NOVELSUncategorized

NAJEEB 10

*NAJEEB*
Granny ta kalli zarah tace “Mai yace fad’amin.
Zarah shuru tayi “Tana tunanin Mai zata cema Granny, “domin bazata iya fad’a mata abunda Najeeb d’in yace ba, dan tasan rashin kunya ne, bai kamata ta fad’a mata ba.

Granny tace “ina magana kinyi shuru, “gayamin abunda dan banzan yace, “Nasan zagi na yayi koh?
Da sauri Zarah tace a’a Granny, “cewa yayi shi bata mishi ba, baya Sonta.
Shuru Granny tayi na wani lokaci, “sannan ta sauke ajiyan zuciya tare da kallon hanne tace maza ki koma ciki, “Hanne ta amsa da toh tare da juyawa tayi ciki, “Granny wani irin murmushi tayi tare da fad’in zanyi maganin d’an banza Wlh, zai gane shayi ruwa ne.
Najeeb kam gaba d’aya ranshi a bace yake “bukka ya nufa ya zauna yana jin ranshi na mishi zafi tare da fad’in “wai ita wannan tsohuwar Ina ruwanta da rayuwa na? And naga Dad kaman yana biye mata, “kafad’a ya d’aga tare da fad’in mum dinshi ce, but ni ba uwata bace, Dad zai iyayin abunda tace but banda ni, “wata iska ya furzar mai zafi tare da fad’in ta rasa wanda zata bani sai wa innan kazaman matan munana, y’an kauye, harda wani yaro mummuna duk jikinshi a bushe, tsaki yaja tare da fad’in kamata yayi in d’auki wannan tsohuwar in kaita asibitin mahaukata, ina tunanin ta Fara tabuwa, Inba haka ba ” how can she think of getting me married with that old lady’s,” and she asking me to choose one among them” nace bana so tana cewa in auri Mai yaro, “murmushi ya saki alaman takaici da mamaki, ko an gaya Mata ni aure yana gabana? ” yaushe zan iya ajiye mata a matsayin matata kullum ta dinga takura min, “women are only for fun….. D’an shuru yayi yana nazari, lokaci d’aya ya tabe baki shi ba namiji bane mai son yara ba, har ake k’okarin aura mishi Mai yaro, shi koda an matsa Mai dole yayi aure ai budurwa zai aura, yaushe zai aura wacce ta taba yin aure, “Dan yasan for sure saita dinga tuna mijinta na baya, “and he can’t take it dan yana da kishi, ajiyan zuciya ya sauke tare da fad’in ” ya kamata ma kawai in koma inbar k’asar tun Kafin wannan mental tsohuwar ta sani gaba ta cinye d’anye, mata kaman mayya sai nacin tsiya….. Muryan Zarah yaji tana fad’in bros
D’agowa yayi, ya watsa mata sex eye d’inshi, tare da fad’in what?
Tace Bros ina son magana dakai “Plz kaban dama ka saurara kaji, ” Zan taimaka maka wajan wannan matsalan na granny
Tsaki yayi tare da fad’in, “don’t worry Sis ban d’auki wannan a matsayin damuwa ba, aure ne bazan yiba, sai dai ta mutu, “and inma tayi mistake tasa aka aura min ita saina kashe yarinyar nima a kashe ni, Waye yayi Asara?
Uhm Zarah tace “tare da fad’in amma bros inda zaka ji shawarata da komai yazo maka da sauk’i, ba tare da d’aga hankali ba.
Yace Zarah just leave me for a while, “ban son damuwa.
Tashi tayi tace “OK but in kana bukatan taimako am ready for help, Tana fad’in haka tayi gaba abunta
najeeb yana nan zaune lokaci d’aya ya d’auki wayarshi ya fara dannawa ” wani irin murmushi ya saki lokaci d’aya tare da fad’in yes, tashi yayi ya shiga cikin gidan “inda yaga Granny a falo .
Ganin Najeeb ya shigo yasa tace ja’iri, ka Fara kallon kanka a matsayin ango Wlh
Baiko kalleta ba ya wuce part d’inshi, toilet ya fad’a yayi wanka tare dasa kaya, ya shirya cikin k’ananan kaya, “koda ya fito ya tarar da harda Dad d’inshi a falon da Mum da Granny sai su Zarah.
Har zai wuce Dad “yace zonan,
Zuwa tsayawa Najeeb yayi ba tare da yace komai ba
Mum tace bazaka zo ka zauna ba?
Zama yaje yayi rai a bace, danshi baya son su k’ara mishi wani maganan aure yanzu
