NOVELSUncategorized

YAU DA GOBE 11-12

 ????????????????????????????????????

  ????YAU DA GOBE ????

????????????????????????????????????????

Story & writing by mmn fareesa

????️11&12

……Cike da mamaki Dr safana ke kallon musty dake kwance kan bed Yana kallon duka “wad’an da kecikin d’akin”azuciyar sa yace kodai mafarki yakeyi ne?”amma yanzun…baby do you love me?”muryar musty takatse ma safana tunani”baby tasaki kuka had’e ga girgiza Kai” tace ba irin son dakakeso ba nakema inamaka SO na y’an uwan taka…tsaki Dr safana yaja had’e da cewa bamasan shirme da shiririta”inzakuyi bayani kuyi bawai kuyita mgn azaurance ba”ummi kuwa d’ukar da kanta k’asa tayi tana tunanin abinda take gudu yafaru kenan…ummi!Dr safana yakira

sunanta”babana ya akayi?”cewar ummin tana kallonsa.ahankali yace abashi abinci yasha da magani”musty yakarbe zancen da cewa abinci d magani bashine damuwata ba Yaya… tab’e Baki Dr safana yyi had’e da cewa kabani mamaki wlh dazaka kwanta ciwo sbd mace”ciwon zaisaka tasoka?”bazaka nemi soyayya agunta ba?dajan ra’ayinta har wata Rana YAU DA GOBE tasoka”bazaka ganeba Yaya”cewar musty awahale”ai dama bana buk’atar nagane d’in”yafad’a Yana hararar zarah had’e da cewa kekuma kizauna sbd ke har yakwanta asibiti”meye yasa bazaki soshiba?”shagwabe fuska zarah tayi had’e da cewa K’ANINA fane Yaya”tsaki Dr safana yyi had’e da cewa so what?”ink’anin kine,kokuwa haramun ne?”cikin tura Baki zarah tace ah ah”yatsina fuska Dr safana yyi yace kuka sani can ta matse muku”inkunshirya fine akasin hakanma fine…bejira cewarta suba yafice…ummi kuwa had’e Rai tayi had’e da ajiye plate din abinci d cup din tea Mai kauri yana turiri”kusada musty tace maza tashi kaci kasha magani” tafad’a fuska a’daure”kafin ta harari zarah tace wuce kije driver yamayar dake gd” musty tamkar yyi kuka haka yayita kallon zarah” yanason su had’a ido tak’i yarda harta fice,ummi ta dubesa tace inada babban dalili Mai k’arfi Wanda nasan duk Daren dad’ewa YAU DA GOBE wata rana gsky zatayi halinta”auta kayi  hakuri da zarah ko kayi k’ok’arin saka soyayyarka aranta”inrabon kace  ka aureta”amma banaso ka aureta kaikad’ai kesonta”kasan dalilina na hakan?”jikinsa asanyaye yace ah ah ummi”tace dalilin farko bazan fad’a ba”YAU DA GOBE zaka sani”dalili na 2.shine bazakaji dad’in Zama da itaba tunda tasan kaike sonta, sannan bazata maka biyayya ba sbd tana ganin ta girmeka”kaga kuwa zaman aure ahaka be yuyuwa”nasan agd zarah namaka biyayya”Amma yanzun tunda kace kana sonta “wannan biyayyar ta rushe tunda kaike sonta”kakuma daure ka rarrashi kanka”kadage da addua da neman zab’in alkhairi inzarah rabonkace zaka sameta”amma saka tunani da damuwa aranka” bashi bane mafita ba… musammun kwanciya ciwon dakayi…ajiyar zuciya musty yasauke cike da gamsuwa da mamakin k’aifin hankali irin na ummi… lallai duk Wanda yaraina mace besan abinda yakeyi ba” ahankali  yace ummi naji shawarar ki,nakuma d’auka”nagode Ina alfahari dake amatsayin uwa ta gari agareni”yafad’a azuciyar sa yasha alwashin cusa soyayyarsa azuciyar zarah…cikin sakin jiki yasha tea da abinci harda magani…ummi ta kara masa pillow jikin bango yajingina suna fira.. tamkar bashine d’azun magashiyan ba….



   Dr safana kuwa cike da jin haushin musty yanufi office d’in Dr Nasir”yasa meshi yagama duba patient Yana hutawa ,suna waya da Mina matarsa”Zama Dr safana yyi had’e da cewa mlm koka kashe wayar Kona fice”Kuna bani mamaki wlh”ace Koda wane time Kuna wahalar dakanku da soyayya… murmushi Dr Nasir yyi yace me yafi ranmu?”yafad’a Yana kashe wayar byn yamata sallama! Yadora d fad’in safana kenan”wacce kuke soyayya Baku daceba d juna ,shiyasa kake ganin bata time ne soyayya”Ina rok’on Allah yasa kaso wata son dabanyi tunaniba….tsaki Dr safana yyi yace d’an iska kawai narasa me my rukky takashe maka “azahiri kake nuna bakason na aureta…hmmm yanzun yamai jiki?”wani tsakin yakoma ja”had’e da labartawa Dr Nasir halin da musty yake…Dr Nasir yace kamasa uzuri abokina”bazaka gane ba sai hakan yazo kanka”

Harararsa yyi yace Allah yatsareni…yauwa Dan Allah Wai me yahad’a ka da yarinyar nan sumayya?”atake Dr safana yahad’e rai..yatashi tsaye yace kaga mlm inkana maganr mutane dena sakota”nalura bakason zamana a office naka ko?”to sai anjima”dariya Dr Nasir yakece da ita”afili yace ohni Nasir safana anya zaka canza?”hmmm mace kawai zata canzaka “irinku inkuka fad’a tarkon SO Baku iyaba wlh…



????????????????????????


