DARAJAR 'YA'YANA PART 1

DARAJAR ‘YA’YANA PART 1


hakura, amma ba zan taba xuwa ko ina neman
aure ba saboda ina da munmunan halayen da
ban can canta a bani mataba,tace, ni ban ce
ba,ya ce to iya tunda ba a bani a gida ba in naje
nema a wani gida suka bani na cutar dasu tunda
ba su san hali na ba,yana kai aya ya mike tare
da cewa, sai na dawo.Ita kuma lafuzan nashi
suka hanata magana.Ita zahiri ba wai bata son
auren ya Aliyu da sadiya bane, na farko ta san
halinsa, sanan tana tsoron ta tursasa min.Kullun
Aliyu sai yayiwa iya naci amma taki ko ta ga zai
dauko zancen sai ta hade fuska.Wata safiya ina
kwance kangado ina fama da matsananciyar
ciwon mara, dama mun rabu da yin waina tunda
iya tayi rashin lafiya.Ya Aliyu ya ce, a daina yin
wainar duk wata nake wanan ciwon marar.Yaya
Aliyu ne ya shigo gaida iya, bayan sun gaisa ta
ce, har ka shirya fita kenan?Ya ce mata eh, akwai
wani case a hannunsane yana son ya kammala
dashi kafin fitowar(AC) ta ce, to Allah ya taimaka,
a can zaka karya?Ya ce, eh.Sanan yayi shiru ta
ce, da magana ne?Ta sani in har yayi haka to da
magana a bakin sa, ko da yake ta san zancen na
sa daya ne, bai wuce na sadiya ba.Kuma tana
son Sadiyar ta ji ma kunnenta in ta amince
ruwanta don haka ta ce yaya autana?Yace iya dai
maganar Sadiya, Allah iya ba maganar yabon kai
ba, ina da kamalar da za’a bani mata, ya ko ta
gidan waye ‘yar taki ai ba kyau tafini ba,ya fada
cikin sigar wasa, ta ce,duk da haka ba zan baka
ba, kai ita fa tarigata fidda mijinta.Yace dan Allah
iya ki fada mata kinji?Ta ce, au, nice ma zan fada
mata?Lallai ba ma son auran nata kake ba.Ya ce,
ni iya in na fada mata sai naga tamkar zata
rainani ne.Iya ta ce, kun ji girman kan ba?Don
Allah kayi hakuri nifa ka tayar dani,ba zan yarda
ba.Aliyu da ya gaji ya fita.Tun daga lokacin da
naji ya Aliyu ya ambaci sunana na mike zumbur
hankalina atashe,ni Sadiya yaya Aliyu yake nufi
ko wata?Kai in ko nice na more, dan gaskiya yaya
ba irin mijin da zance bana so bane, tab!Wanan
shine tsintar dami akala.A a iya kada kyi min
bakin ciki, ina jin fitarshina fito da sauri ina
kallon iya, ko zata ce wani abu, amma sai ta
shareni, na ta nufintadaga yanda na dauki
al’amarin tunda ta tabbatar naji.Ko daga irin
fitowar da nayi, ganin iya ba zatayi magana ba
sai na ce iya ta dubeni, wai ya Aliyu wa yake so?
Ta tabe baki dan Allah rabu da shi, wai ke, na
dafa kirji da karfi na furta da gaske?Ta ce, zan
maki karya ne?Na ce to iya shine zaki ce mashi


ina da wanda nake so?tace, au.Sharri nayi maki
kenan?Ina ce ke naji kina cewa kin tsaida Idris?
Na ce, ai ban fada mashi ba.Ta ce, meye nufinki
yanzu?Kina so ki ce min kina son Gadanga?Nayi
shiru tare da hade fuska, mamaki ya cikata, ta
ce, Sadiya dama can kina son Gadangan ne?Na
ce, nifa ban ce ina sonshi ba, amma ke meye
dalilin da kika ca baki yarda ba?Iya ta shiga tafa
hannu tana salati.Kin tirke nine lallai sai kinji?To
ba wani dalili bane sai na kare mutuncinki,
gadanga yana da zuciya, gadanga yana da fushi,
sanan ga miskilanci,ina tsoron ki shiga matsala,
gaki karamar yarinya, shi kuma shekaru sun dan
soma ja.Da sauri na ce iya in dai dan wanan ne
na yarda kinji?Ta ce, wai me ya burgekine a dan
sanda duk jikinki ya hau bari?
Ku ziyarci blog dinmu domin karanta Littatafai
masu nishadantarwa Anamdorayi.mywapblog.com
Kokuma ku kasance taredamu a facebook
https://mbasic.facebook.com/HAUSA-
Novels-389304544597988/?e_pi=7%2CPAGE_
ID10%2C737012347
Na ce, to iya gaskiya ya Aliyu ba irin mutumin da
za a ce ba a so bane .Ta ce, ni dai na ce a a ban
yarda ba.Na mike cikin fushi na fita tsakar gida,
da kallo iya ta bini, matuka ta ji mamaki
musanman ta sanni bani da rawar kai.Ni kuma
kicin na shiga na zauna banyi aune ba sai kurum
naga hawaye suna zuba a ido na, ni kaina har
naji mamakin kaina.To da bai ce yana sona ba
fa?Ranar haka na yini har dare, kusan mutum
uku suka aiko kirana naki fita, iya duk tana lura
dani tana kallona ranar bai dawo gida ba sai sha
biyun dare, sanan tunda a subahi ya fita.Yau
sam na kasa sukuni, iya sai kallona takeyi tana
salla, can bayan ta idar ta ce sadiya!Nayi shiru, ta
ce, nasan kina jina ta shi kawaiki tashi, na tashi
zaune ta ce, sadiya ina ganin baki gane nufina ba
game da zancenkike da gadanga shi yasa har kike
fushi dani.Gadanga bahogon mutum ne, ni na
haifeshi na sanshi tun yana dan karamin shi,
gadanga bashi da dadin lamari, amma in kinji
Allah ya baki sa’a.Sai dai ina so ki sani in da
wanda zaiyi farin cikin aurenki da gadanga to ya
biyo baya na,sai dai duk da haka ba zan kasa
fada maki gaskiya ba.Shawarar da zan baki kuma
ki rage rawar kai in ya fahimci kina doki kimarki
ta zube.A zaton iya zan hakura amma sai taji na
ce, in sha Allahu ba zan sami matsala ba.Ta tsura
mini ido haka kika ce?