Dad yace mun riga mun yanke ko ince mama ta yanke zaka auri wannan yarinyar K…
Da sauri Najeeb yace Dad bazan aureta ba, inada wacce nake so in Aura, so ita zan aura, And Dad akan wani dalili za’a ce in auri wancan Y’ar kauyen? For god sake ko Kai bazaka aureta ba sai ni
Dad kallon d’an nashi yake cikin mamaki, Amma da yake yana son d’an nashi sai bai d’auki maganan da yake fad’a mishi da zafi ba, “yace toh wacece kake so?
Najeeb yace ita zanje in d’auko tazo Nigeria tun jiya,
Dad yace Toh hakan yayi, ka kawo ta sai Mama ta ganta ” Dad kallon Granny yayi tare da fad’in mama yace akwai wacce yake so, yanzu haka ita zaije ya d’auko ki ganta.
Granny ta washe baki cikin jin dad’i tare da fad’in ko shifa, “Aida ya fad’a tun tuni da banje yola ba, Allah yasa Fulani ce itama.
Itbisam kam haushi taji da Granny bata dage akan saiya auri Hanne ba, taso a aura mishi ita,taga yanda zaiyi
Suna nan zaune, baifi awa d’aya da fitan Najeeb ba sai gashi ya dawo shida wata baturiya.
Da sauri Granny ta tashi ta k’are Mata kallo, yarinyar tasa wata doguwar riga wacce ta tsaya mata dai dai Giwa, ga kanta da Attachment brown, Granny salati ta Fara tare da fad’in amma Najeebu ko dan bantan uba, badai wannan zaka aura ba?
Najeeb harara ya sakar ma Granny danya Lura yanda take maganan kaman wannan dinma bata mata ba
Yarinyar idonta nakan Granny da taji tana Yaren daba ji take ba, “Granny tace Dallah dena kallona, da ido kaman na mujiya
Najeeb ya fara nuna ma yarinyar Dad yace “Gina ga Dad d’ina cikin harshen turanci yake mata magana, Hannu ta mi’ka ma Dad suka gaisa, “Granny salati ta saki lokaci d’aya kuma tasa kuka, tana fad’in audullahi gaisawa da wacce ba muharramanka ba, a gabana a gaban iyalinka.
Mum tace mama hakan ba komai bane ai K…… “Dallah Rufamin baki, mara kishin kai Granny ta fad’ama Mum haka, “yanzu mijinki ya gaisa da mace amma kice ba wani abu bane, oh ni wannan zamani duniya ta lalace,
Dad kam shuru yayi ya kasa magana, “NAJEEB in banda hararan Granny babu abunda yake, Gina kam ita mamaki take tare dason jin abunda tsohuwar take fad’i, amma babu dama
Su Zarah da ibtisam kam dariya suke k’asa k’asa
Najeeb yace Dad itace Zan Aura, kallon zarah yayi yace “ki fad’ama wannan granny d’in ga Matar da zan aura nan
Zarah ta fad’ama granny abunda Najeeb yace,
Granny kallon Alh Abdullahi tayi tace, yau ka nunamin ban isa ba, ka kuma nunamin irin tarbiyan da kayi ma y’ay’anka, Indai wannan shine boko tir da wannan karatun, baka da iko da y’ay’anka, sai kuma ta saki kuka
Cikin tashin hankali Dad yaje gabanta yana bata hakuri tare da fad’in “mama nimai biyayya ne a duk abunda kika ce, wlh komai kika yanke shi za’ayi indai bai sabama Shari’a ba, “Dan Allah kibar wannan kukan, kiyi hakuri
Cikin kuka tace Indai na isa muje yola a nema ma Najeebu auran Hanne cikin satin nan, dan ban yarda ya auri wannan yarinyar ba ta nuna Gina dake kallon ikon Allah
Dad yace hakan za’ayi mama insha Allah jibi zamu, sai a d’aura auren.
Mum najin haka ta tashi tabar falon rai a bace, “Wlh bazata yarda a d’aura ma d’anta wannan matan ba, taya za’a mishi auren da baya so, komai zai faru sai dai ya faru Wlh
Dad kallon Najeeb yayi yace yaje ya maida yarinyar ya dawo yana son ganinshi yanzu yanzu, “yanda Dad yama Najeeb magana babu wasa yasa Najeeb yasha jinin jikinshi duk yanda akayi kukan da wannan tsohuwar takeyi akwai abunda ta k’ulla, “Dan haka ya kalli Zarah yace Sis zo muje in ganki
Koda suka fita yasa Gina a mota yace ta jirashi, magana yake da Zarah akan ta fad’a mishi abunda Granny tace
