BABU SO HAUSA NOVEL

ANEESA YAR PRESIDENT HAUSA NOVEL

Alhmdllh Allah nagode maka to yanzu sai love koh Sweet Anee…….

Ido ta fiddosu waje kamar zasu fado kasa kana tace ai toh baka gama bani amsa ba me nake karantawa????

Damm….. zuciyar Ashraf ce ta buga akaro na biyu amma daya tuno da cewar Allah ne yabashi sa’ar na farkon sai kawai yaci gaba da addu’a acikin zuciyarshi

Budan bakinshi sai cewa yayi kina karanta biology/chemistry ne

Kaiiiiii……. Allah ban yarda ba dama yasan sunana da abinda nake karantawa Adama nasan kece kika fada mashi

Dariya suka fara mata ganin yanda taketa zuba duk tabi ta rude kawai saboda zata fara soyayya Adama ce tace wallahi Anee ban gaya masa komai ba kawai ki dauka wannan hadin daga Allah ne

Kuma ma da kikabi kika daga hankalinki soyayyarnan fa ta sati biyu ce kacal fa Smile Ashraf yayi kana yana fada a zuciyarshi cewar Adama kenan ai wannan soyayyar ta har abada ce nida Aneesa ta sai mutuwa kai ko mutuwarma……..

Adama ce ta katseshi dacewar bari nabaku guri kufara soyayya kana ya furta a fili cikin razana cewar har a kiyama ma muna tare inshaa Allah

Aneesa tace kaida wa?

Shiru yayi dan baimasan lokacinda ya furta hakan ba

Adama tace toh sarkin love nidai kwaga tafiyata sai kin shigo

Ashraf ne yace haba Adama dawo kiyi zamanki toh kawai tace sannan ta zauna Aneesa da duk tabi ta rude tace nidai zan shige ciki sai anjimanku Ashraf yace haba Sahibata dan Allah ki zauna mudanyi hira

Aneesa tace ba yanzu ba Adama tace ohhhh wai so take kaje gidansu

Aneesa tace waneshi ai baisan gidanmu ba idan kuma ya sani toh in ganshi acen yau kafin in isa gida smile ashraf yayi kana ya furta shiyafi komai sauki

Aneesa tace me?

Yace zuwa gidannaku mana nan Aneesa tace toh shine na ukunda zaka cikasa kafin in aminta da soyayyar 2 weeks din takarashe maganar tana smile

Shima smile din ya mayar mata nanfa sukaci gaba da hira har 1:30pm ganin lokacin sallah yayi ne yasa dukkansu mikewa ashraf yayi gaba sukuma suka wuce masallaci don sauke farali

Ina labarin Hajja rahma????

✍????by Leemat

Love u all❤????????
????????‍⚖ANEESA YAR PRESIDENT????????‍⚖
Na Hannatu Dada Kuta
????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????

UMMU SAFWAN HAUSA NOVELS????

                      18

Hajja Rahma tunda taje gidan bokanta tasa aka turama Aneesa bakin aljani shikenan hankalinta ta kwanta sai taji kamar an mata kyautar Aljannah

Alokacinda taji lbrin abinda ke faruwa da Aneesa taji dadi kuma bataji dadi ba abinda yasa bataji dadi ba kuwa shine ba haka taso ba taso Aneesa tayi hauka ne ko kuma tayita tafiyarta ta bar nigeria gabaki dayanta na har abada sai gashi hakan bai samu ba

Toh fa nan takuma komawa akan ama Aneesa kurciya tabar nigeria amma kar a haukatarda ita asa ta dan dimauce kadan da zarar tabar nigeria hankalinta ya dawo amma kar ta tuna komai gameda rayuwarta hmmmm niko nace kunji wata sabuwa

Karfe 4:30pm su Aneesa na hango cikin mota sai faman hirarsu suketayi abinsu hankali kwance har ta isa kofar gidansu Adama nan ta sauketa sannan sukayi bankwana kasancewar gobe basuda lecture Adama ta shaidama Aneesa cewa gobe tana nan zuwa mata hira toh kawai aneesa tace kana tace Allah kaimu Allah kawomin ke lfy Ameen Adama ta amsa sannan ta dagama Aneesa hannu

Aneesa nakaiwa kofar gate dinsu ai kuwa sai ji take kirjinta na buga 3 uku

Ai kuwa me zata gani?