Nayi shiru ta ce shi kenan, to da sharadi ba zuwa
kawo kara.Da sauri na ce, to,da kallo tayi ta bina
ni dai na tashi na koma makwancina ina
murna.Na zaci da safe zata neme shi ne ta fada
mashi ayi sai kurum ta share, ko da dai ya fita
da wuri, wasa wasa sam taki zancen inaji lokaci
da yawa da ya dauko zancen zata ce don Allah ya
rabu da ita.Sai dai abinda ke bani mamaki,
kullum yanda yaya Aliyu bai can za min yanda
yakemin ba , amma nakanyi uziri cewa kila sai
iya ta amince sanan za mu soma yin tadi.Cikin
haka ne har aka dauki tsawon lokaci muka shiga
shirin zana jarabawa (SSCE) duk na kori samari na
babu wani mai zuwa tunda na fada musu na
tsaida miji.Shikam ya Aliyu bai san na sani ba,
kullum ya zo gurin iya sai yayi mata nacin shi fa
yana nan yana jira ita kuma takan ce mishi kar
ya dame ta, ba ya ce ya fi son yar jami’a ba?Ya
je ya nema.Ni kuma in ya tafi wani sa’in in ce iya
don Allah ba kince kin hakura ba, tunda na
yarda?Sai ta ce min sakarya, dubi fa ko kallo baki
isheshi ba, amma duk kin tsamgwami kanki don
fitina, ni dan kare mutuncinki nake kin abin nan.
Ku ziyarci blog dinmu domin karanta Littatafai
masu nishadantarwa Anamdorayi.mywapblog.com
Kokuma ku kasance taredamu a facebook
https://mbasic.facebook.com/HAUSA-
Novels-389304544597988/?e_pi=7%2CPAGE_
ID10%2C737012347
Usman abokinsa yaji shiru batun maganar Aliyu
da sadiya, sai ya zo gurinshi musanman don
zancen , dama ya kirashi a waya yaji cewa yana
nan.Bayan sun gaisa usman ya ce, aboki wai
haryanxu ban sake jin batunka da yarinyar nan
sadiya ba, in mun hadu baka yimin zancen ba, ni
kuma ban tambaye ka ba.Aliyu ya gyara zama
yayi sanan ya lumshe ido don haushi ya ce,
kabari kawai abokina, haushin maganar nake ji,
shiyasa ban taba yi maka zance ba.Ya miko
hannu ya dafa gyiwar usman abokina ban taba
samun abinda ya bani matsala ba kamar
maganar yarinyar, ni abin haushi duk lokacin da
nayi kudirin hakura dazancen sai na kasa.Kullum
adu’a ta Allah ya yaye min ita daga raina, amma
abin ya faskara.Ko son yarinyar ne ya kamani?
Usman yayi murmushi lallai sonta kake yi, Allah
yasa ita ma ta soka hakan.Aliyu yace ina ruwana
da ita?Iyace kurum damuwata, in da ta amince
shi kenan, amma baiwar Allah nan wai zan cuci
yarinyar ita ba zata bani yarinya karama
ba.Ranar harda cewa na tsufa.Usman yace zanje
in sameta aboki, kada kadamu.Aliyu ya ce, ko
kaje matarnan ba zata yarda ba, na dai fada
mata ni na hakura da yin auren.
.Usman yayi ta dariya tare da zolayar Aliyu da
cewa, aboki ka dai shiga da yawa, to da ka ajiye
duk wani girman kai ka dinga kiran yarinya hira
in taga haka zata fi yarda cewa da gaske kake
yi.Aliyu ya ce ka yarda ni ba zan taba iya kiran
yarinyar ba, ko ba Sadiya ba, kuma sanin kanka
ne ban taba ba, so bansan ta ina zan fara ba.Ba
ta ita fa nake ba, in iya ta yarda tayi hakuri ta
aureni dan da cewa auren sai kuma ya ja tsaki
kada ma ta hakura.Tama ji dadin zancen ta samu
miji irina, Usman ya ce, yabon kai?Aliyu yayi
dariya aboki ka fadi gaskiya, ni da ita wa yafi
kyau?Bai jira amsa ba ya ci gaba na farko dai
kaga ita fari ne kurum ya ceceta….. Usman ya
katsishi au, wai dama haryanzu akwai
mummuna?Ni dai yanzu na daina ganin
mummunaai tunda naga alamun kai ya waye, ba
a zama da kazanta, Aliyu ya ce, haka ne, amma
wani wan wani ne a kyau.Usman ya ce, duk da
ka fi ta kyau dai ita zuciyarka ta zaba, zanyi
maka kokari, zanje in samu iya.Aliyu yace tunda
ka dage jeka din, duk yanda kukayi zamuji.
