DARAJAR 'YA'YANA PART 1

DARAJAR ‘YA’YANA PART 1

Takan tabe baki
ta ce, uhm ni rabu dani da wanan zancen, ni dai
insuna yi sauraransu kurun nake yi, don sam in
yaya Aliyu yana fira da iya bana sa baki, domin
tsawa zai daka min ko ya harareni, haka nake
rayawa a raina ba wai dan haka ta taba faruwa
ba.Iya tana yin wainar saidawa a cikin gida,
muna yin ciniki sosai, wani lokacin har da
sha’anin buki suna ko walima duk muna yi da
sana’ar ta take yi mana dawainiyar karatu ni da
yaya Aliyu, sai dan abin da sauran yara suka
kawo mata.Dan suma yanzu ko wanensu yana
nan da dawainiyar iyalansa, karatun ya Aliyu
shine mai cin kudi, dan Alokacin yana karatun
digree sa ne a jami’ar Ahamadu bello dake
zariya.Ku ziyarci blog dinmu domin karanta
Littatafai masu nishadantarwa


Anamdorayi.mywapblog.com
Kokuma ku kasance taredamu a facebook
https://mbasic.facebook.com/HAUSA-
Novels-389304544597988/?e_pi=7%2CPAGE_
ID10%2C737012347
Yana karantar (Engineering) ban san yanda zan
kwatanta muku ra’ayinsa ba, amma shi mutum
ne mai babbancin hali da ra’ayi.Bayan ya
kammala karatun sa ne ya dagewa iya yayyinsa
shifa sai yaje police Acadamy, wato makarantar
horar da manyan yansanda dake wudil jahar
kano, dakyar ya sha kansu.Ko da yake har sai da
kawunsu kannan iya dake Hadeja,Kawu Adamu
ne yaje har gida ya lallashi iya.Bayan ta yarda
tace, to ita fa bata da kudi,yaranta kuma suna
fama da iyalansu, dan haka yaje ya nemi


kudi.Aliyu ya ce, iya ai na fada miki asaida gona
ta, ta gadonmu da aka raba mana.Nan ma da
kyar ta yarda kawu Adamu shineya saida gonar
Aliyu yaje ya amsa, haka yayita zirga zirga
tsakanin kano da kaduna har sai da yayi nasarar
shiga police Acadamy.Ranar farko da yaxo ni
kadaice ina cikin wanke kayan waina bayan mun
tashi, iya bata nan taje kai kudin kayan miyan
wainar gobe, sai kurum naji sallamar sai naga
mutum tsaye kyam da kayan dan sanda riga blue
mai haske wando baki, ga wanan takalmin na su
da hula.Nikuwa dama gani da tsoron Dansanda,
sai naji cikina yana kugi, fuskarshi daure yace,
bakinki yana ciwo ne, bakya iya amsa sallama ko?
Cikin in-ina nace, wa…alai…kassalam.

Ya zuba
min harara, yau ne kika fara ganina ne da har
zaki tsareni da idanu ko na can za maki ne?Na
sunkuyar da kai, a’a ya nufi dakin nace bata nan
ta je wurin Isa mai kayan miya, ya ciji ya tsa to
dauko min makullin dakina najena duba inda na
san iya tana ajewa na dauko masa da zan bashi
sai da na dan rusuna.Ya amsa ya nufi dakinshi
nazo na karasa wanke wanken na gyara gurin ya
fito cikin gajera wando da yar T-shirt irin ta
yansanda,Ina cikin kicin zan dora tafashen kashin
waina, yace baki san mutun yazo kiyi mai tayin
abinci ba, kenan ina ganin rowa zakiyi?Nace nayi
zaton ko kana azumi ne, na ga kullun kana yin
azumi,yace, oh, dama kina samun ido ne har kika
san cewa kullum ina Azumi?To yau ban yi.Nace,
duk abincin ya kare sai sauran tuwo kuma baka
cin dumame, sai dai in ko na dafa maka wani
abu.

Yace barshi nasha cornfilakes,ya juya ya nufi
dakin sa.Na sauke ajiyar zuciya ban san meyasa
ba yaya Aliyu in yana guri bana so in tsaya a
gurin sai in ga duk ya cika gurin,gashi tsananin
tsoransa nake bai dai taba duka na ba watarana
ne dai da yake iya gadanga take ce masa sai tace
in kira mata shi, ni kuma naje nace iya ta ce kazo
gadanga.Wata tsawa da yayi min kadan ya rage
in saki fitsari, ya dora yatsinsa a dan manuni a
goshi na.In kika sake ce min gadanga sai na
zaneki tas kinji ko?Jikina yana bari nace, kayi
hakuri.Don tsoro lokacin har fitsari nayi a
wando.Lokacin da iya ta dawo tai murna da
ganin autanta, nan suka zauna suna yin fira, cikin
hirar ne naji tana yi masa zancen aure, inda ta ce
gadanga dan Allah ka nemi matar aure kasan
shekarunka nawa yanzu?Yayi dan murmushi ni
kwan nasan shekaruna, muke nan kullum cikin
rubuta date of birth ba dole in rike shekaruna
ba?Talatin da uku ne kacal.


