RAUDHA 1-END

RAUDHA Page 31 to 40

????????????????????

   *RAUDHA*

????????????????????

????????????????????

????????????????????????????????????????

*MALLAKAR:* ✍️

              _Nafisat Isma’il Lawal Goma._

*بسم الله الرحمن الرحيم*

 

*FEENAH WRITER’S ASSO*????

“`®Ɗaya tamkar da Dubu“`????✓

*JIKAR LAWALI CE*✍️

*Wattapad: UmmuDahirah*????

         *F.W.A????/*

.

  *NOT EDITED* ___________________________????

        *SEASON THIRTY ONE*

_______???? Idanuwan ta ne suka lumshe sabida jinin ta dake faman kwaranya a ƙasa, ta faɗi babu alamun numfashi a tare da ita..

Sosai hankalin Suhaib yayi ƙololuwan tashi da jin kausasan kalaman ƙanwar sa, kiran sunan ta ya soma yi but babu amsar ta, da sauri ya katse kiran.

       Kamar mintuna biyar sai ga Rayyan ya shigo ɗakin sabida kiran da Suhaib yayi masa, ba don tashin hankalin da abokin sa yake ciki ba babu yanda za’a yi ya zo duba ta

Ganin ta a yashe cikin jini hankalin sa ya tashi matuƙa, domin be taɓa tunanin zata iya yin ma kanta illa ba, dasauri ya ƙarisa gaban ta yana kiran sunan ta, sai dai ganin ba ta numfashi sai yayi saurin ɗaukan ta ya aza ta kan gado, rasa inda zai samo abinda zai ɗaure mata hannayen yayi, da sauri ya cire t.Shirt ɗin jikin sa ya yaga tare da kamo hannun ta ya soma ɗaure wa, shi kansa tamkar yayi kuka sabida tsaban tausayin ta da ya shige sa, domin ba ƙaramin illa tayi wa hannayen ta ba, gaba ɗaya ta yayyanka sai zallan nama ake gani, “Anya yarinyan nan tana da hankali kuwa? Wanene zai yi wa kansa wannan mummunan hukuncin?”

Numfashi kawai yake sauke wa har ya gama ɗaɗɗaure mata hannayen, wayan shi dake ƙara ya ɗauka ya kara a kunne ganin Suhaib ne

Tambayan da Suhaib ɗin kawai ya jefo masa ya kiɗima sa, but sai yayi jarumta wajen tattaro nutsuwar sa tare da dai-dai ta muryan sa yace, “Dude ka kwantar da hankalin ka babu abinda ya same ta, ka ganta nan a gaba na wayan ta ta rotsa a ƙasa, kuma na ba ta nawa tayi magana da kai taƙi, kasan ƙanwar ta ka akwai taurin kai”.

Shiru yayi yana sauraron Suhaib ɗin

Murmushi ya saki yace, “baka fi Ni son ta ba Dude, ƙanwar ka ƙanwata ce, bazan ɗau matakin da zai mata illa ba, da yardan Allah zan yi iya ƙoƙarina wajen nuna wa RAUDHA hanyar Gaskiya, zan kula da ita sosai”.

Numfashi yaja idanun sa a kan kyakykyawar fuskar RAUDHA, sai da suka yi kamar two minutes suna wayan kafin ya tsinke, Numban wani abokin sa ya lalubo ya kira, bayan ya ɗauka sun gaisa ya buƙaci ya samo masa doctor, daga nan katse kiran yayi ya saka wayan a aljihun wandon sa, gefen gadon ya zauna yana tsira mata idanu tamkar zai cinye ta, tunani ne kawai fal a ransa duk zuciyar sa ta cinkushe, fesar da numfashi daga bakin sa kawai yake faman yi, har sanda abokin sa ya kira sa ya sanar masa ya kawo doctor ɗin, tashi yayi ya fita haraban gidan, acan suka haɗu suka gaisa sannan suka shigo da doctor ɗin, shi kuma abokin ya tafi don a tunanin sa Ray ɗin ne babu lafiya duk da kuwa ya faɗa masa ba shi bane, amma kuma sai yaƙi yarda sai da yazo ya gani da idanun sa.

     Da suka shiga ɗakin likitan ya soma duba ta

Shi kuma Ray zama yayi kan stool ɗin dressing mirror bayan da ya ɗauko wayan ta dake yashe a ƙasa, danne-danne ya soma yi aciki na ɗan wani lokaci kafin ya ajiye, ya mayar da hankalin sa kan aikin likita

Time ɗin ma likitan har ya gama yana naɗe mata hannayen da bandage, bayan ya gama ya juyo ya fuskanci Ray yana masa bayani ta yanda za’a kula da hannun, sallama suka yi sannan ya fice

Rayyan tashi yayi ya iso bakin gadon ya tsaya yana kallon ta, ya daɗe ahaka yana faman tunani idanun sa akanta kafin yaja dogon numfashi ya juya ya fice, ɗakin sa ya koma ya kwanta yaci gaba da tunanin sa, sai da aka kira sallan magriba kafin ya tashi ya ɗauro alwala ya fice.

