NOVELSUncategorized

YAR SADAKA 29&30

???????? *’YAR SADAKA..*????????


*STORY & WRITING BY…*
         *BY*
*MOMN SULTAN*


*DEDICATED TO…..*
*MMN AMATULLAH*



*SPECIAL GIFT TO…*
*AMARYA SURY BABY.*



2⃣9⃣&3⃣0⃣

Haskene ya gauraye Dakin nan yafara Dube Dube Yana mamakin ta inda doyi yake fitowa,,idansa ya Maida Kan nijlah dake baccinta tana qara juyi cikin gudawan daya gama wanke Mata jiki..
Subhanallah badai yarinyarnan kashin kwance tayi ba,, mashkur yafada Yana Duba jikinsa,,gani yayi Duk Kashi ya gama batasa Hatta wuyansa Saida ya Bata ga Kuma hannunsa daya taba lokacin dayaji laima a jikinsa..

Rasa abinda zeyi yayi ya Kuma nijlah Sai qara matsowa jikinsa take sabida jinta cikin sanyi,,tureta yayi ya daka matsawa Yana Kiran sunanta.
Afirgice ta farka tana addu’a tare da qanqameshi,,take yaji tausayinta sedai be nuna Hakan ba ya sake daka Mata tsawa a Karo Na biyu yace..

Dama haryanzu kina kashin kwance,,to wallahi Bazan laminchi wannan iskancinba Dan haka diapers zanke Samiki..

Kashi Kuma nijlah ta fada tana qoqarin Tashi zaune” hararanta yayi Yana cewa ah ah Karya nayimiki..

Hannu tasa Taji danshi a jikinta Dan haka ta turo baki tana cewa,, Allah bansan nayi ba nidai Naji cikina ya Murda Daga nan naganni a gona Ina Kashi..

Cike da masifa yace,,Toba a gona kikeba Akan katuwar katifa kikayi,,kinga yanzu saikisan yadda zakiyi damu..

Marairacewa nijlah tayi tana Hada hannunta tace,,wallahi bansan yadda Zan gyaraba nidai ka temakeni ka wankemin kada cikina ya kumbura,,wallahi tsami yafara damuna, nijlah ta fada tana toshe hanci..
Sabida haushi mashkur besan lokacin daya cire hannunta Daga Kan hancintaba Yana zazzaga Mata masifa..
Shiru tayi tana sauraransa jikinta Na rawa ta Rasa yadda zatayi dashi,,Dan ita Bata Saba Jin irin wannan fadan ba..

Seda yayi shiru Dan kanshi kafin nijlah ta kalleshi tana murguda baki tace,,
Naga Dai Duk kaika jamin wannan kashin,,Saida Nace kabani tuwan dawa kaqi kabani kaza da irin wannan taliyan ta larabawa Sai yanzu da haka ta faru Zaka Sani gaba kana….doke bakinta yayi da hannu biyu tare da kama kunnanta Yaja sosai Yana Mata kashedi..
Kinsan Allah Daga Yau Kika qara yimin kashin kwance Saina Miki Duka,,yanzu da a gidan mummy kikayi Yaya zanyi da raina,,Ina kikeso nasa kaina nijlah,,Ke haryanzu baki da wayo???
Idanta taf da hawaye tace kayi hakuri Allah Bazan qaraba,,tureta yayi ya Tashi a hankali Yana Kallan jikinsa,,rintse idonsa yayi Yana me Jin takaicin abinda nijlah ta aikata masa..

Yanzu yaya zanyi? 
Ta Ina zanfara gyara jikina Dana wannan yarinyar,,Babu shakka Na Hada kaina da aiki indai irin haka ta cigaba da faruwa..
Tinda nijlah taga ya Tashi itama tafara qoqarin Tashi tsaye tana toshe hanci,,kallanta yayi yayi kwafa Yana cewa,,Idan baki cire hannunki a hanci ba Saina wanke Miki fuska da wannan kashin koba Ke kikayi ba,,Zaki Wani rufe hanci kama kama wanine yayi Miki..