Kamar yanda Usman ya alkawarta yazo ya samu
iya wajen la’asar ina yi mana tuwo, itakuma tana
zaune a kofar dakinta.Na gaida shi sannan na
dauko masa tabarma ya zauna, na kawo masa
ruwa sanan naje na ci gaba da aiki na.Daga inda
nike ina jiyosu suka gaisa sanan ya fara yi mata
zancen da ya kawoshi.Iya dama akan batun
abokina ne da yar uwarsa sadiya, iya dukkan su
naki ne, a ganina wanan abin farinciki ne.Iya ta
tsuke fuska,Usman ina ganin kimarka, zaifi kyau
ka bar zancen nan bana jin cewa zan
amince.Usman yayi shiru yana tunanin yanda zai
bullo mata.Can ya ce, to shi kenan, amma na so
ki amince domin yana cikin wani hali na son
yarinyar nan, nasan halinshi kin san halinshi,baya
daga cikin mutane ma su magana biyu.Yayi mun
rantsuwar ba zai taba aure ba in ba Sadiya ba,
duk duniya ita yake so.Zaman shi haka nasan
yana damunki.Ta ce in duk duniya Sadiya yake so
ita Sadiyar ya tambayeta ta ce tana sonshi? Nifa
ba zanyiwa yata auren dole ba, don in faranta
masa.Daga inda nake a kicin na da ga hannu ko
nace ya tsa tamkar mai bada amsa a cikin
ajinmakaranta, sanan na kwalawa iya kira!!Ta
kalleni tare da yi mun da kuwa, shi dai baisan
dalilin dakuwar ba, tunda ya bani baya, ita kila
ya zaci laifin nayi mata.
Ku ziyarci blog dinmu domin karanta Littatafai
masu nishadantarwa Anamdorayi.mywapblog.com
Kokuma ku kasance taredamu a facebook
https://mbasic.facebook.com/HAUSA-
Novels-389304544597988/?e_pi=7%2CPAGE_
ID10%2C737012347
Usman ya fahimci nufin iya, shi yasa ya ce mata
Aliyu ya dinga kiran yarinyar suna fira.Ya dubi
iya, to in sha Allahu za mu tuntubi yarinyar, idan
bata amince ba shike nan.Yana fita ya dauko
waya ya kira Aliyu, bugu uku ya dauka. Usman ya
ce, Aboki da farko fara bani goron albishir.Cikin
sauri Aliyu ya ce kada dai ka ce mun
tasaurareka? Usman ya ce, in sha Allahu munyi
nasara Aliyu ya ce shi kenan sai na xo aboki,
gidanka zan sauka kaitsaye daga office yanxu ina
kan wani aiki.Suna cin abinci a falonsu Usman
yana koro mashi bayani duk yanda sukayi a
karshe yace yanzu kaga tana nufin ta yarda sai
dai amma tana so ka kira yarinyar ka nemi
amincewar ta.Aliyu ya tsirawa Usman ido, sanan
ya ce, ai wanan shine mai wahalar, gaskiya a boki
ba zan iya kiranta ba.Usman ya ce, tsoronta kake
jine?Raini ne bana so, yanxu dai kai kaje ka
sameta kuyi magana.Usman ya ce, nima ke nan
zan yi maka yakin neman sonta?Aliyu ya ce, duk
yanda ka ce amma ni in na kira tafa ba ra’ayinta
zanjira ba, umurni xan bata.Usman ya ce, shi
kenan ka bari xanje.Bayan sallar isha’i muna
zaune ni da iya muna cin abinci tare kamar
yanda muka saba, yaya usman yayi sallama shi
da matarshi Anty Abida da yaran shi guda
biyu,tsam na mike daga cin tuwon ina yi musu
sannu da zuwa, suka zauna na kawo musu abinci
da ruwa, sukace yanxu suka tashi daga kan cin
abinci.Na koma tsakar gida bayan na dauki
yarinya wato Ummulkhairi, yarinyar tana da wayo
yar mai kyau taji kitso, na ce Ummulkhairi kina
makaranta? ta ce eh mana, kuma Abban mu yake
kaini har ma da Abulkhairi, nace, iye, to koya
mun karatu.Ta ce, na islamiya ko na boko?Na ce,
a a islamiya dai.Ta gyara zamanta a cinyata ta ce,
in miki sunayen Allah kyawawa?Na ce, eh,ta fara
kenan babanta ya fito, ya kallemu karatu kuke yi?
Na ce, eh, tana koya mun ne.Yayi dan murmushi
ya ce ummu jeki wajen umman ki, ki ce mata ta
jira ni ina zuwa.Ta na shiga daki ya ce, kanwata
zo mana.Na mike na bishi zuwa kofar gida,
nasake gaisheshi nayi , bayan mun tsaya ya
ce,Sadiya nasan ba zakiji mamakin kiran da nayi
maki ba ko?Na ce ba wani mamaki, kila zaka
aikeni ne.
