ALIYU GADANGA 1-END

ALIYU GADANGA Page 31 to 40

   Suna Fita ya karisa gareta lokaci daya yana harde hannuwansa bisa kirjinsa kallonta yake dakyau yadda Fuskarta tayi Fayau tabashi Sha”awa,Sunanta yakira ahankali..”Pretty…” Tana jinsa tayi mishi banza harda dan nishinta alamar barci takeyi,yana kallonta yar dariya ta kamashi,sai ya saka hannu ya dan,matse hannun Da aka sanyamata Drip,taji zafi da hanzari tajaye hannunta tana Fadin”Wash..”tafada tana Jaye hannunta bata bude ido ba,ta mirgudamai baki,dariya ta kamashi sai ya Rankwafa yana lakucemata hanci yake Fadin”Matar Sunnah bata Fushi da mijinta,kuma in yayimata laifi yakamata ta Sausautamai,koyasamu damar bada hakuri..”,tana jinsa tayi mishi banza,sai ma juyamai baya datayi,Kai ya dafe yana Saka hannu abaki,kafin ya Sauke ajiyar zuciya yace”Shikenan ki Adanamin duka Fushinki pretty har na dawo,nayi alqawarin daukan kowani mataki kika Dauka akaina,ammh i want to u to know one Thing i relly miss u so much,and kinbiyani Tunda kikayi Saurin Cafkan sako na,Adaren Farkomu,Allah ya saukeki lafiya..”Yafada kafin ya duka ya bata kissa Ahannunta,ya saka kai Yafice yana mai jin Farinciki,Sai da ta tabbarta da yafita kana ta bude ido tana Dafe kirji tace”Ina da cikin yaya captain yanzu a wannan cikin? tafada Tana dafa cikinta lokaci daya tana Sakin mirmishin Farinciki,hawaye suna zubomata ta sanya hannu ta Share Tana fadin”,Allah na godemaka..Ni nan da wata Tara nazama mama”Tafada kafin ta saka dariya ita kadai,shafa cikin take tana mirmishi ita kadai,kafin chan kuma ta Tura baki tana fadin”Ina Sonka,ammh ina Fushi da babanka,duk da kewarsa da Soyyyarsa bazata taba barina Fushina yayi Tasiri Akanshi,Alhamdulillah Allah nagodema..”take Fada tana mirmishi ita kadai.

Shiko Aliyu achan waje,har kasa ya dukama goggo kafin ma yayi mgana tayi Saurin dagoshi tana fadin”Tashi gadanga,Har Abada goggon gadanga bazata yi Fushi dakai ba,konayi baya zuwa ko”ina na yafema Tunranar da naje mkrantansu Azeema Shugaban mkrantar ke Fadamin kagama biyanmta komai,Tun wajen nace na yafema nayita sakamaka albarka,duk da dai Ja”irin ka batamin Rai ammh kadan..”Tafada tana mangaremai kai,dariya yayi kafin ya Fada jikinta ya Rumgumeta yana Fadin”Nayi kewarki goggo..”Kunnensa ta murda tana Fadin”Karya kayi dai kewar matarka ko? ammh bani ba..”Dagowa yayi yana kallonta Kafin ya Shagwabe yana Fadin”Ni Allah goggona nayi kewa..”Dariya tana fadin”Toh naji Nima nayi kewar gadanga ko Tsiyar damuke ankwana biyu ba”a hadu ba..”,Dariya suka saka gabadaya kafin Gadanga yace”Goggo zamu koma bakin aiki..”Jinjina kai Goggo tayi kafin tace”Basai kamin bayani ba,yanzu Jabir yagamamin bayanin komai Kuje Allah ya Tsare yakuma bada Sa”a Azeema kuma zan kular maka da ita har kadawo nayi alqawari..”Da Ameen suka amsata mata kafin Suyi mata sallama Su Tafi,daganan Asibitin hanyar gombe suka dauka,dama tawagar da sukazo Tare Tun Sadda zasu kai Azeema Asibiti suka basu Umarnin juyawa gombe,toh Tuni sun damki hanya kilama Sun isa Tundazu.

  Koda goggo takoma wajen Azeema tayi barci lokaci,tatasata tayi tana ta zuba godiya Ga Allah,har saida Tafitar da kwallah,Allah sarki Gadanga,shifa Tunda yatashi baisan dadin wani Dan”uwa ba,sai Hisham,wanda kusan yanayin aikin banki da Tsanani da Takura gashi ba sakewa so basu cika haduwa ba,sai dai awaya,haduwarsa da Jabir yasa yasamu aboki sosai,gashi Allah ya ba matarsa Ciki tana Fatan cikin ya zamanto Silar Farincikin gadanga dasu gabadaya.