Jikin musty da sauk’i bbu laifi”kafin magrib aka bashi sallama suka wuce gd.ummi kawai tashiga cikin gdn”musty da Yaya Aliyu part nasu suka wuce”

     Zarah na zaune tayi tagumi “tana tunanin koyaya jikin musty?”zamanta kenan bayan tagama abincin dare”kasan cewar bataje islamiyar marece ba”da safema bataje skul ba”ahakan ummi tashigo tasameta,ko amsa sallamar ummi batayiba,ta Mike zunbur had’e da cewa ummi yajikin broth ?”Yana inane?”da mamaki ummi keta kallon ta”kafin tace Yana d’akinsu an sallameshi…ajiyar zuciya zarah tayi Takoma ta zauna , yyinda ummi t shige bed room d’in ta..


**************

Hakafa rayuwar gdnsu Dr safana tacigaba da tafiya”tsakanin zarah d musty mgn saita Kama”har kulawar dayake Bata askul ko agd yadena”da bautar siya Mata wannan da wannan dayakeyi ada duk yadena”besakar Mata fuska “mgn saita Kama yake Mata ita”hakan yyi mugun d’aga hankalin zarah “Kai hatta keys din d’akinsa dake hannunta tana gyara Masa dak’i duk ya amshe”sakata tadafa mishi kaza da kaza duk yadena”sannan zai iya shigowa agdn yyita fira da ummi ko kallo bata ishe shiba”babban damuwarta shine wannan week din zaitafi kaduna service”itakuma anan Kano Yaya Aliyu yasa marmata… kasancewar sunkusa degree”kusan wata 3 kenan suna wannan takun sakar”Wanda musty daurewa kawai yakeyi”amma sonta Yana nan daram aransa”



    “”””Bangaren su sumayya kuwa “mamanta na nan da tsohon ciki”yyinda sumayya tashak’u da Yaya Sadiq sosai”Gefe guda Kuma Yana nuna Mata soyayyarsa”saidai tak’i nuna tagane sbd tsoron hjy jamilah mahaifiyar’sa”Abba kuwa yagama gano Sadiq son sumayya yakeyi”musammun akan yawan zaryar da Sadiq d’in keyi part d’in mama dakuma yawan ganinsa tare da sumayyar dayakeyi”wata Rana ma”shike kaita skul”sumayya nason sanarma Sadiq akan matsawar da hamsahak’i kemata tana tsoro aganinta karta zak’e !amatsayinta na agola”hjy jamilah kuwa bata canzaba saima k’aruwa abinta yyi sbd ganin mama da ciki “hankalinta yasake tashi”gefe guda Kuma sai cusa jidda akeyi ga Dr safana shikuma Yana basarwa”har gidn su jidda kezuwa amatsayin takaimusu ziyarar zumunci…bacin gaisuwa besakar Mata fuskar yin wata mgn…sadai hjy jamilah taci alwashin ko Abba Tama mgn “akan yabawa Dr safana umarnin ya auri jidda…



Kamar kullum indai alhamis ne ko jumma’a”sumayya na lanbun gdn tana duba books nata”zaune take kan plastic chair..sanye take da pink &white na lace riga da siket da hijab pink iya gwiwa”fuskarta da light make up”kanta bbu d’an kwali tayi acuci da gashinta”tana duba hand out”k’amshin turaren sa yadaki hancinta”ta d’ago kanta da sauri,suka had’a ido”shagwabe fuska tayi had’e da cewa shine ka tsoratani? tattausan murmushi yyi had’e Jan kujera guda yazauna Yana fuskantarta”ahankali yace sorry my sumy banyi zaton Zaki tsorataba…hmmm kawai tace tana cigaba da abinda takeyi…muskutawa yyi murya can k’asa yace SUMAYYA! Inaso kibani shawara!ajiye hand out d’in tayi jin yakirata bbu wasa afuskarsa”ahankali tace inajinka Yaya”tafad’a batare data kallesa ba and batasan yawan had’a ido dashi…Abba yabani 3 month nafito da wacce nakeso”gashi lokaci yyi amma ban fitarba….meye shawara?”to Yaya dama bakada budurwane?”eh sumy”meyasa to?”da yawan matan sun Zama abin tsoro”amma kinsan akwai wacce nikeso”amma bansanar mataba”murmushi tayi had’e d’agowa ta dubesa tace wacece?”yace hmmm Kumafa nasan abba zaiyi farin ciki dajin hakan.uhumm kawai tace”murmushi yyi yamik’e tsaye yace kinason sanin ko wacece “ahankali tace eh”

1 2 3Next page

Related Articles

Leave a Reply

Back to top button