Badan tasoba ya cire hannun sedai takasa hadiye saliva,,Yana Shiga toilet tayi saurin binshi,,harya Shiga ya leqo Yana Mata Magana da Ido,,tini ta gane abinda yake nufi Dan haka ta tsaya tsaye Akan gadon tana kuka..

Air freshener ya dauko yafara feshe Dakin dashi Yana sakin tsaki Akai Akai,,Seda yaji tsamin ya ragu kafin ya dawo Kan gadon..
Daga tsaye yafara cire kayan jikinsa,, nijlah Na ganin Ze zare wandansa tayi saurin rufe Ido tana juya masa Baya..
Babban wandansa ya cire ya rage daga Shi Sai Dan qarami Yana kallanta..
Tana Daga tsaye yace,,kicire wannan wandan kafin nayi boll dake,,kazama kawai,,Ni wallahi tinda nake bantaba aiki cikin dare ba Sai akanki,,Yoko jaririya nadauko Sai haka..
Kukanta ta qara volume shiko yayi shiru Yana sauraranta.

Zuwa can dabata ta fado masa ganin Bata da niyyar cire kayan yace,, shikenan nizan wuci Dayan Dakin Kinga saiki kwana cikin doyi,,da anjima kare yazo ya cinyeki..

Wayyo Allah kaka dan birni ze,,kifa denamin ihu Ko bakisan da makoftaba,,salan suyi tunanin satoki nayi”‘ uhmn uhmn Toni ka ciremin kayan Allah Bazan Iya tabawa ba..

Mamakine ya kamashi ganin yadda ta zage tana kuka takuma Qi taba jikinta ita a dole kyankyami takeji..

Babu yadda ya Iya haka yasa hannu ya cire Mata wandan,nan ya ajiye Kan gadon yasa hannu yajanyota jikinshi nan yafara cire Mata riga,,Yana gamawa ya safketa kasa Shima ya safko,,Gana daya ya tattare bedsheet din da kayan jikinsu ya dauko katuwan Leda yasa ciki,,nan ya Cilla cikin Shara Yana kallan yadda tafara karkarwa sabida sanyi..

Toilet ya Shiga ya Hada ruwa me zafi ya dawo ya dauketa,,cikin ruwan yasata yayimata wanka sosai,,Bayan ya gama Mata ya Bata towel ta daura,,Zaki Iya jirana a waje Nima nayi wankan,, girgiza masa kai tayi tana turo baki..

Banace kidena turomin baki ba,,koso kike Na zuba Miki Ido kinayin abinda kikaga Dama,,a hankali nijlah tace ah ah kayi hakuri..

Bude Mata kofa yayi yace ki zauna anan yanzu Zan fito ba dadewa zanyi b,,Yana gama fada ya Koma ciki yabar anan tsaye tana jin tsoro..

Bayan ya fito ya dauketa suka Koma daya dakin,,shida kanshi ya shafeta da Mai Shima ya shafa,,turarensa ya shafa Mata Yana Kallan yadda tayi Shiru kama ba ita ba,,Kan bed ya Koma hannunsa riqe da nata..

Suna kwanciya bacci ya daukesu,,be Iya tashin asuba ba Sai farkawa yayi yaji Har an idar da sallah,,dasauri ya Tashi ya fada toilet yayi brushe,a gaggauce yayi wanka sabida gajiya dake damunsa Bayan ya gama ya dauro alwala ya fito Yana tsane jikinsa da towel,,kallan Nijlah yayi Yana murmushi tare da Kiran sunanta a hankali..

Wardrobe ya bude ya dauko jallabiya,,nan ya shinfida sallaya ya tada Sallah,,Bayan ya isar yayi addua sosai tare da Neman mafita a al’amuransa..

Nan ya dawo kan gadon Yana tashinta,,ke nijlah tashi mana lokacin Sallah na shigewa..

