RAUDHA 1-END

RAUDHA Page 31 to 40

Cikin girmamawa ta amsa masa

Sannan ya taka ya wuce.

        Sai da ta gama gyaran kafin ta wuce ɗakin RAUDHA, time ɗin tuni ta tashi daga barcin, duk da kuwa jikin ta babu wani zazzaɓi yanzu, but zafin jikin ya ƙi sauka, sai kuma kanta da har yanzu yake mata ciwo, tana kwance har a lokacin

Zuwan Ester sai taji daɗin ganin ta, nan ta nuna mata inda zata ɗauko mata magani tasha

Daƙyar ma Ester ɗin ta iya jin abinda ta faɗa mata, domin ko kaɗan muryan ta ba ya fita, gaba ɗaya ya disashe sai kaɗan

Ester fita tayi ta haɗo mata tea me kauri kamar yanda ta buƙata, sannan ta kawo mata, ta koma tasoma gyaran ɗakin da yayi kaca-kaca, a ranta tana mamakin abinda ya faru ɗakin ya hargitse haka, gashi can ma Parlour ta ga an tarwatsa Centre table, sai dai babu halin tambayar tunda bata ga fuska wajen wanda zata yi mata tambayan ba, aikin ta taci gaba da yi, sai da ta kwashe Glassess ɗin ta fitar dashi sannan ta soma share wa.

        Koda RAUDHA ta gama shan tea ɗin sai ta kora da magani, ta miƙe ahankali tanufi Toilet, wanke bakin ta tayi sannan tayi buƙatar ta; ta fito tanufi kan sofa ta zauna, don alokacin Ester na gyaran gadon ne

Wayan ta tasaka Ester ta miƙo mata, ta’amsa ta riƙe da yatsun ta, don su ne kaɗai zata iya sarrafa wa, ta soma latsawa tana neman Numban yayan ta, duk da ta ga messages but bata duba ba, sai dai numban nasa ba ya shiga saboda network, sai ta mayar da akalan kiran ga Rash, ringing biyu ta ɗauka, magana RAUDHAN ta soma yi sai dai Rash ba ta jin ta, dole ta katse tashiga message inbox tasoma yin mata typing:

         “`”Rash Ina buƙatar ki zo gidan mu yanzu ina neman ki, ki taho da mota please”.“`

Babu jimawa itama ta dawo mata da reply ɗin ta:

_”Ok! Me ya faru ne wai Babe? Mun kira wayan ki duk bamu samu ba, mun biyo sawu kuma gidan a rufe, wanene mutumin nan da ya ɗauke ki a Club? Gaba ɗaya mun shiga tashin hankali wallahi, kuma sai ga shi baki zo school ba”._

Nan RAUDHA ta soma faɗa mata abinda ke faruwa, sun jima suna chart ɗin, suna ƙulla yanda zasu zo su ɗauki RAUDHA tabar gidan gaba ɗaya, daga nan ta koma can da zama.

        Har zata fita daga text message ɗin kuma; sai ta tsaya duba message ɗin da takula an yi mata har sau biyu, da baƙon number ne, koda ta buɗe na farkon an rubuta:

     _”Aslm alaikum ya ke wannan kyakykyawa, Barka da arziƙin kasancewar ki cikin ƙoshin lafiya da kuma samun asalin nasarar cafke zuciyar da bata san komi ba face soyayyar ki ya ke me cikon burina, ɗumbin gaisuwa me cike da fatan alheri a gare ki, tabbas na daɗe ina kallon taurarin samaniya yayinda naga wacce tafi ko wacce haske, sai na ga ba kowa bace nake gani sai ke, sannan na daɗe ina neman wata kalma wadda babu wanda ya santa, sai gashi a lokacin da na same ki sai na samu wannan kalman, RAUDHA ke ta daban ce, kuma ke kyakkyawa ce, kin zarce sauran mata. Haƙiƙa so gamon jini ne, kuma ya kama Ni, don a yanzu ina faɗa miki yarigada ya zama jinin jikina, ƙaunar ki RAUDHA ta rigada tayi min dabaibayin da ba na tunanin zan iya kufce wa face na mallake ki ba, ina son ki RAUDHA, Ina matuƙar ƙaunar ki, na zaɓi wannan hanyan ne don sanar dake abinda ke cikin zuciyata, domin shi ne kaɗai hanya me sauƙi da zan iya fahimtar dake abinda ke raina. Ki kasance cikin farin ciki har abada pretty”._

      Ɗayan ta sake buɗe wa ta soma karanta wa

_”Ba zan iya rayuwa idan ba tare da ke ba, a mafarki da kuma a cikin soyayya babu abinda ba zai iya faruwa ba. Ina son ki sosai hakan ya sa nake ji tamkar ba zan iya rayuwa idan ba tare da ke ba. Ba na fatan rasa ki a rayuwa ta, domin kuwa a duk kan lokacin da na rasa ki, na tabbatar da rayuwata zata shiga garari, ina son ki kuma ba zan taɓa sanja wa ahakan ba, ke ce murmushi na, domin da akwai miliyoyin furanni a cikin lambun masoya a wannan duniya. Da ace zan tsunko ko wanne fure na baki shi a hannun ki, hakan bai isa ya bayyanar da adadin yanda nake son ki ba, pretty ke ce murmushi na! kuma ke ce farin cikina! ina matuƙar ƙaunar ki da dukan zuciyata! ki bani dama don Allah, dama ɗaya tak”._

     Shiru RAUDHA tayi tana tunanin wanda ya aiko mata da wannan text ɗin, sai kuma taja tsaki tana jin ranta na mugun ɓaci, domin a rayuwa babu abinda ta tsana sama da soyayya, ko kaɗan kalaman nan basu burge ta ba, sai ma ɓacin rai da jin haushin wanda ya turo ya saka ta

Ajiye wayan tayi ta kwanta tana me lumshe idanuwan ta.