Motace anyi parking kusa da gate din ganin Ahsraf jingine da motar yana smile yasata daure fuska ai kuwa sai tayi kamar batasan ma da mutum a wurin ba

Baba na bude mata gate sai tayi shigewarta ganin haka yasa Ashraf zuwa daidai baba zai rufe gate din ganin Ashraf yasashi smile Ashraf kuwa ya gaidaahi cikin girmamawa

Sannan baba yake tambayarshi wa yake nema ai kafin ya bude baki da sauri Aneesa tace baba ai kuwa juyowa yayi yana kallonta har ta karaso wurin nan ta gaida baba sannan tace baba jeka abinka dan makarantarmu ne

Ok toh yar Albarka juyawa yayi ya karasa rufe gate din sannan yashige cikin gida

Nan ta maido da kallonta ga Ashraf wanda shima ita yake kallo tace Ashraf kk koh ma menene ya akayi kasan gidanmu

Kagafa ni bana soyayya ban tabayi ba kuma bana sha’awar yinta yanzu

Ashraf yana kallon yanda Aneesa keta yimai masifa har takai aya bai amsa mata ba sai faman smile yaketayi

Hakan ne yabata haushi ai kuwa tajuya zata shige cikin gida Ashraf yace Sweet Anee dan Allah ki bani minti 2

Juyowa tayi amma batace dashi kala ba

Smile yayi kafin ya fara magana

Yace Angel ina kaunarki dan Allah kibani dama muyi soyayya koda na 1 week ne idan har bakiji komai akaina ba toh ni Ashraf nayi alkawarin barinki har abada

Hmmmm… yaci gaba da magana har saida yakai aya sannan aneesa tace ok naji nakuma amince amma pls banda takura kuma …….

Sai kuma tayi shiru ashraf yace kuma me sai tace kuma bkm smile Ashraf yayi kana yace ok toh yanzu dai bara nazo na tafi saboda kisau ki huta yanzu in yaso sai zuwa anjima kamar 8pm dinnan sai nazo muyi hira koh

Ido Aneesa ta fiddosu waje kana tace aa karkazo ni kaga ka rufamin asiri nidai babu ruwana wato kanaso baba da mama su dauka na fara soyayya ne ko bacin ba soyayyar gaskiya bane…….

Ashraf yayi maza yace inji waye yagaya maki ba soyayyar gaskiya bace?

Tabe baki Aneesa tayi kana tace toh dama na gaskiya ce ai soyayyar 2weeks ce kawai

Aahraf yayi smile kafin yace ok naji ba soyayyar gaakiya bace amma inaso mu daukeshi kamar na gaskiya ta inda mutane zasu gamsu da soyayyarda mukema juna harda kula da juna zamu rika yi

Aneesa tace nidai bamuyi haka dakai ba Ashraf yace ai basai munyi hakan dake ba kinga kyan alkawari cikawa ina nan zuwa anjima sannan kuma karki manta saida kika bani aiki har 3 kafin nan kika amince da soyayyar dan haka yanzu turn dina ne ya karishe maganar yana kashe mata ido????

Aneesa tace kai dama nasani da ban yarda da hakan ba kaga nifa banason takura toh kaga tafiyata Ashraf yace toh sai nazo

Aneesa bata juyoba har saida takai bakin gate sannan ta juyo har lokacin idon Ashraf na kanta sai ji yayi tace toh naji din saika zo amma karkazo ka takurawa babana idan ka iso kawai ka kirani ta waya

Ashraf yace toh zo kibani number taki smile Aneesa tayi kana tace ba ka iya searching sunana da abinda nake karantawa ba?

Toh kaje kayi searching din number ta a google dinka idan har kasamota shikenan an gama takarashe maganar tana dariyar mugunta dan ita aganinta bazai samu ba nan tace sai najika anjimar koh?

Bata tsaya jiran amsarshi ba tayi shigewarta abinta smile ashraf yayi kana ya furta Aneesa kenan lallai bakisan waye Ashraf ba Allah akanki sai ince nafi kuda naci wurin shan mangwaro

Shigewa cikin motarshi yayi ya tadata bai tsaya ko inaba sai kofar gidansu Adama yana isa yayi sa’a sharif ya dawo daga aikenda ummansu tamasa zai shiga gida kenan sai Ashraf yace ji mana dan Karamin abokina

Sharif ya juyo yana washe hakora nan ya gaida Ashraf bayan ya amsa ne yace halan kai kadin adama ne dan naga kuna kama da ita eh ni kaninta ne kasan Anty Adama muguwa ce idan bamuyi homework dinmu ba sai ta zanemu ko kuma ta hanamu kallo kasan saurayintannan mai zuwa nan shikuma ba…. ……. Ashraf ne yace kai abokina shiga ka kiramin ita kace ana nemanta a waje

Toh sharif ya shige ashraf dariya yayi kafin yace ohhhhh God……….. me nayi ne wai yau…….

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21 22 23 24 25 26 27 28 29 30 31 32Next page

Related Articles

Leave a Reply

Back to top button