Yyace bahakabane na kiraki ne dan in sanardake
wani abun alkairi, ko da yake ban san yanda zaki
amshi abun ba.Na gane zan cen ya Aliyu, ya
duba duk cikin matan da ke garin nan yaga babu
wadda tayi masa sai ke, tamkar bai san zancen
ba na furta da karfi so!!!Usman ya ce ba wani
abun mamaki bane, dami ne kika tsinta a kala.A
raina na ce lallai ma yaya usman din nan, to bari
in latsa shi.Na ce, ya Usman ka ce masa yayi
hakuri kawai dan na riga na tsaida mijin aure
wanda nike so.Ya Usman ya ce, kin kai shi gida
ne?Na ce, gobe ne iyayan sa zasu shigo gidan
mu.Usman ya ce, in har zan baki shawara ki
yarda zan so ki dakatar da su domin kowa zaki
aura na tabbata bai kai Aliyu ba, samunsa sai an
tona, ko na ce irinsa.In kika sameshi a matsayin
miji tabbas zakiyi alfahari samun muji kamarshi,
mata da yawa suna sonsa, kila sun fahimci
nagartarsa, amma ba matsi in baki sonshi zan
koma in fada masa cewa baki sonshi da aure.Na
kalleshi bance bana sonshi ba, saboda duk
abinda iya ta haifa dole ne in soshi, kai ko wani
ne can ba danta ba in dai ya mutunta ta to zan
soshi bare dan cikinta, na riga na zabi wani
ne.Usman yayi shiru, ya zaci da yayi mun
magana zan amsa da murna, can ya ce, to yanxu
mai zanje in ce masa?
Ku ziyarci blog dinmu domin karanta Littatafai
masu nishadantarwa Anamdorayi.mywapblog.com
Kokuma ku kasance taredamu a facebook
https://mbasic.facebook.com/HAUSA-
Novels-389304544597988/?e_pi=7%2CPAGE_
ID10%2C737012347
Na ce, ka fada masa zanyi tunani zuwa gobe. Ya
ce, shi kenan, zan kiraki amma kiyi shawara da
kawarki wadda ta sanshi, na san zata fada maki
qualitie din Aliyu. Na ce, ba damuwa. Ya ce, shi
kenan gobe zanzo naji. In kin shiga kicewa Abida
su fito mu tafi daman na sallami iya. Na ce, to.
Bayan tafiyar su iya tashiga yi mun fada wai ai
gashi nan saboda bai daukeni da muhimmanci ba
abokinsa ya turo min, ta san jikina yana bari na
ce na yarda. Na vata fuska tamkar zan saki kuka
na ce, ni fa iya banyi fa rawar jiki ba, ce masa
kawai nayi zanyi shawara zuwa gobe. Ta ce, ato
in kin kimanta kanki yaga darajarki in kuma kinki
ni dai na fada maki babu zuwa a kawo mun kara.
A waya Aliyu yaji duk yanda mukayi, mamaki ya
dinga yi wai wanan yarinyar ce zata ce sai tayi
shawara, dawa zata yi? Kuma ita ce wa? Usman
ya ce ita ce mace. Aliyu ya ce, shi yasa kaga ba
zan iya kai kaina ba ga wata ya in ce ina son ta
ba, bare tayi mun yauki, nidan oya-oya ne.
Usman ya ce ka barni da itakawai na san jan
ajine zamuyi nasara cikin jin haushi Aliyu ya ce,
in taki ka kyaleta kawai, yarinya sai kace wata ta
gold sai ga ruwa nake yi a kanta. Ya ja tsaki nan
ya kashe wayar ba tare da ya sake jin mai
Usman zai ce ba. Kwana Aliyu yayi da zullumin
halin da zai tsinci kanshi, in yarinya taki
amincewa da shi. Da safe ina shara ya fito daga
dakinsa ban san me ke sani faduwar gaba a duk
lokacin da na ganshi ba.Na gaida shi ya amsa
cikin isa, kuma a ta kaice kamar yanda ya saba.
Sanan bai ko kalleni ba sai dai nice na bishi da
kallo. Namiji ne sosai ko tafiyarshi ta shaida
haka, daga ganinshi baka ga rago ba, dama abin
da ya dace dashi kenan jami’in dan sanda. Iya
daga daki ashe tana kallona ta ce, in kin gama
kallonshi sai ki ci gaba da sharar ko? Cikin kunya
da shauki na ci gaba da sharata. Da rana naje
gidansu Aisha kawata nake bata labari duk yanda
muke ciki, tace, tabbas! Sadiya idan zan fada
maki gaskiya ki amince kawai, kada ma ki tsaya
wani jan aji,sau nawa nake fada maki Aliyunku
unique ne?Allah in kika yi sake kin tsaya yauki
kya zo kina na dama, kin san shi da zuciya ya ce
yafasa.Kash!Ina ma nice ya ce yana so?Jin haka
yasa na kagu dare yayi.Har na debe tsammanin
xuwansa dan tara ta kusa, duk na tsure kar dai
ya Aliyu ya hakura da gaske.Can sai na tsinkayi
muryar wani yaro yana sallama ni ina cikin daki a
kwance kan kujera.Iya ce ta amsa salamar don
tana tsakar gidan, ya ce an ce sadiya ta zo inji
wani a waje.Ka fin ya rufe baki na mike, zaraf na
suri mayafi na fita.Iya ta ce, kai jama’a!Kai
jama’a!!Ni wanan yarinya ko dai zaki kai kanki
ne?Na ce ban fa san ko wane ne ba, ma ai
iya.Cikin gatse iya ta ce, ina zaki sani, shiyasa
kike ta sintiri tun daxu kin kosa ko wanene maya
zo?Na ce, sai na dawo.Ta ce, kada ma ki dawo ki
kwana can.Usman yana tseye a gurin da muka
tsaya jiya, na sameshi da sallama, muka gaisa ya
ce to kanwata nazo jin me kika yanke?Na danyi
shiru kamar mai nazari, ya ce, kada ki damu in
har baki sonshi ya ce babu komai.Na ce, ai ba
zan iya cewa bana sonshi ba ko dan iya, don
haka ka ce masa na amince.Usman ya ce,
Alhamdulillah, sai kin ji mu.Ranar nayi farinciki
har nafila nayi don godiya ga Allah, iya ta ce yau
kuma ibadar ce ta motsa har da nafilar dare?Ni
dai ban tanka mata ba, ta ci gaba, Allah ya sa a
dore, ina ta samun gadanga ce akayina san daga
yau shi kenan.
