa da a yanzu yake ɗauke da aski na mutunci, sai sajensa dake kwance luf masha ALLAH.
Jin motsi a office ɗin nasa ya sakashi ɗaukar p-cap ɗinsa jaa ya ɗora a kai, sannan ya zauna bakin gado ya saka takalmansa suma baƙaƙe da ɗan kwalliyar ja kaɗan.
Harya ƙaraso cikin office ɗin da aka gyara tsaf yana zuba ƙamshi Solomon na kallonsa ta ƙasan ido, a ransa kuwa yaba iya ado da kwalliya irinta ogan nasu ya keyi, sai dai yana mamakin ganin a ƴan kwanakin nan gaba ɗaya ya daina saka sarƙa, hakama ƴan kunne baya sakawa. Saurin katse tunaninsa yayi cike da girmamawa ya miƙe tsaye yana faɗin,
“Good Morning sir”.
A taƙaice Yoohan yace, “Same”. Yana zama a kujerarsa. Ɗan kallon Solomon ɗin yayi ya ɗauke kansa da faɗin, “Bani Coffee”.
Solomon na cikin haɗa coffee ɗin akai knocking ƙofar. Izinin shigowa ya bada idonsa akan file ɗin Nu’aymah daya tattara na binciken jiya. Dr Aysha ta shigo hannunta ɗauke da basket. Saman table ɗin ta ɗora tana faɗin, “Good morning Doctor”.
Kaɗan ya kalleta ya ɗauke kansa zai maida ga file ɗin, sai kuma ya sake dubanta ya dubi basket ɗin yana faɗin, “Morning. How are you?”.
“Alhmdllh sir” ta faɗa tana sake faɗaɗa murmushinta ganin yanda yake kallon basket ɗin data ajiye. A taƙaice tace, “Breakfast. ban saniba ko zaka iya cin jagwalgwalon hausawa”.
Ɗan lumshe idanu yay ya buɗe yana maida kansa ga abinda yakeyi da faɗin, “Thanks” a taƙaice.
Bata damuba, sai ma murmushi da ta sakeyi tana amsa gaisuwar da Solomon ke mata fuskarsa a murtuke kamar ma shine boss ɗin. Coffee ɗin daya haɗa ya ajiye gaban Yoohan.
Nanma “Thanks” ɗin Yoohan yace masa batare da ya kallesa ba. Sai da yaja wasu sakanni sannan ya rufe file ɗin ya gyara zamansa da ƙyau yana ɗaukar kofin coffee ɗin da ɗan kallon Dr Aysha da har yanzu take a zaune.
“Matsalar yarinyarnan babbace, ina buƙatar magana da mahaifinta”.
“Sir kana nufin aikin da akai mata jiya ba shine na ainahin matsalarta ba kenan?”.
Sai da ya kurɓa coffee ɗin sannan ya girgiza mata kai, “No ba shi bane dai kai tsaye, dan tana da matsala a ƙwaƙwalwa, wanda shine musabbabin yawaita haddasa mata matsalar saurin suma da wasu matsalolin da akai mata aiki a kansu jiya”.
Cike da tausayawa Dr Aysha tace, “ALLAH sarki, ALLAH ya bata lafiya, gata yarinya ƙarama dan da alama bata wuce 17years zuwa 18 ba”. Yoohan baice komai ba dai. Ganin haka Dr Aysha ta miƙe dan ta bashi damar cin abincin idan yana so. “Bara naje to Doctor, zan duba ko wani cikin ƴan gidan nasu ya shigo”.
Kansa kawai ya ɗaga mata. Ta juya ta fita itama tana jinjina hali irin na Dr Yoohan a ranta. Amma ita duk da haka sam baya ɓata mata rai, sai ma birgeta da ya keyi.
Da harara kuwa Solomon dake can gefe ya raka bayanta.
Dr Aysha na fita su Abdallah na isowa bakin ƙofar office ɗin Yoohan su biyar, dan bayan Abdallah akwai Mahmood da yaransa su uku, sunbar biyu a mota kuma. Mahmood ya ɗaga wayarsa yana faɗin, “Nan shine alama ta nuna, kuma da alama shi ɗinne” ya ƙare maganar yana nuna masa rubutun dake a saman office ɗin mai ɗauke da sunan *_Dr Yoohan Goshpower_*.
Wani Murmushin mugunta da jin daɗi Abdallah yayi, batare da ya jira sunyi knocking ba ya tura ƙofar office ɗin kawai ya shige.
Duk da a yanda aka buɗe ƙofar Yoohan baiko motsaba balle yabar abinda yakeyi. Sai Solomon ne ya miƙe zumbur yay magana cikin daka tsawa. Cikin harshen nasara yace, “Kai wanene zaka shigo nan babu neman izini?”.
