RAUDHA 1-END

RAUDHA Page 31 to 40

Abinda be sani ba ita gaba ɗaya, ta dena karanta message ɗin na sa, duk da ba ta goge wa but taƙi ta buɗe ta karanta.

    Haka kwanaki suka fara shuɗe wa, time ɗin RAUDHA ta dawo normal ta dena jin tsoron da take ji, yanzu a ɗakin ta take kwana, ta so koma wa school but Rash ta sanar mata sun tafi hutu, don haka a ranan ta soma shirin fita yawo, tsawon watanni biyu kenan ko ƙofar Gate bata sake fita ba

Koda ta gama shiryawa ta sauko daga sama, Farida kaɗai ta tarar a parlour’n, tunda a time ɗin Suhaib yana wajen aiki, shima haka Rayyan, shi two days ma ba ya kwana agidan sabida aiki

Sallama tayi wa Farida kaɗai tafice abin ta

Itama Faridan bata tambaye ta inda zata je ba tunda ba yau ta saba fita bata sanar mata ba.

       Direct RAUDHA gidan su Rash ta wuce

Rash tayi murnan ganin ta ba kaɗan ba, haka ta rungume ta suna murna, kafin suka zube akan kujera

Rash tace, “Babe wlh kinyi mugun sauyawa, Ni da zan ganki kin rame kin yi baƙi sabida azaban wannan sojan, amma kuma sai naga kin sake haske kinyi ƙiba abun ki, tamkar baki da wani damuwa”.

Hararan ta RAUDHA tayi, sai kuma ta taɓe baki tace, “ina su Maan?”.

“Maan ya tafi garin su, acan yake hutun sa, d same shima Zen ya tafi hutu can asalin garin su, yace “bazai zauna ba tunda babu ke, shiyasa garin ba ya masa daɗi ya zaɓi yin hutun sa acan”.

RAUDHA bata sake magana ba dai, illa sauraren Rash dake ta faman zuba mata surutu take yi, labarin duk abinda ya faru da ba ta nan take ba ta, sannan ta sanar mata akwai casun da zasu haɗa sati me zuwa, birthday ɗin Maan za’a yi, kuma agidan nan zasu yi ba sai sun je club ba.

   Haka dai sukai ta hiran su, daga ƙarshe suka fita yawo. sai dare suka dawo, sai da RAUDHA ta sauke Rash a gida sannan itama ta wuce, tana yin peacking ta ɗauki jakan ta ta fito daga motan ta rufe, koda ta shiga parlour’n babu kowa, ɗakin ta tawuce ta zube akan gado tana riƙe kanta, lumshe idanu tayi tsawon mintuna goma kafin ta tashi zaune ta hau ciro ƙwayoyin da suka siyo, buɗe wa tayi ta ciri tables guda uku ta afa a baki, sannan ta ɗauki sauran ta adana a cikin drower ta saka keey, sannan ta zare ta ɓoye, tashi tayi ta shiga wanka, bata jima ba ta fito ta shirya cikin kayan barcin ta ta haye gado, a time ɗin daƙyar take iya ma sarrafa kanta, burin ta kawai taji ta a gado; shiyasa bata damu ta haɗu da kowa ba, ko kuma taci abinci; tunda sun yi ciye-ciyen su a wajen yawon su, babu jimawa barci ya ɗauke ta me tsananin daɗin da ta daɗe bata yi irin sa ba, domin ƙwayoyin sosai suka taimaka mata wajen yin barci me nutsuwa sosai.

[3/17, 8:38 AM] نفيسة أم طاهرة: ????????????????????????????????????????

????????????????????

????????????????????

   *RAUDHA*

????????????????????

????????????????????

????????????????????????????????????????

*MALLAKAR:* ✍️

              _Nafisat Ismail Lawal Goma._

*بسم الله الرحمن الرحيم*

 

*FEENAH WRITER’S ASSO*????

“`®Ɗaya tamkar da Dubu“`????✓

*JIKAR LAWALI CE*✍️

*Wattapad: UmmuDahirah*????

         *F.W.A????/*

.

  *NOT EDITED* ___________________________????

        *SEASON THIRTY FIVE*

_______???? A ranan da su Maan suka shirya gagarumin birthday ɗin shi, ƙarfe 05:00pm. RAUDHA ta shirya ta wuce, kasancewar dama da yamma za’a soma har zuwa dare.

    Sosai partyn ya haɗa manya-manyan guys masu ji da kansu, gashi ba ƙarya an kashe kuɗi sosai a wajen, wines ɗin ma da akayi ordaring ɗin su masu tsananin tsada ne

Haka suka wuni suna cashewa, ita kanta RAUDHA sosai ta saki jikin ta, ta shige cikin su Zen ana ta raha. sosai a ranan ta bugu, don ƙwayoyin da tasha ma sun fi ƙarfin ta, sai dai Rash ne ta dawo da ita gida, a time ɗin ƙarfe 08:pm. Ne na dare, lokacin Suhaib na masallaci sai Farida dake zaune a Parlour ita kaɗai, tunda Rayyan ba ya nan

Hankalin Farida ya tashi sosai sanda Rash ta shigo da RAUDHA tana surutai tamkar mara kai, sai dariya take yi tana maganganu, amsar ta tayi tana kallon Rash tace, “ke wai me tasha haka take wannan abun?”