Ku ziyarci blog dinmu domin karanta Littatafai
masu nishadantarwa Anamdorayi.mywapblog.com
Kokuma ku kasance taredamu a facebook
https://mbasic.facebook.com/HAUSA-
Novels-389304544597988/?e_pi=7%2CPAGE_
ID10%2C737012347
Washe gari yaje ya samu yaya zakari da yaya
Sulaiman yayi musu bayani, su kuma suka sami
dan uwan mahaifinsu dake nan layin kasuwa, a
nan unguwar mu’azu.Nan dai suka sa ranar zuwa
zariya gurin mahaifina don jin zance, Aliyu da
zasu tafi ya bada dubu hamsin ya ce har sadaki
duk yanda ta kaya shi kenan.Mahaifina yayi
murna har yana cewa wannan abu ai da ba sai
anxo ba, ita iya Sadiya tata ce, Aliyu ma nata ne,
da ba shi kenan ba sai dai muzo a yan
gayyata.Kawu ya ce, a a kun wuce haka, kuma
dole abaku hakkinku.Baba yayi ta godiya kafin
daga bisani ya ce bari ya kira dan uwansa.Sun
yanke sadaki dubu talatin sanan aka basu na
gaisuwa goma, sai dai suna dawowa suka fadawa
iya duk yanda akayi.Iya ta ce sam yarta tafi
talatin, su kawo goman nan hamsin ne sadakin
yarta, sanan gadanga ya ciko goma kudin
gaisuwa.Da kyar suka shawo kanta ta amshi
goman, sadaki arba’in kenan.Aliyu dai yana
zaune yana jin su yana kallonsu amma bai ce ko
mai ba.Suka ce an tsaida rana watan tara sha
biyar da shi, lokacin kuma ana watan shida.Aliyu
ya ce yaya Sulaiman lokacin nan bai yi tsawo ba
kuwa?Anawa ra’ayin nafi son wata biyu, iya ta ce,
har ka gama shiri ne zaka ce wata uku yayi maka
kadan?Aliyu ya ce, wane shiri ne mai zafi?Ba lefe
bane ko meye ne kuke cewa ya rage ba?Ta ce,
kana da gurin zama kenan ko nan zaka gyara mu
zauna?Ya ce, a haba dai, zan nemi gurin zama
duk a cikin wanan lokacin.Ta kalli Sulaiman ni fa
in nayi auran nan zataci gaba da karatunta ku
shaida wanan, in ya ce a a za a jimu.Aliyu ya ce,
na sani iya, nima ina son ta ci gaba da
karatun.Ta ce, to batun aure a barshi wata ukun,
sai kaga lokacin ya zama ba ka kammala da wani
abun ba har kake raina lokacin.Ya ce Allah ya
kaimu.Ina zaune cikin ajinmu bayan mun gama
zana paper din mu ta karshe, ina kallon yanda
yaran ajinmu suke ta jin dadi da murna tun da
muka baro hall din.Ta gumi na zabga ina
mamakin irin halin ya Aliyu, yau kusan sati hudu
da sa muna rana amma ko sau daya bai taba
kirana ba, haka nan kuma ko cikin gida ya shigo
ban isheshi kallo ba.Nima fa yanxu na soma
sarewa, anya kuwa mutumin nan yana sona?
Kullum iya sai tayi min gori, yau kam zanje in
nemi ya Usman.Bayan nan na cewa Anty Abida in
yadawo tace ya zo, ina son magana da shi, ta ce
to zata fada masa na ce ina su Ummulkhairi?Ta
ce suna makaranta.Da daddare kuwa sai gashi
ana sallama dani, na mike har ina tum tube.Iya
ta ce, sai karaftu kike sai kace a dakin Ajantina,
na san dai ba wanda kike son gani bane, dan
nasan shi ya fi karfin ya kiraki.