Kwanan Azeema daya aka sallamota ta dawo gida,bayan an kafamata dokan banda aiki mai yawa,ba daukan Abu mai nauyi,kuma anbata mgungunar Kara jini,dana saka cin abinci don goggo tace bataci,sai cika ciki da goriba,ba”a hanata cin kayan kwalamanta ba,ammh ance ta dinga cin Abinci sosai,tadai Samu ishasshen Hutu da Lokaci mai Tsawo,goggo ko duk taji bayanan likita Shiyasa suna komawa gida ta zage tayimata Tuwon Semo miyar Kubewa dayan,wacce aka daka kifi aciki,duk da bataci dayawa ba,ammh taci sosai,daddaren Mallam lawal ya Shigo duba Azeema yadade yana mata nasiha hakuri da rayuwa,tare da mata gargadin ta rike mijinta da Amana,nan yake Fadamusu Inna Ramatu tun jiya take kuka da Hajijiya tana Rokon don Allah asakomata Azeeza tatuba tabi Allah,yacema bayan Tafiyarsu saiga Baba Ade tazo,har yara Sun kaimata lbrin Abunda yafaru tazo da kukanta ni nayita bata baki,gyara zama goggo tayi tana fadin”Allah sarki ai tabar kuka,don ta kusa samun megida ko Amarya kai kuma Mallam ka Shiryafa jika na zuwa..”Washe baki yayi yana saka albarka yana kallon Azeema,itako Rufe Fuska tayi Duk kunya ya kamata,Mallam lawal yayi murna Sosai yayita Addu”ar Fatan Allah ya Raba lafiya.

__________________

_Kaduna_

  Yau kimanin kwana hudu kenan da zuwansu barikin baitaba yin nesa daga Sansaninsu ba,iyakarsa Dan haraban wajen,sai jiya kuma da Sukaje bayan bariki sukayi Atisayen Harbi,yau Tunda yatashi yakejin sha”awar zagaye barikin nan duka duk da baisan ko”ina ba yasan baya bata ba,cikin Kakinsu na chan ya Fito yafara Tafiya duk inda yabi yana Daukan Hoto ko video din wajen da Rantsatsiyar Wayarsa kirar Samsumg,Duk inda ya Shiga sai Binsa ake da kallo Abunda yabashi mamaki Wasu Sojojin jahar ta Nageria har kamemai Sukeyi Saboda Su bihakki da gaskiya Dauka Suke Captain Aliyu ne,duk da kuma da bambamcin Uniform din da Suka gani,Abun ya Daureshi mishi kai,sai yakoma daya Hadu dasu yaga sun Kamemai Sun Saramai,kawai sai ya Daukesu Selfe ya wuce yana dariya,suko suyi ta mamaki don Asaninsu Captain Aliyu baya dariya Sai dai mirmishi ko kaga yadan murmusa kumatu kadan.

Yana Tafe yabada baya yana Daukan wani lafiyayyan Titin daya Shararo,wajen ya burgeshi yadda kasan ba”a Nageria ba,kamar akasar Turai saboda Haduwansa gashi so quit,ga wasu Fulawoyi dasuka kawata wajen,sojojin dasuke wucewa kadan kadan ne,sakamakon Lokacin da Safe ne sosai ba’a Fito Training ba.

Jiyayi ya bangaji Mutum harsaida wayar dake hannun Wanda sukayi karo da Umar din,tafadi kasa da hanzari Umar ya sanya wayarsa a aljihu ya duka ya Tattaroma mutumin wayarsa wacce ta watse yana fadin”Am so Srry did know u are coming Srry…”,Yafada yana dagowa karaf ko suka hada ido da Jabir wanda ke Tsaye yana karemai kallo sama da kasa kafin ya zaro ido yana Rike baki yace”Kambu Dude,basaja kakoma kuma,yau Abun naka harda komawa Sojan Niger..”Yafada yana Dariya galala Umar yayi rike da waya yana kallonsa bakinsa na motsi yace”ni..Ni..Bansan meka ke mgana akai ba fa? Kafadansa Jabir ya daka da karfi yana fadin”Kai Dude dawo hayyacinka kasan dai ni bazakamin layan zana bako?any why yau fa kasan akwai Atisayen gudu ina kuma zaka naganga ta nan? Umar ya lumshe ido kafin ya bude,baiyi mgana ya Rike hannun Jabir ya damkamsa wayarsa yana fadin”Ba wanda Kake Tunani bane,Ni Sunana Leuitenant Umar Abdulnaseer Tambari buzu ina daga cikin bakin Sojojin da suka sauka Shekaranjiya..”Kuramsa ido Jabir yayi kafin ya warci wayarsa yana Fadin’Kajimin dan iska,Umar kuma kakoma? Toh in bakai bane waye,Nikaga Tafiyata mallam,dama kai baka Rabo da Maida mutane yan iska..”,Yana Fadin haka ya juya ya cigaba da Tafiya ko waigowa baiyi ba,Galala sake da baki Umar ke binsa da kallo kafin ya rike baki yana Gyada kai,mamaki yakamashi,ammh sai bai ba Mamakin matsungunni ba,juyawa yayi yakoma,ammh kuma Abunda yafaru ya tsayamai Aranshi.

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16Next page

Related Articles

Leave a Reply

Back to top button