Wani banzan kallo Abdallah yayma Solo, sai kuma ya maida idonsa ga Yoohan da har yanzu bai ɗago ya kallesu ba, baima nuna alamar yasan da shigowar tasu office ɗin ba. Hakan sai ya sake fusata Yah Ab, shima a tsawace yace, “Tsaya matsayinka na bodyguard yaro, dan ubangidanka ne dai-dai da ni”.
Solomon zaiyi magana Yoohan da har yanzu ɗin bai ɗago ba ya ɗaga masa hannu alamar kar yace komai. Shirun kuwa Solo yayi ransa na masa ƙuna da takaicin rashin sauran ƴan uwansa.
Cike da ƙasaita Yoohan ya ɗago fuskarsa da ada p-cap ta rufe kusan rabi saboda kansa da ke a duƙe. Manyan idanunsa ya sauke akan Abdallah, sai kuma ya maida kansu Mahmood da ke tsaitsaye suma. Batare da yayi magana ba yay musu nuni da wajen zama cike da basar da yanayin da ya ga fuskokinsu.
Abdallah ne yaja tsaki da ƙarasawa gaban table ɗin Yoohan ɗin, cike da kaushin murya yace, “Ba zaman shan ac da kallon syringe ya kawomu ba, munzo arresting naka ne”.
Ɗan jim Yoohan yayi kamar bazaiyi magana ba, sai kuma ya motsa laɓɓansa a hankali yace, “For......?”. A takaice cike da rainin wayo
A hasale Yah Abdallah ya jefa masa farar envelope ɗin hannunsa.
Da farko Yoohan baiyi niyar dubawa ba, sai dai ganin tsantsar kamannin Abdallah da su baba malam ya sakashi ɗaukar Envelope ɗin, hotunan ciki ya fiddo. A karon farko ƙirjinsa ya ɗan buga saboda cin karo da abinda baiyi tsammanin gani ba. Da kafin ya musulinta ne akazo masa da wannan hoton da yake kissing ɗin Nu'aymah bazai nuna ya damuba, amma a yanzu yana matuƙar sake ƙyamatar wannan ɗabi'ar, idan kuma ya tuna ya aikata akan kuskure yana jin matuƙar takai ci. Kallon na biyu da na ukun yay su ma, amma duk da haka sai ya dake, ya sake tsuke fuska fiye da yanda suka sameta yana jifan Abdallah da yake masa kallon tsana da ƙyama shima da kallo wulaƙanci.
Kafin wani a cikinsu ya samu damar cewa wani abu Dr Aysha ta shigo office ɗin ita da Dr Mubarak, dan sunyi knocking har sau biyu basuji ya amsa ba. A zatonsu ko yayi busy ne shiyyasa suka shigo kawai tunda sunsan babu wani mara lafiya da zai duba bayan Nu'aymah kamar yanda ya sanar musu tunkan yazo.
Da mamaki suke bin su Abdallah da kallon tsoro, sai kuma suka kalli Dr Yoohan ɗin shima. Ganin yanda ya tsuke fuska ya sakasu kasa masa tambayar dake a bakunansu, sai Dr Mubarak ne ya kalli Solomon da ya gama tsumewa da baƙin ciki. “Solomon mike faruwa anan ne?”.
Solomon zai basu amsa Yoohan ya katsesa da faɗin, “Mi kuke buƙata?”. Shiru Solo yayi dan ya fahimci Yoohan ɗin baya buƙatar ya faɗa. Suma jin hakasai duk suka sake maida kallonsu garesa, cike da ƙarfin hali Dr Aysha tace, “Dama mahaifin yarinyar ne ya zo, shine nace a shigo da shi?”.
Kansa kawai ya gyaɗa mata, sannan ya maida dubansa ga su Abdallah “Zaku iya fita ga ƙofa ko”. Ya faɗa cike da tsantsar rainin hankali. Abdallah zaiyi magana Mahmood ya matso da sauri yana nunama Yoohan I'd card ɗinsa. Hakan yayi dai-dai da shigowar Baba malam office ɗin bisa jagorancin Dr Aysha.
Mahmood da ya fara faɗin, “Muɗin jami'ai ne daga hukumar s......” ya kasa ƙarasawa saboda tozali da baba malam. Yoohan ma mamakin ganin baba malam ɗinne ya sakashi sakin hotunan hannunsa saman desk ɗin.
Baba malam kuma da duk ke binsu da kallon mamaki ya sauke idanunsa kan Yoohan a ƙarshe. Takawa yay a hankali zuwa gaban tebirin, ya kai hannu ya ɗiba hotunan dan tun daga inda yake yana hango komai na cikinsu. Ɗauka yay ya sakasu cikin envelope ɗin. Kafin ya samu damar faɗin wani abu saboda nauyi da bakinsa yay masa Abdallah yace, “Abba munafukin nan ashe likita ne anan, dan hak.......”
Baba malam yay saurin girgiza masa kai, mamakinsa na sake bayyana sosai da ganin Yoohan ɗin wai matsayin likita. Koda wasa bai taɓa kawo hakan a ransaba shikam, hasalima ya ɗauka Yoohan ɗan kasuwa ne kawai.