Ku ziyarci blog dinmu domin karanta Littatafai
masu nishadantarwa Anamdorayi.mywapblog.com
Kokuma ku kasance taredamu a facebook
https://mbasic.facebook.com/HAUSA-
Novels-389304544597988/?e_pi=7%2CPAGE_
ID10%2C737012347
Nace, iya to ai ina so ne na ga ko wanene.Ta ce,
oho ke dai kika sani.Ina fita yaya Usman ne
kamar yanda nayi tsamani bayan mun gaisa ya
ce, Abida ta ce kin zo nema na.Na ce, eh.Na
sunkuyar da kaina ina wasa da yatsuna, na ce
dama nazo ne a kan maganar mu ne da ya Aliyu,
in abin ba zai yuwu ba gara mu hakura tun
yanzu.Ya gyara tsayuwa wani abu ne ya faru?Na
ce to ya Usman a haka ne za mu fahimci juna in
san abinda baya so yasan abinda bana so?Na ci
ga ba, bai taba kirana da sunan muyi zance dashi
ba, ko gida ya shigo ban ko isheshi kallo ba, shi
bashi da wani lokaci ne sai na aikin shi?Usman
yace ba wai zan goyi bayan shi bane amma
ninasan kina ranshi,ki fahimce shi, shi mutum ne
mai kishin kasarsa da aikin sa, shi yasa baya
samun lokacin kansa.Amma da zarar kin zama a
gidansa na san dole ya baki dukan lokacinki.Nayi
shiru kamar maganar ta shigeni, ammada na
tuna ko kallo na bayayi na ce, yaya Usman ka
san Allah ba dan aikin shi bane, ko kallo fa ban
isheshi ba.Usman ya ce, to bari zanyi mashi
magana.Na ce, don Allah kada ka ce nayi maka
magana, kada yayi tsammanin na damu da shi
ne.Usman ya ce, zanyi masa maga na da ma ai,
ba zan ce kece kika sani ba.Kusan sha dayan
dare Usman ya daga wayar Aliyu tare da yin
sallama, bayan sun gaisa Usman ya ce aboki
dazun ina ta kira baka daga ba.Aliyu ya ce, bari
kawai aboki, lokacin ina tsakiyar wani case ne
abin nan yana matukar daga hankalina tare da
bani mamaki.Ka san wani mutum dan kimanin
shekara arba’in aka kama yayi wa yar shekara
hudu fyade.Usman ya zabga salati tare da cewa,
wai aboki wanan wace irin masifa ce?Ko dai wani
tsafi ne?Aliyu ya ce, wa ya sani?Wannan fyaden
na kananan yara yayi yawa.Kullum sai mun sami
wanan case din wlh yanda abin nan ke mun zafi
a raina zan iya kashe irin wadannan mutanen,
don mugaye ne.Idan mata ne su je mana ga
karuwai nan,Usman ya ce, to Allah ya shirye su,
ya tsare mana daukacin musulmi.Aliyu ya ce,
amin aboki to kaji halin da nake ciki, lokacin da
ka kirani lafiya lau dai ko?Lafiya lau dama zance
ne ya kamata mu shirya muje muyi hira da
yarinyar nan ko?Aliyu ya ce, wace yarinya ke
nan?Usman ya ce, sai karinka yi kamar baka san
da zancen ba bayan nasan tana ranka.Aliyu ya
ce, tsakani da Allah sai ka tuna min.Usman ya ce,
ok, tunda yanxu iya ta yarda dole ka manta.Aliyu
ya ce subuhanalla? Dama wai Sadiya kake
magana?To wacce hira kuma zamuyi tun da na
rigaya an gama magana, sai jiran lokaci.Usman ya
ce, ai duk da haka za aje ayi hira ta san abinda
baka so don a samu zaman lafiya.Aliyu yayi yar
dariya.To ni ba haka tsarina ya ke ba, ina zaton
in har zanje gurin budurwa zan jene don ina
tallata kaina in in samu shiga,tonina riga na
samu shiga babu dalilin da zan matsawa
kaina.Usman ya ja tsaki kai dai bahago ne wlh, to
sai ka sai mata waya ko ta waya kunyi
magana.Aliyu ya ce, to yan zu dai kaine sarkin
yakinta ko?Suka sa dariya.Usman ya ce, da gaske
nikeyi, akwai wata waya da ake saidawa mai kyau
nan kusa daoffice din mu (MTN OFFICE) ya ke
aiki.Aliyu ya ce, ka suyo mata in kazo sai na baka
kudin, sanan kai zaka bata don har karshen satin
nan ban san lokacin dawowata, kafin ita ta tashi
na fita.Usman ya ce shi kenan.Washegari da
daddare ya usman yazo ya kawo mun waya wai
iji yaya Aliyu, inyi hakuriza mu rinka waya aikine
yayi masa yawa.Bani da zabi dole na hakura
tunda ga waya har da layin (MTN) ko da na nuwa
wa iya baki ta tabe sanan ta ce Allah ya sa
alheri.Tun da na karbi wayar ko flashing ba a
taba yi mun ba, ga dai lambarshi a ciki ya usman
ya samun duk da cewa har da kudi a layin nawa
nima cewa nayi ba zan kira shi ba.Sai dai in ta
kiran kawaye da yan uwa wadanda nake da
number su.
Ku ziyarci blog dinmu domin karanta Littatafai
masu nishadantarwa Anamdorayi.mywapblog.com
Kokuma ku kasance taredamu a facebook
https://mbasic.facebook.com/HAUSA-
Novels-389304544597988/?e_pi=7%2CPAGE_
ID10%2C737012347
Wata rana da dadare naji Iya tana yi masa fada
cewa yana zaton haka za ayi auren ba lefe, biki
saura wata daya da kwanaki, amma ba a ga yana
motsi ba.Ya ce, abin ne ya shige masa, amma
gobe zai je ya sami matar ya sulaiman.Ita da
matar Usman Anty Abida sukai ta zaryar zuwa
kasuwa, saura sati biyu lefe ya kammala da dinki
da komai.Iya ta ce ya Aliyu ya bada kudin mota a
kaisu zariya, ni kuma nan kawaye na sun matsa
da batun anko, lokaci yana tafiya gashi ba zan iya
yi mashi magana ba.Aisha ta ce, kiyi wa iya
magana.Na ce, iya kwana biyu bata sana’a , bata
da kudin anko?Tab! Ba zai yuwu ba.Wayata na
dauka inyi kamar zan kira shi in fasa, Aisha ta
amsa na ce kada ki kira shi dan bai taba kira na
ba, ba wani kiranshi da nima zanyi Allah aisha ni
auren nan tuni ya fitan min daga rai.Ace kai kafi
karfin kazo sai dai abokinka?Aisha ta ce, Allah sai
na rubuta masa tex.Ina kallonta ta rubuta
masa.SALAM.INA FATAN KANA LAFIYA?KAYI
HAKURI KILA YANXU KANA CIKIN AIKI NA TSAIDA
KA, DA MA NAYI MAKA WANAN MESSAGE DIN NE
DON NA TAMBAYEKA A KAN MAGANAR ANKO,
DONKAWAYENA SUN DAMU SABODA LOKACI YANA
KAREWA.NA GODE, KA HUTA LAFIYA.Tana gama
rubutawa ta tura masa, maji amsa-maji amsa
shiru, nace kin gani ko?Ke ayi biki haka bani kara
masa batun anko.Aisha ta ce, niko yanda yake
nashi salon birge ni yake, na ce, au!Wulakancin
da yake min din ne yake burgeki?Tayi dariya, ai
ba wulakanci bane rayuwar sa ce haka.
