BABU SO HAUSA NOVEL

ANEESA YAR PRESIDENT HAUSA NOVEL

Copied By
HAYATU BABA ZUBAIRU(YAYA HAYAT)
(ADMIN OF ADMINS)
(admin
Hayat hausa novels
Hausa novels and fashion
Cool novel, makeup and kitchen1⃣
Cool novel, makeup and kitchen2⃣
AND
Cool novel, makeup and kitchen3⃣)
WHATSAPP NO:
09030159301

????????‍⚖ANEESA YAR PRESIDENT????????‍⚖

  Na Hannatu Dada Kuta 

        20/10/2017

????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????

UMMU SAFWAN HAUSA NOVELS????

Dasunan Allah mai rahma mai jin kai Godiya ta tabbata ga Allah wanda yabani ikon farawa da kammala RAYUWAR LEEMAT kurakuranda keciki Allah yafe min darasinda keciki kuma Allah bamu ikon aiki dasu Ameen rayuwar leemat ya kasance 2rue lyf story ne Sai gashi yau Allah cikin ikonsa ya kara bani ikon fara wata sabuwar novel kuma mai suna
???????? Allah mana jagora Ameen

                    01

Motocine sunfi 10 a jere babu abinda kk ji sai kukan sarin weeee niko dasan kwasoma ✍???? masoyana lbrai nabisu abaya ????

Wani babban gate hadadde naga an bude ai kuwa nan motocin suka shige ciki bayan sunyi parking ne wasu securities ne suka zo wurin motar tsakiya suka bude kofar motan wato gidane nagani a fada tsarin gidan kawai ko hmmm .. ba a magana domin kuwa bata baki ne ga gidan babba gashi hadadde wacce tafito cikin motar aikuwa ina ganinta saida na…….

Wata yar budurwace fara kyakkyawa batada jiki kuma bazaka kirata da slim girl ba ga hancinnan zir kamar pencir ga bakin madaidaici komai nata cip cip kamar ita ta halicci b abin sai wanda yagani ANEESa kenan yarinyar albarka ga kyau ga ilmi ga hankali mashaa Allah

Jallabiyace ajikinta sai mayafin jallabiyar da tayi hijab dashi yayi mata kyau sosai wasu mata ne suka fito suka durkusa har kasa suna mata sannu da zuwa Aneesa ta amsa sannan tayi masu umurni dasu mike tsaye ba musu suka mike ai kuwa kafin takuma cewa uffan wasu yan mata ne suka fito dauke da wasu kwanoni kyau ga daukan ido flowers ne suka fara zubawa a kasa suna wakoki Aneesa tace kudai wai bakwa gajiya ne ?

Duk dawowana sai kunmin irin wannan tarba…. ai sai ji tayi popospoossss kamar ana fasa baloons kamar kuma knockout kunnuwanta tayi da hannayenta bibbiyu kana tace wai me haka ne Allah ni banason haka wai inasu mom ne da murmushi suka fito dauke da cake a hannun mom din murmushi itama Aneesar tasakar mom dinta sannan taje ta hura candle din da ke saman cake din da baki takuma sa knife ta yanka tabama mom dinta sannan itama taci

Mom dinta ta mikawa wata mata kusa da ita sannan ta rungumi Aneesa cikeda so da kauna a haka suka shiga har cikin palo Aneesa tace…… ban tsaya ta fada ba niko in baku lbr ganin dukiyarda ke cikin palon ne yasa na kasa cigaba da ✍???? domin kuwa hannuna har nauyi yamin

Love u all ????????❤????????
????????‍⚖ANEESA YAR PRESIDENT????????‍⚖

  Na Hannatu Dada Kuta

????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????

UMMU SAFWAN HAUSA NOVELS????

             02

Aneesa ta rusuna har kasa ta gaida mominta sannan tagaida kawayen mommy bayan sun zaina ne aneesa ta kalli momminta tace wai mom dan Allah bazaku daina wannan kashe2 kudinba?
Da wannan kashe kudinda kukayi dan tarbata wallahi mom da sadaka kukaje kukayimin da ita da yafimin kuma danafi jin dadi wallahi mom bazan gaji da fada maki hakan ba waishin mom kinkosan adadin mutanenda ke cikin damuwarda idan kika basu wannan kudin cake kawai zai fiddasu cikin kuncin rayuwarsu kuwa?

Mom tace toh ustaziya ai kyabari ki huta kafin kifara wa azin naki da baki gajiya dayinshi koh?