Zarah bata boye mishi komai ba ta fad’a mishi
Ran Najeeb ya baci Sosai lallai kam zaiba Dad d’inshi mamaki indai dagaske yake zai aura mishi wannan y’ar kauyen….
Zarah ce ta Katseshi tare da fad’in Bros inaga in baka son wannan auren why not kace ma Granny kana son ibtisam zata sa a fasa kuma Kun dace kai d……. “Najeeb ya dakatar da Zarah tare da fad’in keep quiet
Kina da hankali kuwa? Ni zance zan aura wannan yarinyar? Kin mafi rainani akan Granny, “let me tell you” Wlh da in auri wannan ibtisam din gwara na auri wacce Granny ta bani, ya k’arasa maganan cikin zafin rai
Zarah ganin haka yasa taja bakinta ta tsuke, ” Dan tasan tunda yace hakan, Toh dagaske yake, cikin ranta tace itama ibtisam din inda tasan nace maka haka ba k’aramin fushi zatayi dani ba, “Toh wai Mai yasa suke ma junansu irin wannan kiyayyan ne haka? Sai kace ba y’an uwa ba, haba abun yayi yawa
Najeeb gaba yayi tare da shiga mota, direct hotel din da Gina ta sauka ya kaita, tare suka shiga dan yana bukatar hutu, koda suka shiga, “Gina ta Fara shafashi tare da fad’in naajit Mai wannan matar take cewa? Naga harda kuka takeyi?
Najeeb yaja tsaki tare da fad’in plz stop asking me dis question. “tare da tashi ya d’auko wata kwalba ta alcohol yasha amma ba Sosai ba,, Yadai kusa shan rabin kwalban
Ganin haka yasa ta kame bakinta ta tsuke, dan tasan Waye Najeeb, abu kad’an yake bata mishi rai, “wani irin tafiyan tsutsa take Mai da hannunta, Tana k’okarin Kai hannunta kan banana d’inshi ya tashi tare da tureta ya fita daka d’akin “tunawa da yayi Dad d’inshi yace ya maida yarinyar ya dawo yana son ganinshi, dan haka gida ya nufa direct
Koda ya shiga cikin gidan Granny da Dad kawai ya gani a falo, zama yayi ta kujeran dake kallon Dad d’in
Dad yace mun yanke zaka aura yarinyar da mama ta zaba maka, saika shirya jibi zamu yola acan za’a d’aura auren
Najeeb ba tare da shakka ba ko kunya, yace Dad Wlh bazan aureta ba, gwara kar kayi gigin cewa zaka aura min ita, so is better kabar wannan maganan, ko ince kabar biyema wannan tsohuwar
Dad yace ni kake fad’ama haka Najeeb?
Najeeb yace gaskiya na fad’a maka, and banga wani abu dana fad’a ba, so baka da right da zaka sani abunda banyi niya ba, Nasan y’ancin kaina….. Tas Tas Dad ya sakar mishi Mari har biyu tare da fad’in ni? Najeeb ni kake fad’ama haka?
Najeeb cikin zafin rai ya tashi yana fad’in Dad do whatever you want amma bazan auri wacce kuke so in Aura ba, ko ince wacce mamanka take son in aura ba…. Dad na k’okarin k’ara maranshi Mum data fito tazo da sauri ta ri’ke hannun Dad Tana fad’in ka kyaleshi
Najeeb part d’inshi ya nufa inda ya fara had’a kayanshi
Mum cikin kuka take fad’in ga irinta nan, gashi nan, tun yaro na k’arami ka daukeshi ka kaishi wata k’asa karatun boko, baka taba tunanin yayi karatun addini ba, wlh yau komai Najeeb yayi laifinka ne tana fad’in haka tabar falon
Da yake da Hausa tayi maganan Granny taji komai, lallai gaskiyan mum ne, komai Najeeb yakeyi laifin audullahi ne, tun Farko irin abunda Granny ta hango kenan, lokacin da za’a kai Najeeb karatu waje bata soba, Amma dan nata ya dage, abunda yasa Granny koda ya dwo bata d’aga hankali ba, tunda taga yana sallah.
Dad kam tsumar tsaye yayi yana mamakin abunda d’an nashi yayi mishi Wanda bai taba zato ba, ko a mafarki ba.
Najeeb kam Bayan ya gama had’a kayanshi, “ya fara jin jiri, alaman giyar da yasha ta gama gauraye jikinshi da jininshi, “lokaci d’aya bacci ya D’aukeshi a zaune inda yake….. Muje zuwa yanzu aka fara…..
~MARYAM OBAM~

Related Articles

Leave a Reply

Back to top button