RAUDHA 1-END

RAUDHA Page 31 to 40

“Wayyo Allana! na shiga uku”. Ya faɗa a ransa yana runtse idanu

Ko motsi ya gaza yi illa sauraron kukan ta da yake yi, daƙyar ya iya jarumtar jan ƙafafuwan sa zuwa bakin ƙofan ya rufe suka sake dawowa, kan gadon ya nufa ya sake janye ta ya zaunar da ita sannan shima ya zauna, ganin zata sake shige masa jiki yace, “kee kina da hankali kuwa? Ko kina son in cutar dake ne? Kin ishe Ni fa”.

Hakan be sa RAUDHA ta dakata daga abinda tayi ninya ba

Sai yayi zumbur ya tashi yana daka mata tsawa

“Keee! Ki koma ki kwanta ko ki bar min ɗaki na”.

Sosai RAUDHA ta tsora ta da ganin yanda ya kirne fuska, gashi tsawan da yayi mata har tsakar kanta sai da ya amsa, nan ta sake rikice wa ta hau fasa masa kuka, sai dai ta kasa motsawa daga inda take, cikin rawan baki tace, “tso..roo nake ji..” tayi maganar numfashin ta na sama tamkar zai ɗauke

Sai ta bashi tausayi matuƙa, shima ba wai yana hakan sabida ba ya so ta raɓe sa bane, gudun kar wani abu ya faru ne, ya zo ya aikata dana sani, abinda ba ya fatar kasancewar shi

Komawa yayi ya zauna, cikin lallami ya soma rarrashin ta, daƙyar ya samu ta kwanta a bakin gadon, shima sai da ta riƙe masa riga gagam kafin ta rufe idanun ta, kuma ba ta yin mintuna biyu take sake buɗe idanun don ta tabbatar yana wajen, duk da kuwa tana riƙe da rigan sa

Shi dai Rayyan tagumi ya zuba kawai yana kallon ta, ji kawai yake yi da ma matar sa ce? Har ya ga abinda zai biyo baya

Numfashi kawai yake sauke wa tsawon wasu awanni, sai da ya tabbatar da ta daɗe da koma wa barci kafin ya janye rigan sa ahankali, tashi yayi ya shiga Toilet yayi uzurin sa, sannan ya dawo ya ɗauki pilow ya koma kan sofa ya kwanta, sai dai ya kasa barci, tsananin tunanin RAUDHA ya hana sa sukuni, sai juye-juye yake yi, daga ƙarshe gyara kwanciyar sa yayi; yayi Facing ɗin ta yana kallon ta, ahaka be san sanda barci ya ɗauke sa ba.

      Da asuba da ya tashi ya ɗauro alwala, sai ya nufi inda take ya hau tashin ta, but ko motsi taƙi yi, juyin duniya yayi ya tashe ta but taƙi, aransa tunani yake “ta cika mugun barci, sai ka ce wata gawa” ganin zai yi latti sai ya fice abun sa.

      Koda ya dawo ma, ya gwada tashin ta, nan ma be yi nasara ba, tsayawa yayi kawai yana kallon ta

“Anya ma yarinyan nan tana sallah?” Yafaɗa a ransa

Sai kuma ya saka hannu ya birkito ta yana faɗin, “ke RAUDHA tashi mana, ki tashi kiyi sallah”.

Shanyayyun idanuwan ta tabuɗe akan sa, tana yi tana rufe wa

“Tashi ko”. Ya sake faɗa yana ɗan bugun kumatun ta

Sake langaɓe wa tayi tana son koma wa ta kwanta

“Keee tashi mana, wannan wani irin barci ne haka, tashi na ce ko in ɗibo ruwa in zuba miki”.

Tarwai ta buɗe ido akansa, kallon sa kawai take yi tana son tunano abunda ke faruwa har tagan shi kusa da ita, jujjuya kanta ta soma yi tana kallon ɗakin

Shi kuma sai yaja ƙafafuwan sa ya nufi kan sofa ya zauna, sannan ya mayar da idanun sa kan ta ya ce, “ki tashi kiyi sallah lokaci na tafiya”.

Bata motsa ba illa lumshe idanu da tayi tana matse gashin kanta da hannu ɗaya, sai a time ɗin komi ya dawo mata ƙwaƙwalwa, sake ware idanuwan ta tayi tana kallon sa

Shima dai ita yake kallo, sai ya ɗauke kai abinsa, be sake bi ta kanta ba illa wayan sa da ya ɗauka ya soma latsawa

Ita kuma taƙi ta tashi, sabida baza ta iya barin ɗakin ba, gani take yi idan ta koma can ɗakin zata ga waɗannan halittun da ta gani a mafarkin ta, shiru tayi ta faɗa tunani, sai yanzu take jin kewar yayan ta, ta tabbata da akwai shi, da a yanzu tana nan maƙale dashi, kuma baza ta ji tsoro haka ba.