Wata mata ce ta kalli Aneesa kana tace lallai ma Anee wallahi in bancin ina gari her excellency ta haifeki ko toh wallahi da babu abinda zai hanani tunanin ko daukoki tayi a gidan gajeyu

Yarinya da gatanki amma sam ga naira ga ga ….. amma sam baki damu da cinsu ba

Lallai ne kam bahaushe yayi gaskiya dayace Allah baiya baiwa mai wuka nama in da nice cikin wannan daular da sai na taki uban kowa inci mutuncin talaka kuma in kwana lfy amma kashhhh… sai gashi a lokacina babana teacher ne wanda hakan yasani a damuwa domin kuwa makarantar yan masu naira nake zuwa har kunyan gidanmu nake kuma ……

Hajiya Fatima tace habaa hajiya da kanta kibar bata yawunki indai akan ustaziya ce domin kuwa ko sauraranki bazatayi ba

Kinga da ace a Nigeria na haifeta kuma da ace tiyata akamin toh da bb abinda Zai hanani cewa an chanzamin yarinya

Aneesa kam sai jinsu take domin kuwa idan sabone tariga da ta saba dajin irin kalsamannan nasu mara dadi saidai babu yanda ta iya dasu tunda iyayenta ne a kullum addu’a take masu akan Alah shiryesu niko nace Ameen

Shin wacece ANEESA????

Kubiyoni don jin cikakken…….

Love u ol????
????????‍⚖ANEESA YAR PRESIDENT????????‍⚖

Na Hannatu Dada Kuta

????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????

wannan page din nakune YAN GROUP DIN RAYUWAR LEEMAT Allah bar kauna ????????????????????

               03

Wacece Aneesa?

Aneesa Abbas Abdullahi shine cikakken sunarta diyace a wurin Alhaji Abbas mutan Niger state amma a Abuja sukeda zama Alhaji Abbas hamshakin mai kudi ne wanda sunanshi ya shahara a kasashe da dama dan siyasa ne babba wanda aduk inda aka kira sunanshi sau 1 toh fa ba a kumawa domin kuwa sananne ne na karshe…..
matarshi 1 Hajiya Fatima Dada Kuta wacce akafi sani da TIMABBAS dukkansu gwarawa ne kuma gwarin shiroro ne soyayya ce mai karfi a tsakanin ma auratannan biyu wanda hakan ya sanyasu hada sunanyensu gu 1 Fatima da Abbas sai suka maidashi TIMABBAS babu wanda bai san masoyannan 2 ba
lokacinda suke koyarwa a wani makarantar matar aure dake SHIRORO LOCAL GOVERNMENT abu kamar wasa dai har manya suka shigo tsakani bayan an daura aurensu ne Allah ya albarkancesu da yaya 2 Abdul-Basit da Aneesa ana haka sai Alhaji Abbas yashiga siyasa Allah yabashi sa a yacinye zabenshi a karo na 1 inda yafito takarar House of Assembly daga nan ne yakuma fitowa na House of rep sai yanzu da yake neman shugaban kasa dukiya kam ba a magana domin kuwa ya tarasu abin sai wanda yagani ga boutique nan na gani a fada daya budema Hajja Fati wannan kenan

Cigaban Labari
Hajiya Fatima tace Ustaziya bismillah zo muci abinci sannan ki hau sama ki huta in yaso daga baya kyayi wa azin naki da kika saba ba musu Aneesa ta mike sai kan dinning wasu yan mata ne sunsha uniform jiki na rawa suka bubbude warmers dinda ke kan dinning table din Aneesa ta sakarwa da daya daga cikinsu smile kana tace da ita haba Aisha Aneesa ce ke zaune anan fa ba …. Hajiya Fatima ce ta iso da mukarrabanta hajiya Rahma ta kwashe Aisha da wani wawan mari wanda ya firgita kowa kana tace dan kutuman bu…….. mu tsaranki ne ko kuwa Anee din tsararkice da zaki kura mata ido harda murmusawa dan Ubanki ko slippers din Anee ya isa ya ciyar da ke da danginku gabaki daya shegiya kawai nifa na tsaneki tun ranarda nasakaki a idanuwa Allah kadai yamasani ko me kika bawa diyarmu da take ji dake kamar wata class dinta Aneesa kam ji tayi ba dadi hakan yasata ta mike dan bazata iya jure ganin rashin mutuncinda Hajiya Rahma kema Aisha ba kawai saboda dan ta tsaneta ba sannan bazaka ce hajja Rahma tabaka kwakkwaran dalilin tsanan Aisha datayi ba tabaka ba sai dai kaji tana zubo maka lbrin da bakai ba gindi…….

Hajiya Fatima tace……

Love u all????????????
????????‍⚖ANEESA YAR PRESIDENT????????‍⚖
Na Hannatu Dada Kuta
????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????

1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21 22 23 24 25 26 27 28 29 30 31 32Next page

Related Articles

Leave a Reply

Back to top button