HALIN GIRMA COMPLETE HAUSA NOVEL

HALIN GIRMA 31-35

Yace ya sa kai ya fice da bishi da kallon mamaki, bata taba
tunanin zai yarda haka kai tsaye ba, murna ta hau yi ta dinga zagaye dakin tana
jin kamar wahalar ta, ta kare kenan dan ko giyar wake take sha idan taje gida
ba zata dawo ba sai dai Abba ya kashe ta.

  Murmushin mugunta yayi yana barin dakin, shi kadai yasan
tsiyar da ya shirya ya kuma tabbatar da ko taje gidan toh sai ta dawo da kanta
ko Maman ta sakota gaba ta dawo da ita.

 

***Waya suka gama yi da Ya Maryam ta cigaba da shiryawa a
tsanake saboda safiya ce, sannan yace ta jira shi ya fita toh dole sai ya dawo
zata tafi, tana so taga Abban ta da Marwan da Gaji da sauran yan gidan, shiyasa
ta tashi tun wuri ta hau shiryawa yadda zata samu zuwa da wuri ta dade kuma.

   Tana zaune taji shigowar motocin sa, ta yaye
curtains din dakin ta ga wasu motoci guda biyu da bata san su a gidan ba, sakin
labulen tayi, ta sake fesa turare ta fito suka hadu a falo.

   Tafi ya shiga yi mata dan ba karamin kyau tayi
ba, lace ta saka me orange da black yayi mata kyau ya dace da kalar ta, zaunar
da ita yayi ya dauke ta hotuna masu kyau sannan yace idan ta gama ta ga driver
nan idan yaso zai zo da daddare su dawo tare. Jakar ta, ta dauko ya rakota har
wajen motar ya bud’e mata ta shiga, sannan suka fita daga gidan yana tsaye yana
kallon su. Tasa motar ya fad’a shima ya bar gidan dan yana da important abun da
zai yi. A daidai lokacin Zeenat suka fito da Bashir, ya kunna machine din da ya
aro a wajen abokin sa dan Hajiya ta fita da motar ta, kamar tace ba zata hau
ba, sai kuma ta hau dan bata da ko biyar din da zata dauki adaidata sahu,
tunanin idan taje gida ta karbo masa sam be zo kanta ba.

 

 

_ZAFAFA BIYAR 2022🔥_*

 

*_NANA HAFSAT(MISS XOXO) s_*

_SO DA ZUCIYA_

 

*_SAFIYYA HUGUMA_*

_DABI’AR ZUCIYA_

 

*_MAMUH GEE_*

_DEEN MARSHALL_

 

*_HAFSAT RANO_*

_HALIN GIRMA_

 

*_BILLYN ABDULL_*

_TAKUN SAKA_

 

*_Zaku biya kudin wainnan daddadan labaran Kamar haka_*👇👇

D’aya 300

Biyu 400

Uku 500

Hudu 700

Biyar 1k

 

*_Zaku tura kudin a_*

 

6019473875

*MUSAA ABDULLAHI SAFIYA*

*keystone bank*

 

*Sai shedar payment dinki a*👇👇👇

 

08184017082

 

*Kokuma katin waya na MTN anan*👇👇

 

09134848107

2/12/22, 11:31 – Buhainat: Halin Girma

      33

 

*_ZAFAFA BIYAR FACEBOOK LINK👇🏾_*

https://www.facebook.com/groups/494948898814888/?ref=share

 

*_ZAFAFA BIYAR INSTAGRAM LINK👇🏾_*

https://www.instagram.com/invites/contact/?i=u8e91axrluzc&utm_content=nj79azb

 

*_ZAFAFA BIYAR WATTPAD LINK👇🏾_*

https://www.wattpad.com/1178725798?utm_source=android&utm_medium=whatsapp&utm_content=share_published&wp_page=create_on_publish&wp_uname=ZAFAFABIYAR&wp_originator=Rf3bdM1DxoE6rtr%2FpmofDT2LwC%2FVfwSkcdyq99bn0JQs6Y4vrnr66bh9cxKlfOuPfF5VyLoSKGor57378NB4Zb%2FxLxcsULfA0VJvg4flaQvgAACdVin4LPGGN8XRDxBS

 

*_ZAFAFA BIYAR TELEGRAM LINK👇🏾_*

https://t.me/+SBu4brdnI29hSBfw

 

*******�

A kusan jere suke tafiya da motar Abba da Habib ke ciki shida
mama, kasancewar tint ce ya saka basu gane Iman din bace a ciki, suna shigowa
layin su Habib ya sake kallon motar yace

 

“Ina tunanin fa Iman ce a motar nan.”

 

“Wacce motar? ” Mama tace tana waigawa, gabanta ne ya
fadi ganin dalleliyar mota a bayan su,

 

” Ta ya akayi ka sani?”