 

         Ray ganin taƙi tashi ta fitan masa a ɗaki, sai ya miƙe ya nufi Toilet ya shige, wanka yayi sabida ganin gari ya soma haske, sai ya fito ɗaure da towel yana tsane jikin sa, ko a jikin sa be damu don akwai ta a cikin ɗakin ba, ta yiwu ma tabar masa ɗakin idan taga yana shirya wa

    Amma be san cewa RAUDHA ko a jikin ta ba; wai don ta gansa a haka, tunda ta kalle shi sau ɗaya ta ɗauke kai ta yunƙura ta tashi zaune tana faman matsa cinyoyin ta.

    A sace yake kallon ta, ganin taƙi tashi sai kawai ya taɓe baki, aransa yana faɗin, “dama ya za’a yi ki ji tsoron gani na ahaka tunda kin saba ganin gardawan banza”.

Sai maganar ya ƙular dashi, sabida tsananin kishi da yaji ya turniƙe shi, tamkar wani ne yayi maganar ba shi ba, kallon ta yayi suka haɗa ido, ya ɗaure fuska tamau ganin yanda take bin sa da kallo

“Ke tashi ki fitar min a ɗaki zan shirya, tunda ke baki da kunya Ni ina dashi”.

Tamkar sokuwa haka take bin shi da kallo, sai dai maganar na sa sun yi mata tsauri, don ta kasa fassara su

“Baza ki tashi bane ina miki magana kina kallo na? Fitar min a ɗaki na ce zan shirya, tunda ba a gaban ki zan shirya ba”.

Sai anan RAUDHA ta fahimci inda ya dosa, sai ta taɓe baki cike da tsantsan tsanar sa ta ce, “menene a jikin naka da zan kalla? kai baka isa ka kai namijin da zai tsole wa RAUDHA ido ba, nafi ƙarfin ka har ABADA”. Ta ƙare maganar tana zaro masa ido

Ran sa yayi mugun ɓaci, be yi wata-wata ba ya nufo ta, ya saka hannu zai…

.

_Tooo! Me kuma zaka sake janyo mana Captain Ray? ????_

_Babu ruwana Ni dai???? ????????‍♀️????????‍♀️_

[3/17, 8:25 AM] نفيسة أم طاهرة: ????????????????????????????????????????

????????????????????

????????????????????

   *RAUDHA*

????????????????????

????????????????????

????????????????????????????????????????

*MALLAKAR:* ✍️

              _Nafisat Ismail Lawal Goma._

*بسم الله الرحمن الرحيم*

 

???????????????????????? ????????????????????????’???? ????????????????????

®Ɗ???????????? ???????????????????????? ???????? ????????????????????✓

*JIKAR LAWALI CE*✍️

*Wattapad: UmmuDahirah*????

         *F.W.A????/*

.

  *NOT EDITED* ___________________________????

        *SEASON THIRTY FOUR*

_______???? Marin ta ya so yi, sai kuma ya dunƙule hannun nasa ya duki iska

Ko kaɗan shi ba mutum bane me son dukan mata, bare kuma ita tana da babban matsayi a zuciyar sa, shiyasa da zaran ya so ɗaukan mummunan mataki akanta yake kasa wa, amma ba don haka ba; wlh da tuni ya nuna mata kuskuren ta a rayuwa, domin baza ta taɓa manta shi ba, shi mutum ne da ba ya ɗaukan raini.

     Hannun sa ya saka ya finciko ta daga kan gadon

Ƙwalla ƙara tayi sabida a zaban da ya ziyarce ta, sakamako jan mata hannu da yayi har sai da yayi ƙara tamkar ya karye, kuma be barta haka ba sai da ya matse hannun ta yanda zata ji zafi sosai

Waje yayi ya jefar da ita a bakin ƙofan, sannan ya mayar da ƙofan ya rufe garam

Kuka ta fashe dashi, ta taso da gudu tana dukan ƙofan, kuka sosai take yi tana kiran sa ya buɗe mata ƙofan

But Ray na jinta yayi biris da ita, a ganin sa in ba iskanci ba taya zata maƙale masa a ɗaki; daga taimako?. Ran sa duk a ɓace yake haka ya gama shirin sa cikin uniform ɗin aikin sa, kayan sun bala’in yi masa kyau sun sake fito da zallan yarintan sa da hasken skin ɗin sa, gaban mirror yaje ya gyara suman kansa tare da siririn sajen sa, sannan ya feshe jikin sa da parfomer’s masu shegen ƙamshi, sake gyara zaman wandon sa yayi sannan ya nufi bakin gadon ya ɗauki wayan sa tare da nufo wa bakin ƙofan

Yana buɗe ƙofan ta faɗo kansa, da sauri ya sake riƙe ta yana kallon fuskarta da yayi caɓe-caɓe da hawaye, lumshe ido kawai yayi yana jin saukar ajiyar zuciyar ta a ƙirjin sa, ko kaɗan ya kasa janye ta a jikin sa sabida wani irin kasala da ya ziyarce sa

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14Next page

Related Articles

Leave a Reply

Back to top button