Rash na sosa Kai tace, “kiyi haƙuri aunty, wlh party muka yi..” Sai tayi shiru ta kasa ƙarisawa

Tsaki Farida taja tana hararan ta tace, “dalla wuce ki bar mana gida, wlh idan baku ji tsoron Allah ba, watarana zaku yi nadama”.

Ita dai Rash bata ce komi ba, tayi gaba abunta.

    Har ɗaki Farida ta shigar da ita, a time ɗin RAUDHA tayi ta kwarara amai kamar zata amayar da hanjin cikin ta, babu yanda ta iya dole ta wanke mata, sannan ta sauya mata kaya. har a time ɗin bata bar surutun da take yi ba tana ɓaɓɓaka dariya, kwantar da iya tayi ta fice a ɗakin

A Parlour ta tarar da Suhaib, nan ta faɗa masa duk abinda ke faruwa, ai babu ɓata lokaci yayi ɗakin RAUDHA, a kwance ya ganta idanun ta a rufe fuskarta ɗauke da murmushi

Ƙarisawa yayi kusa da ita ya zauna a gefen gadon yana kiran sunan ta

Buɗe idanun ta tayi ta aza a kansa, sai ta ƙyalƙyale da dariya ta hau yin masa maganganu, har da su zagi, ko kaɗan babu kan gado

Ajiyan zuciya ya sauke, ya ɗaura hannu a kanta ya soma tofa mata addu’a cike da damuwa a cikin ransa, ya daɗe yana mata addu’a, har sanda barci ya ɗauke ta sannan ne ya tashi yabar ɗakin.

      A taƙaice dai kwana biyu cur RAUDHA tana cikin wannan halin, taƙi komawa normal, dole Suhaib ya ɗauke ta zuwa asibiti. Sai dai bayanin da likita yayi masa, ya ɗaga masa hankali matuƙa

Ƙwayoyin da tasha sun taɓa mata ƙwaƙwalwa, that’s why take irin Wannan abun

Har kuka sai da Suhaib yayi, ya rasa yanda zai yi, nan ya kira Rayyan ya sanar masa halin da ake ciki, shima hankalin sa yayi matuƙar tashi, nan ya taho asibitin akai ta zirga-zirga dashi, sannan aka ɗaura RAUDHA akan magani

Bayan kwana biyu ta ɗan samu sauƙi aka sallame ta, a ranan ne ta sake mugun mafarkin da ya ɗaga mata hankali, take ta farka tana kwatsa ihun da ya karaɗe ilahirin gidan

Lokacin da su Suhaib suka taho ɗakin ta hankalin su a tashe, time ɗin ta rigada ta sume, sun zuba mata ruwa amma bata farka ba, dole suka wuce da ita asibiti, tare da Rayyan suka tafi, sai aka bar Farida a gida.

     Duk iya gwanintan likitoci akan su samu ta farfaɗo amma abin ya gagara, sun yi iya yin su sun kasa, dole suka barta suka ci gaba da bata taimakon iya abinda suka gani, ahaka har kwanaki uku suka yi amma RAUDHA bata farfaɗo ba, su Suhaib sun rasa yanda zasu yi, ana cuku-cukun fitar da ita ƙasan waje ne, sannan ne ta farka, sai dai ko kaɗan taƙi yin magana, sai dai tayi ta ɓaɓɓaka dariya

Likitoci sun gano cewa ƙwaƙwalwan ta tarigada ta taɓu, sai dai a ɗaura ta akan magani ko Allah zai sa adace, kafin ciwon ya kai ga nisa

Kuka me sunan kuka, shi Suhaib ya dinga yi, kamar ransa zai fita, ko kaɗan be kalli girman sa ba, haka zai zauna yayi ta kuka, Rayyan shine me rarrashin sa, gashi shima ba ya zama sabida aiyuka sun yi masa yawa, yau suna nan; gobe suna can, ga tarin damuwa shima da ya riske sa, ya kasa samun nutsuwar zuciya.

     Ita kanta Farida ta kasa samun sukuni, ga rainon Haneep mara lafiya, ga halin da mijin ta yake ciki, ga kuma tashin hankalin da suke ciki akan ciwon RAUDHA, bata da maraba dai da mahaukaciya, bige-bige ne kaɗai ba ta yi, amma gaba ɗaya ba ta gane wanda ke kanta, tamkar ƙaramar yarinya haka ta koma, wani time ɗin kuma sai su ga ta koma normal kamar ba ita ba, sai dai ta dinga kuka kenan tana taɓara karasa ma me take so.

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14Next page

Related Articles

Leave a Reply

Back to top button