      Sai wajen ƙarfe 08:30pm kafin RAUDHA ta farka, yanda taji hannun ta na mata zugi babu shiri ta runtse idanuwan ta tana hawaye, abubuwan da suka faru daga jiya zuwa yau suke ta kai kawo cikin zuciyarta, nan da nan hawayen fuskarta suka ci gaba da ɓulɓulowa tamkar an kunna famfo, buɗe idon tayi ta ɗago hannayen ta tana kallo tana tsiyayar hawaye, ta jima ahaka kafin ta tashi zaune, ahankali ta sauko tayi cikin Toilet daƙyar, so take yi tayi fitsari but hannun ta gaba ɗaya ciwo ne, daƙyar take iya ma sarrafa hannun ta, haka dai da dabara tayi fitsarin tana kuka sannan ta fito, yunwan dake cin ta yasa ta nufi hanyan fita.

      Parlour’n babu kowa sai hasken lantarki, kan dainning ta nufa ta zauna tana tsira wa coololin wajen kumburarrun idanunta, sai kawai ta fashe da kuka tana kifa kanta saman table ɗin ta soma rerawa.

      Rayyan da tun jiyo motsin ƙofan ta yafito yabi bayan ta, sai dai daga ƙarshen benen ya tsaya yana bin ta da ido, sosai ta ba shi tausayi don ya san babu yanda za’a yi ta iya cin abinci, ahankali ya soma takawa yanufi wajen dainning ɗin, har ya ja kujera nesa da ita ya zauna bata sani ba, sai da ya soma buɗe coolarn ya ɗauki Plate kafin tajiyo motsi ta ɗago tana kallon sa

Idanun ta kawai ta saka masa tana sake jin tsanar sa na ƙara kumbura a zuciyarta, bata motsa ba har sanda ya nuna mata abincin da ya zuba “wai taci”.

Ƙanƙance idanuwan ta tayi cikin baƙin ciki da tsananin fushi tace, “I hate youuuuuuuu so much”.

Tamiƙe da gudu tayi hanyan Steps ta wuce ɗakin ta

     Da kallo ya bi ta, kafin ya taɓe baki yajuya kai ya soma cin abincin, a ransa yana tunanin wace iriyan yarinya ce wannan? Ba ya tunanin ma ƙwaƙwalwan ta ƙalau ne.

      Tana shiga ɗaki tayi kan gadon ta tazauna gefen gadon ta soma rusa kuka, tana yi tana saka damtsen hannun ta tana share hawayen ta, sabida ko ganin ɗakin ba ta yi yanda hawayen ta ke kwaranya, ta jima tana zaune tana kukan kafin tayi shiru tana sauke ajiyan zuciya, tsaban kuka har datse harshe take yi sabida sauke ajiyan zuciya da take yi akai-akai

Miƙewa tayi ta isa bakin Fridge, ahankali ta saka hannu ta buɗe taciro Robbern coke guda biyu ta ajiye a ƙasa, rufewa tayi takoma wajen kayan zaƙin ta, anan ta samo cake da ya rage guda ɗaya ta dawo gaban Fridge ɗin ta zauna, haka ta dinga kora lemun tana haɗawa da cake ɗin daƙyar, har ta cinye

Sai da ta samu ruwa cikin Fridge ɗin ta kuskure bakin ta ta zubar a wajen kafin ta tashi ta haye gado, nan wani sabbin hawayen suka soma sintiri a face ɗin ta, sosai take jin azaban hannun ta, ga kuma jikin ta dake faman mata ciwo saboda haukan da tayi jiya, tana buƙatar wanka amma babu hali, ƙiri-ƙiri ta kasa yin barci a wannan daren, kuka kawai ta dinga yi sai da kanta ya ɗau zuuu yana mata ciwo sosai kafin ta shafa wa kanta lafiya, tuni zazzaɓi ya rufe ta, har ta miƙe da ninyan kwaso kayan mayen ta ta afa ko zata samu salama, sai ta tuna babu ko ɗaya, haka ta koma takwanta tana sake jin tsanar Ray na sake shigan ta, tasan babu wanda ya isa ya kwashe mata sai shi.

      Idanunta da suke a kumbure suka ƙanƙance ta aza a kan wayan ta dake faman ƙarar shigowan message a inda Ray ya ajiye, lumshe idanun tayi tana jin zafin zazzaɓin har cikin idanun ta, bata sake motsa wa ba har barci ya ɗauke ta daƙyar.

????????????????????????????????????????

        Washe gari ƙarfe 08:30am. Ray ya fito cikin shirin sa na sojoji, ɗakin RAUDHA yabi da kallo kamar ya shiga sai kuma ya sauka abun sa, acan Parlour ya haɗu da Ester tana gyara, ya kira ta ya bata Numban sa ya umarce ta “ta kula da RAUDHA, idan akwai matsala sai ta kira sa”.

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14Next page

Related Articles

Leave a Reply

Back to top button