Lokacin yana office din commissiner ya je a kan
nemansa da yayi tsam ya kame kamar yanda
yake al’adar yan sanda, sanan ya soma magana
cikin natsuwa ranka ya dade an ce kana nema
na.Commissioner ya dube shi cikin natsuwa
sanan ya ce da ma na kira ka ne a kan maganar
barawon shanu din nan da aka ce kaki yarda a
bada belinshi.Aliyu ya sunkuyar da kai don
girmamawa, yace ranka ya dade haka ne, naki
bada belinshine saboda bincike ya nuna shi din
ba karamin mai laifi bane.Daji suke shiga da
motoci suna kora shanayen fulani suna kwashewa
su kai kudu su saida, wanan kamawar ita ce ta
goma sha uku amma ba a taba mikashi kotu ba,
azzalumine na gaske,Commisioner yayi dan
murmushi sannan yazo ya dafa kafadar Aliyu ya
bubbuga alamun jinjina, san nan ya ce, Dan
Sanda mai kishi, lallai kasan aikin ka da ka tsaya
binciko wannan files din, ka tattarosu ka miko
min nan, ni nasan yanda zan kawo karshen
lamarinsa.Zan shigo gurinku anjima kaje.Aliyu ya
sara masa, sanan ya fito.Gaskiya in son samu ne
case din nan ya tsaya a hannunsa dan kam zaiyi
gogaiya da zalunci.Shigarshi office din sa kenan
sako ya shigo wayarsa, sai da ya zauna sanan ya
duba.Murmushi yayi bayan ya karanta, a fili
kumaya ce, ko me nene anko?(hahaha,kunjifa
dan rainin hankali inji,shin kuna ganin zai yuwu
ace baisan Ankoba,ai dai kayan yansanama
Ankone,kuma kala biyu, wasu su sa baki
kawai,wasu kuma baki da light blue ko? Cewar
ANaM Dorayi)
Ya kira layin Usman bayan sun gaisa ya tambaye
shi ko menene Anko? Usman yayi murmushi wato
kai dai in kaje ka shige caji ofis dinku shi ke nan
baka tuna meye a cikin garin.Aliyu ya ce, aboki
mu kuwa dake wanan ofishin mu muke da
labarin abunda ke cikin garin, amma ba wanda
ya shafi biki ba.Usman ya ce zaka bata kudi ne
kurum ta shiga kasuwa da kawayenta su zabo,
haka su ke yi.Aliyu ya ce, gashi ni kuma bana son
yawo bare kuma xuwa kasuwa, in dai zani ne in
zan je gidan zan tsaya nan wani super market in
sayan masu, guda nawa ake siya?Usman ya ce,
da ka basu kudin.Aliyu ya ce, ba zata kasuwa ba,
wanan shine ra’ayi na, zan siyo musu zani.Usman
ya ce shi kenan, sai ka suyo musu mai kyau.Aliyu
ya ce ina ruwa na da zabe, ni dai kawai in dau
zani.Don haushi Usman ko sallama babu ya
kashe wayar.Aliyu ko da wuri ya bar office din ya
bi ta kasuwa ya sai zaunnuwa kala uku ko
wanneguda bibbiyu ya nufi gida.Iya tana zaune
tana yankan kubewa ni kuma ina daga kicin ina
kwashe tuwo ina mulmulawa a leda ina sakawa a
kula ya Aliyu ya shigo da sallama.