Yoohan dai ya gaza yin magana, kallon baba malam ɗin kawai ya ke ko ƙyafta ido bayayi. Baba malam ya ajiye envelope ɗin yana duban su Mahmood. “Zaku iya tafiya abinku mun gode”. Kamar Abdallah zaiyi magana sai kuma yayi shiru, sai ma alamar su Mahmood suje ɗin kawai yay musu da kai. Batare da Mahmood yace komaiba ya nunama yaransa hanyar fita suka fice badan ransu yaso hakanba.
Bayan fitar tasu babu wanda ya iya sake yin magana a office ɗin har tsahon kusan mintuna biyu, sai Abdallah ne keta antayama Yoohan harara, Solomon kuma na hararsu gaba ɗayansu. Dan duk haushi suke bashi.
Cikin ƙarfin hali Yoohan ya duba Dr Aysha da Solomon. Murya a sarƙe yace, “Kuje zan neme ku”. Babu wanda yay musu a cikinsu suka nufi hanyar fita kowanne da abinda yake kissimawa a cikin zuciyarsa.
“Dama kai likita ne Yahya?”.
Kai Yoohan ya jinjina ma baba malam da yay tambayar, yace, “Eh Uncle”.
Murmushi baba malam yayi a karo na farko, yace, “Masha ALLAH, ALLAH ya sanya albarka, yay riƙo da hannunka wajen aikata alkairi ga al’umar MANZON ALLAH ”.
Cike da jin daɗi Yoohan ya amsa da “Amin” kansa a ƙasa dan ya kasa kallon baba malam ɗin, harga ALLAH kwarjini yake masa matuƙa, musamman ma yanzu da yaga hotunan nan duk da bai tabbatar da alaƙar dake tsakanin baba malam ɗin da yarinyar da har yanzu shi ko sunanta ma bai saniba.
Cike da takaici Abdallah yace, “Abba mutum nan fa shineya lalata rayuwar Nu’aymah, ta yaya zamu cigaba da fiskantarsa kamar munajin tsoronsa?”.
Da turanci Abdallah yay maganar, dan haka Yoohan yaji komai, ya kuma fahimci komai. Sai dai kafin yace wani abu baba malam ya kalli Abdallah fuskarsa na nuna ɓacin rai, sai dai kuma baice komai ba. Yanzun ma shiru Abdallah yay badan yaso hakanba, sai dai yanda yake sauke huci zai tabbatar maka cewar zuciyar ƴan mazan a wuya take.
Fuuu ya fice a fusace da ga office ɗin. Da ga baba malam har Yoohan duk binsa sukai da kallo…………✍
ZAFAFA BIYAR 2021
Hafsat miss xoxo????
KIBIYAR AJALI……!
(Sulke baya tareta saita gitta).????????
Mamu gee????
MIN ƘALB!!????????
Hafsat rano????
ABINDA KE CIKIN ZUCIYA…!!????????
Safiyya huguma???? SIRAƊIN RAYUWA????????
Bilyn Abdull????
SARAN ƁOYE????????
Duka akan farashi mai rahusar gaske.
Kamar haka????????????????
Ɗaya___300
Biyu____400
Uku_____450
Huɗu____500
Biyar_____700
Zaku biya kudinku acikin wannan asusun namu na banki????????
ACCOUNT NO 0812652655
ACCOUNT NAME- HAFSAT LAWAN GAMBO
BANK NAME: ACCESS BANK.
saiku turawa wannnan numban shedan biyanku(evidence of payment)????????
0903 234 5899
IDAN KUMA KATIN WAYANE KO VTU/TRANSFER ZAKU TURA TA WANNAN NUMBER TAREDA SHEDARKU????????
09033181070
????????????????????????????????????????
TEAM—-ZAFAFA BIYAR????????????????
ALLAH ka gafartama iyayenmu????????????.
[5/27, 2:14 PM] +234 806 269 3623: LITTAFIN nan na kuɗi ne. Dan girman ALLAH ki daure ki biya kafin ki karanta, idan kuma bazaki iya biya ba ki haƙura domin ALLAH karki karanta. Idan kuma kin saya dan girman ALLAH karki yaɗa mana????????.
No. 38
………….Duk yanda su Abdallah sukaso a tuhumi Yoohan tun a asibiti game da zancen Nu’aymah baba malam ya hana, hakama su Abba basu bada goyon baya ba.
Zuwa yanzu dai Yoohan ya fahimci alaƙar baba malam da patient ɗinsa. Ya kuma gane Nu’aymah. Sai dai taka maimai abinda bai gama fahimta ba shine hotunan da Abdallah ya kawo masa da tsantsar ɓacin ran da yake ganni tattare da samarin gidan su baba malam ɗin gaba ɗaya harsu malam ƙarami da ya fara sabo da su.