.

_Ba na samun Comment masoya? Ko dai a dena?_

[3/16, 3:20 PM] نفيسة أم طاهرة: ????????????????????????????????????????

????????????????????

????????????????????

   ????????????????????????

????????????????????

????????????????????

????????????????????????????????????????

????????????????????????????????: ✍️

              ???????????????????????????? ????????????????’???????? ???????????????????? ????????????????.

*بسم الله الرحمن الرحيم*

 

???????????????????????? ????????????????????????’???? ????????????????????

®Ɗ???????????? ???????????????????????? ???????? ????????????????????✓

???????????????????? ???????????????????????? ????????✍️

????????????????????????????: ????????????????????????????????????????????????

         ????.????.????????/

.

  ???????????? ???????????????????????? ___________________________????

        ???????????????????????? ???????????????????????? ????????????

_______???? Bata fi mintuna biyu da ajiye wayan ba, kiran Suhaib ya shigo, tashi zaune tayi tana peacking ta kara a kunne, sai dai taƙi yin magana sai ta fashe mishi da kuka

Suhaib ya rikice don ya ɗauka wani abun ne, ya soma rarrashin ta cike da sanyin murya, don a yanzu sosai ya shiga damuwa da yanayin da ƙanwar ta sa take ciki tun tahowar su, ko yaushe kuka

“Baby menene? ki faɗa min abinda ke damun ki kar ki saka zuciyata ta buga, kullum a cikin damuwa nake saboda halin da kike ciki”.

Cikin kukan tace, “Yaya ni bazan zauna da mutumin nan ba, don Allah ka dawo ka tafi dani, ba na ƙaunar sa, na matuƙar tsanar sa fiye da mutuwa, wlh yaya sai na kashe sa duk sanda na zama soja, da bindiga na zan harbe sa”.

“Baby soja kuma? Taya zaki zama soja? Please baby ki dena kiyi haƙuri bazai sake miki wani abu ba, baki fahimci halin Abokina bane, amma shi ba mugu bane..”

Kuka ta saka mishi, dole yayi shiru ya hau rarrashin ta kamar zai yi mata kuka, sosai yake jin kukan nata har cikin ransa, ya rasa ya zai yi, don duk yanda ya so ya rarrashi RAUDHA ta ƙi, daga ƙarshe ma kashe wayan ta tayi, koda ya sake kira sai taƙi ɗauka, haka yayi ta kira but taƙi peacking, dole ya hakura ba don ya so ba

Ita kuma kukan ta kawai taci gaba da yi ko kallon wayan bata sake yi ba, sai can daga baya ta sake jin wani kiran, har zata share sai kuma ta tuna ko Rash ne, ilai kuwa ita ɗin ce, tayi saurin ɗaukan wayan tana kara wa a kunne bayan tayi peacking

“Hello kin zo ne?”

Daga can Rash tace, “wlh Baby babu yanda za’a yi mu shiga gidan, domin sojoji ne kewaye a gidan, kuma sun hana Ni shigowa duk da nayi musu bayanin wajen ki muka zo, sun ce ogan su yace, “kar su bar kowa idan wajen ki zai zo…”

Ba ta ma tsaya jin ƙarisan bayanin ba tayi jifa da wayan ta hau rusa kuka, azuciye ta miƙe tayi hanyan ƙofa ta fice, Parlour ta nufa sai dai babu kowa, sai ta koma saman ta nufi ɗakin Ray, tura ƙofan tayi da karfi, sai dai babu shi sai sassanyan ƙamshin sa da ya shige mata hanci, wurwurga idanu ta soma yi cikin ɗakin kafin ta ƙarisa ciki tana jan majina, tsayawa tayi tsakiyar ɗakin, har ta juya zata fice sai kuma ta dawo ta soma bincike ta inda zata gano kayan mayen ta da ya kwashe, but bata samu ba, har Fridge ta duba babu a ciki, sai da tayi masa baja-baja da kaya sannan ta fice, ko bi takan gyarawa bata yi ba, ɗakin ta ta koma ta faɗa kan gado tana lumshe idanun ta, tunanin kawai abinda ya kamata tayi take yi, zuciyarta sosai take ta tafarfasa tamkar zata fito, idanuwan ta gaba ɗaya sun juje sun yi jazur kamar garwashin wuta, sai kawai ta soma wani irin kuka kamar na kenwa, ta silalo ƙasa tana fizge-fizge tana tafiyan maciji kamar zata shige ƙasan kujera.

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14Next page

Related Articles

Leave a Reply

Back to top button