Kusan kwana hudu ban sashi a ido na ba , da ya
zauna yana gaisheta.Ta amsa ya ce, ga zaunnuwa
anko ne suka ce ko menene ma?Ta dauki ledar
tana cirowa ta re da fadin kaine ka siyo ankon
gadanda da kanka?Ya ce, to duk ba zani bane,
shi nan sai su zaba.Ina kallo daga ciki kuma ina
jin su, tun kafin in fito zaunuwan suka tafi
dani.Ya ce, naki ne da nata.Iya ta ce, to mun
gode, da ma ina so inyi maka zancen gidan ne, a
ina kasamu?Ya ce, to ni dai nafi so a can kasan
layinku, gefen makabarta din nan, to ba a samu
ba sai na dawo neman na siyarwa, kudina
dakekasa yanxu za su iya semin gida, amma
albashin wanan watan da na wancan watan hada
mana za ayi.To ganin kurewar lokacin sai kurum
na barshi yanxun anjima zamuje mu ga wani gida
da yaya Sani da Usman wai ciki da falo sai kichin
da ban daki dubu dari da hamsin.Iya tayi shiru
tana nazari, can ta ce ina nufin kasan gidan su
babba ne?Ya ce ciki uku ne da kicin da ban daki
sanan ga filin da mutum zai iya fakin din mota
har biyu.Iya ta ce kuma nawa?Da sauri ya ce wai
miliyan daya da dari takwas.Ta ce, ina ganin zaifi
ka siya gidan in yaso sai a daga bikin.Ya dubi iya,
ai saboda bana son dagawar shiyasa na hakura
da siyan gidan.Iya ta ce siyan xai fi maka sauki
ka huta da biyan haya, auran kurum za a daga
ba.Ya ce ba dagawa za’ayi ba, abinda ya sa in an
daga za ayi asara da yawa.Abokaina sun kashe
kudi gurin kati mai tsada tare da wasu abubuwan
abokan aikina suma sun kashe kudi gurin shirya
bukin.Iya ta ce to, kana ji ko, yanda za ayi kawai
a daura auren da buki, sai ta zauna gida kafin a
gama gyara tunda dai nan a gida ne ba a dawa
ba, bana so ka rasa gidan nan ne muhalli a bariki
ba karamin rufin asari bane
Aliyu ya ce, shi ke nan sai ayi haka din bari zan
kira yaya Sani sai muje dake ki ga gidan sai a
biya.Lumshe ido nayi cikin jin dadin an fasa daga
bikin, kai naso in tare a gida na ranar amma baji,
buri na dai a daura auren, amma da iya ta so
kwafsawa wai a daga.Ya mike ya juya da nufin
fita ida nunsa sukasauka a kichin a inda nake, da
sauri na ce ina yini?Sai da ya dauke kai sanan ya
ce, lafiya.Har ya fita ina kallonshi.Iya ta katse ni
da cewa, wata rana sai kin gaji da kallon shi.Na
sunkuyar da kai kunya ta rufe ni, ban santana
kallona ba sa karya, in dai gadanga ne gaki ga shi
nan.
Pink din muka zaba ni da Aisha, sai dai muna
zuwa kasuwa aka ce dubu uku ce gashi kudin
aisha bai kai ba.Sai muka dawo gida da kyar
mamanta ta cika mata muka koma muka
siyo.Muka roki mai shagon ya ajiye mana da mu
siya da yawa.Yamma tai mana a kasuwa gashi
ana wahalar mota.Muna tsaye a kan titin kano
Road, na ce bana son magariba tayi mana tun
daya muka fito gashi iya ba ta san mun koma
unguwar mu’azu mun dawo kasuwa ba.Aisha ta
ce, sai dai muje mushiga dambancen ko za mu
samu, na ce zamuje.Ta kan legas street wani
lokacin ba a wahalar mota.Muna tafe wai wani
mai mota ya tsaya, ‘yan mata kuzo mana.Na ja
tsaki tare da kara sauri, Aisha ta ce, lafiya?Ya ce
rage muku hanya zanyi.Na ce Aisha, kema kika
tsaya tambayarshi.Haka mutumin nan ya ci gaba
da bin mu yana magiya, duhun magariba ya
shigo na ce Aisha ko dai mu tsayar da mutumin
nan ya kai mu gida?Don ina tsoron fadan iya.
Ku ziyarci blog dinmu domin karanta Littatafai
masu nishadantarwa Anamdorayi.mywapblog.com
Kokuma ku kasance taredamu a facebook
https://mbasic.facebook.com/HAUSA-
Novels-389304544597988/?e_pi=7%2CPAGE_
ID10%2C737012347
Tace, nima hakan zan ce,dai dai lokacin ya sake
cewa ku kuwa tunda na ce Allah ya kamata ku
saurare ni, dan kun san mugu dai ba zai yi muku
sallama ba.Aisha ta ce unguwar Mu’axu muke.Ya
ce, ai hanya ta ce ni kuma Nasarawa zanje.Cikin
far gaba muka shiga motar ya ce mun a’a ke
dawo gaba dai ki nuna mun hanya , na koma ga
ba.Ya tam bayi sunayen mu, ina shirin xollo masa
karya sai naji Aisha daga bayana ta ce, ita Sadiya
ni kuma Aisha .Ya ce, masha Allah , sunaye masu
ma’ana.Ya dube ni, Sadiya dan ke fa nake ta
wanan bibikon sai aka ci sa’a kina da sunan
matata, ni sunana Auwal.Hakika jin sunanki ya
kara samun sonki Halimatu duk wace ta amsa
wanan sunan takan zama mai hakuri da hange,
bata rani bata daukar raini, macen rufin asiri zan
so na sake samun ki.Na ce matar taka ta hada
duk wanan halin shine zaka yi mata kishiya?Ya ce
jin dadin halinta yasa zan kara.Aisha ta ce bakai
mata adalci ba, au, ke fa sunan uwata ne ke da
zaki tayani yakin neman shiga?Aisha ta ce, nan da
sati biyu ita ma tana dakin angonta.Da sauri ya
ce, da gaske?Ta rantse mashi tare da fada mashi
ashobe muka zo siya.Daga nan nayi shiru bai
sake magana ba harya shigar damu layin kasuwa,
na ce sauke mu a nan ma mun gode.Sai mu
karasa.Ya tsaya muka fito, ya ce marya ba
godiya?Na dawo dai dai saitin shi na ce, mun
gode, na ce kayi hakuri muna sauri ne dare
yayi.Ya ce shi kenan, Allah ya baki zaman
lafiya.Juyawar da zanyi in tafi tare da cewa amin,
sai maganar ta tsaya, sa kamakon ya Aliyu da
nagani tsaye yana kallon mu.
Ku ziyarci blog dinmu domin karanta Littatafai
masu nishadantarwa Anamdorayi.mywapblog.com
Kokuma ku kasance taredamu a facebook
https://mbasic.facebook.com/HAUSA-
Novels-389304544597988/?e_pi=7%2CPAGE_
ID10%2C737012347

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9Next page

Leave a Reply

Back to top button