 

” Number na duba. “

 

Ya amsa mata yana tsayawa a daidai kofar gidan, daidai lokacin
motar Iman din itama ta tsaya, yayi daidai da isowar Zeenat a saman machine din
Bashir. Mutuwar zaune Mama tayi ta kasa bud’e murfin motar balle ta fito, idon
ta yana kan motar da ta gama gane wacece a ciki, ta saitin ta Bashir ya zagayo
bayan ya faka machine din, ya leko yana cewa

 

” Sannu da zuwa Mama. “

 

Wani abu taji, ta kalle shi a kaikace kamar ta falla masa mari,
tayi dauriya ta danne zuciyar ta ta amsa tana jan kofar ganin yana kokarin
bud’e mata, matsa wa yayi ta fito idon ta akan Zeenat da tayi wani irin haske,
hasken da tana kallon ta, ta gane na menene, kamar wadda aka sage wa guiwa haka
ya shiga jan kafarta zuwa cikin gidan, suka rufa mata baya a jere Iman din na
magana da Zeenat da take ta kokarin maida hawayen da take jin zasu zubo mata
wanda bata san dalilin su ba

 

“Ashe zaki zo?” Tace a sanyaye

 

“Wallahi, ya gida? Ko waya bamuyi ba.”

 

“Wayata ta lalace ne. “

 

” Ayya.” Kawai tace suka karasa ciki, nan da nan
mutanen dake harabar gidan sukayi kan Iman, kowa so yake ya ganta, duk sun rude
babu wanda yabi ta kan Zeenat, ganin haka yasa ta sulale ta gudu bangaren su,
ta samu Mama a zaune tana kuka wiwi, kukan bakin ciki, kukan dana sani da aka
ce keya ce wadda bata da amfani, ta tuna watarana da aka zo akayi sallama da
Iman, ranar ce ta farko da aka fara zuwa kuma wajen Iman din, tun basu kai
yanzu ba, da kanta ta saka Hijab ta koreshi irin korar wulakanci, ba tare da
kowa ya sani ba sai Habib, wanda bayan ta kore shi ne Habib yake gaya mata waye
shi, da kuma gidan da ya fito,. Tun daga lokacin ta dauki alwashin dakushe Iman
din, ta kara maida ita mara yanci cikin rashin sanin cewa gata tayi mata, babu
in da zata shiga rayuwa ta bata wahala musaman irin abubuwan da suka shafi kula
da gida.

   Taba ta Zeenat tayi ganin sai sallama take amma
bata amsa ba, firgigit tayi tana dawowa tunanin ta, suka rungume juna Zeenat
din ta fashe da kuka, bata hanata ba, sai da tayi me isar ta dan tasan kukan
zai rage mata abinda take ji, gwara ace kishiyar uwa ke gallaza maka akan ace
kishiyar ka ce zata hanaka sakat da sukuni, abinda tayi ne ya juyo kanta amma
ta siga ta daban, sigar da bata taba tunani ko tsammani ba.

  Yan uwan Abba ne suka biyo Zeenat din har cikin gidan
nasu, da mitar me ya faru zata shigo ta wuce su babu ko gaisuwa, Mama na jinsu
bata ce komai ba, dan tasan da biyu suka zo maganar, tana jin Zeenat din tace
suyi hakuri, wanda ya saka su jin nauyi da kunya kuma, suka tafi cike da borin
kunya.

  Suna fita Iman ta shigo, ta russuna har k’asa ta gaida
Mama kamar yadda ta saba, ko ba komai ita a uwa take kallon ta, dan itace tayi
mata komai na mahaifiya idan aka cire shekarun haihiwa zuwa yaye, ita ta sani,
ko ma menene dai tayi mata wani abu.

  A chunkushe ta amsa, har yanzu akwai haushin Iman din a
zuciyar ta, wanda bata jin zata daina sai ko ranar da ta bar duniya, har gobe
tana kallon Iman din ta tuna cin amanar da akayi mata, wanda take ganin da
gaske Itace baa kyautawa ba.

   Ta dan zauna a bangaren nasu, babu me magana a
cikin su, sai jefi jefi da suke magana tsakanin ta da Zeenat wadda take cike da
mamakin sauyawarta, tayi sanyi sosai kamar ba ita ba, ta kuma hangi wani abu a
idon ta, da take da yakinin damuwa ce. Tashi Mama tayi ta barsu a falon tayi
shigewarta daki, domin ta samu damar yin tunanin abinda ya kamata tayi akan
auran Zeenat din.

   Bin ta Zeenat tayi, ganin haka ya saka Iman
ficewa ta koma bangaren Gaji in da anan me jegon take, ta shiga yan uwa aka
cigaba da kuranta ta da yaba ta, kowa yana so ya samu ya kafa kansa ganin cewa
yanzu ta wuce duk wani matsayi ta kai in da basu taba tunani ba, shiyasa kowa
yake kokarin chusa kansa dan idan wata dama ta taso ko da ta aikin Hajji ne,
toh Iman din zata tuna da mutum.

   Wajen azahar sai ga Yaya Maryam tazo, sai da ta
biya ta asibitin da take ANC sannan ta tawo shine dalilin rashin zuwan nata da
wuri. Jan Iman tayi suka koma gidan su, suka zauna su isu matasa aka hau hirar
aure da yadda rayuwar auren take ma baki daya, sosai Iman take daukar haske,
tana karuwa da wasu abubuwan tunda sun fita jimawa, bata saka musu baki ba, a
tunanin Yaya Maryam ma bata jin su, nan kuwa ta haddace komai akanta.

  

 

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10Next page

Related Articles

Leave a Reply

Back to top button