Uhmn uhmn nika bari bacci nakeji,,Sallah zakiyi Sai ki koma baccin,,kinga nima Shi nakeji..
Kasa Tashi nijlah tayi saima juya masa baya datayi tana turo Dan qaramin bakinta,duk a cikin bacci..

Ganin tana Bata Masa lokaci yasashi fara yamata chakulkuli,,tinda bazaki tashiba ninasan maganinki..
Dariya nijlah tariqayi tana ture hannunsa,,nan ya  dauketa ya kai toilet,,harya juya baya da niyyan tafiya yaji takira sunanshi..

Nini ban iya kunna wannan ba,,ta fada tana nuna kan famfo,, murmushi yayi ya kunna mata,,tsayawa yayi Yana kallanta kafin yace to madam Sai Kuma me,, brushe ta nuna masa tana satar kallanshi.

Bashida yadda zeyi Dan haka ya dauko nasa ya matsa maclean,,amsa tayi tana boye fuska tace nagode..

Idan kin gama ga ruwa nan Sai kiyi wanka ,,ni ah ah,bayan nayi wanka dazan kwanta,,nifa kaka har fada takemin idan taga ina wanka kullum

To suda ba wannan na tambayeki ba,,wanka nace kiyi ko harkin manta laifinki,,shiru nijlah tayi tana kauda fuska,,nan ya fita yana cewa kiyi sauri ina jiranki..

Bata Dade ba ta fito tana turo Baki,,kallanta yayi yaga babu alamun wanka a jikinta, idansa akanta yace,,Amma dai Baki wanka ba???

Daga masa Kai tayi ta kuma qi qarasowa inda yake.
Meya hanaki Yi?

Kai tsaye nijlah tace,,ban iyaba,,

Murmushi kawai yayi kafin ya nuna mata sallaya,, hijabi tasa tayi saurin tada sallah Dan zuwa yanzu tafara gajiya da kallan dayake mata..

Kafin ta idar harya hau kan bed yana bacci yafara daukanshi..

Nijlah kasa hawa gadon tayi Dan tsoro,,nan ta kwanta kan sallaya itama bacci ya dauketa..


**********

Nasir nifa tsoran fita nake Dan wallahi gani nake kama malam ze iya gane wani abu,,dafashi Nasir yayi yana magana a hankali..

Kaga Bello ka kwantar da hankalinka,,ninasan malam baze kawo komai a cikin ransa ba,,tinda dai yana ganina a gari..
To shikenan Nasir Amma fa saika rakani,
Tashi Nasir yayi yana kama hannun bello,,kaga tashi muce kafin lokaci ya qure..

A kofar gida suka Sami malam danya kasa zaman gida,,sabida kukan da kaka ta damesa dashi,,yayi rarrashin harya gaji Dan haka ya dawo kofar gida koze Samu sauqin wani abun..

Yana ganin su bello yafara murmushi yana cewa..
Ah ah Muhammad bello harka dawo,,daga masa Kai yayi suka qarasa kusa dashi suka zauna..

Bayan sun gaisa,,Nasir yayi qoqarin sanar da malam abinda ya faru na rashin zuwan bello birni..

Nisawa malam yayi kafin ya maida hankalinsa ga Nasir yace..

Nasir nifa banaji a jikina yarannan mashkur ze wulaqanta nijlah,,jinake kama ze riqeta Amana kamar yadda muma muka riqeta,,duk da cewar mu dole tane,,sedai ina masa zatan alkairi,,idan kuma yaci Amana shida Allah,,Dan ko bamuyi masa Allah ya isaba nasan zata bishi..

Hakane baba to Dama shiyasa mukaga ya dace muzo mu gayama,,

Godiya sosai malam yayi musu kafin ya tashi ya shiga gida,,shidin ma karya yayima kaka yace bello yadawo lafiya kuma yaga gidan da aka Kai nijlah Dan Shima anyimasa karba ta musammam.

Sosai yakumbo taji dadin labarin malam harta fara sakin ranta daga damuwar datake ciki,,haka ta kwana cikin farin ciki..