Iya tayi dariya talatin da uku shine kacal?Ai dai
cikin sa’anninka ina tsammanin kai kadai ka rage
ba kai aure ba.Ya ce iya ba ni kadai na rage ba,
kin manta da usman?Ta ce, usman bikin shi kafin
Azumi ba kuyi waya bane?Aliyu ya zaro ido, iya
da gaske?Tace, ko jiya na kira shi na fada masa
yau zan shigo shi ne zai ki sanar dani?Iya ta ce
kila sai kazo din za ka ji zancen.Ya ce, iya kiyi
adu’a kawai amma ayanzu ba mata a ga bana,
kokari na in hada wanan course din nawa.Ta ce,
Allah ya taimaka.Ya ce sauran mu wata shida.Ta
ce, to Allah yasa a gama cikin nasara, ni dai fata
na ka zama mai gaskiya da amana, kayi aiki a
kasarka da kishi.Ya ce in sha Allahu, na gode.Duk
ina jin su har suka gama ya dube ni ita waccen
sunyi jarabawar J S. C.E din?Iya ta ce, tin yau she
har sun amso yan zu kici kicin shiga SS din ta
muke yi, ya ce zo ki bani saka makon na ki in
gani, dan nasan bawata kwanya ce da ke ba.

Iya
ta ce, in ji wa?Sadiya boko da islamiya tana da
kokari.Na dauko gaba na yana faduwa na bashi
ya duba sanan ya kalleni babu laifi, amma kina
jin turanci?Na sunkuyar da kai, amma ban iya
bada amsa ba.Ya ce shirmen yaran hausawanmu
kenan, kuna jin tsoro ne kada kuyi ba dai dai ba
ayi muku dariya, to ai gara ayi muku dariyar
sanan a gyara muku.To ni dai daga yau kada ki
kara mun hausa.Har in koma duk kuma zuwan
da zanyi in baturanci zakiyi mun ba bana son jin
maganar ki.Iya ta ce, kuji mun fin karfin hali
gurin gadan ga, wanan ai mugun horo ne.Yare ba
na uwarka ba, ba na ubanka ba kace dole sai tayi
maka magana da si.Ya ce, in ba haka ba yau she
zata iya ga yanda zamanin namu ya zama sai da
karatu, ko da ta gama scondary zaki mata aure?
Iya ta ce, tana samun miji zan sallamata, don
haka kar ka takura mata.Ni dai nayi ciki na barsu
nan suna ta jayayya, yana cewa ilimi ko dan
tarbiyar yara ai ko ni ba zan auri matar da bata
ta shiga jami’a ba.Iya ta ce Allah ya taimaka ni
tawa tana samun miji zan turata can gidan
mijinta shi ne babbar jami’ar ta.Ku dai yan
zamani baku da magana sai dai in kun tashi aure
kun fi son yan boko sabo da tarbiyan yayan ku.

To
amma kada ka manta ni banyi boko ba, amma
duk in da kuka shiga yabon ku akeyi ana sha
awarku.Aliyu yayi dariya, to iya in kin lura ai
baban mu yayi boko, kefa kika ce mun lokacin su
yaya sulaiman suna yara sun zo da home work
shi yake musu.Nima lokacin da na taso sune suke
yi mun ba, tace to wanan ce tarbiyar?Ban ce ilimi
baya cikin tarbiyya ba, amma bashi ne
gundarinta ba.Gun darin tarbiya shi ne ka dora
dan ka kan hanyar Allah da monzo (S. A. W) su
rinjayi komai a kan mazaunin shi.Sanan ka cusa
musu Tauhidi su iya rike Amana,Cika
Alkawari,Tausayin na kasa da taimakonshi,
Girmama na sama, in dan ka ya san wanan sai
ka hada masa da ilimin zamani da na adini shi
ne tarbiyya.Kai in dan ka ya san wadancan ya
rike ko bai je boko ba zai yi rayuwa


ingantacciya.Aliyu ya ce, haka ne zancen ki Iya,
Allah ya sa muma muyi tarbiyar yayan mu kamar
yanda kuka yi mana.Ta ce ameen.Ina da ga ciki
ina jin su na ce, in dai Iya ce duk musun ka da
gardama tana yi maka baya ni sai ka
fahimta.Abin da ya bani al’ajabi da mama ki, da
dare na je kai masa abinci dama fakon sa na yi
tayi dan ba zan yar da wata magana ta hada mu
da shi ba, tunda ya ce sai da turanci, niko dan
tsinta tsinta na iya.Dan haka ina ganin shigarsa
ban daki na dauki abincin na nufi dakin sa na
ajiye zan fita sai na hangi wata mujalla can kan
katifar sa, ni kuma da shegen son kalon hotunan
yan film.Na zata irin tasu ce yan fin din India, sai
na koma na dauko na bude jiki na ya dauki
tsuma ganin mata tsirara.Da sauri na rufe wato
dai mujallar ta tsiraici ce, na sake bude wani
shafin da sauri na rufe, ina fitowa yana isowa
kofar dakin.Ya ce cikin harshen turanci me kike
so na cecikin hausa, dama abinci ne na kawo

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9Next page

Leave a Reply

Back to top button