*******

Kwana Yasmeen tayi tana fama da kanta ga wani zazzafan zazzabi daya rufeta Banda karkarwa babu abinda take,,ahaka har garin Allah ya waye tana nan nade cikin bargo,,,mama bata iya leqataba sabida haushinta datakeji,,abbane ya fito cikin shirinsa na zuwa office kalllan mama yayi yana cewa..
Hajiya yana ganki ke daya kina karyawa,,ina ita ‘yar lelen take??

Tabe Baki mama tayi tana nuna masa dakinta,,Abba be qara magana ba ya shiga dakin,,nan ya ganta kwance cikin bargo dasauri ya qarasa yana janjan bargon tare da kwalawa mama Kira..

Hajiya hajiya,,Baki da hankali Zaki barmin yarinya cikin wannan hali,,da gudu mama ta qarasa shiga tana cewa alhaji lafiya..

Inafa lafiya duba kiga halinda ‘yar lele take ciki,,wallahi idan wani abu ya Samu yarinyata sainayi maganin wannan yaran me suffar munafukai..

Kayi hakuri ba laifin kowa bane bace laifinta,,shidin mijintane ko Dan ita kadai aka haliccesa dazatasa irin wannan damuwan,,to wallahi bari na gayamiki,,idan ma kashe kanki kikayi shidai baze fasa abinda yayi niyyaba,,shashasha mara wayo,,

Kuka Yasmeen tasa tana karkarwa ta rungume Abba tana nuna mama,,tsawa Abba ya daka mama yana nuna mata hanyar fita..
Fita nace ki fita anan kafin nayi maganinki,,sai yanzu nagane bakya kaunar yasmeen,,ki haifeta da cikinki amma kina nuna mata kiyayya,,kodan ke bakisan zafin kishi ba..

Eh bansani ba,,maganar so kuma sedai ka fadi San ranka Dan ance kaso naka duniya ta qishi,,kaqi naka duniya ta soshi,kuma ni ba qin Yasmeen nake ba..

Kifita nace ko bakiji ba,,fita mama tayi sabida jin ihun na Abba yayi yawa,,mama na fita Abba ya Samu dakyar Yasmeen ta tashi zaune,, nan ya dauka waya ya Kira kanwarsa,,

Hello mami,,daga daya bangaren mami tace na’am Yaya,,barka da safiya..

Abba be iya amsa gaisuwa taba kawai yace idan mubeena na gida ki turomin ita yanzu,,to mami tace tana mamakin yanayin dataji muryan Dan uwan nata..


Daga mummy har aunty lateefah babu Wanda ya iya baccin kirki sai kusan asuba bacci barawo ya dauke mummy,,nan aunty lateefah ta zuba mummy ido tana zancen zuci,,tinanin ta inda zasu bullowa lamarin mashkur take taji mummy ta tashi tana cewa ke lateefah yarannan ya dawo..

Mummy wanne yaro?

Mashkur Mana,,girgiza Kai Yasmeen tayi tana cewa ah ah be dawo ba,,mummy ta Yaya ze dawo yana tare da wancan yarinyar..

Nidai da Zaki yadda da shawarana,,Allah gwara su dawo ta zauna anan gidan kafin muyi maganinta ta fita da qafanta..

Mummy batayi magana ba tace,,bani wayana,,wayan lateefah ta miqa mummy tana kallan abinda zatayi..

Number mashkur mummy ta Kira tana jinjiga qafa..

Mashkur na bacci wayar tafara ringing,,dasauri nijlah ta bude ido tasa hannu ta dauka wayan,,garin tabe tabe ta amsa Kiran..

Nijlah bata San ta daukaba sai jin maganar mummy tayi tana cewa Kai dan ubanka… Mummy bata qarasa magana ba taji nijlah nacewa Wai waye to bacci me wayan yake….







Comment & share







*Momn sultan ce*✍✍✍

Related Articles

Leave a Reply

Back to top button